����������������
�� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������
Na *AYUSHER MUHD*
ayushermohd.blogspot.com
*LAST PAGE*
No. 7⃣8⃣
Can gida kuwa wasu abin nan ya basu haushin gani suke Dad bai kyauta ba, wasu kuwa harda habaici na dama yarinyar da batada mahaifi me zaisa ya had'ata da d'ansa?"
Zahra kam taji ba dadi dasu Junaid sai dai ya za'ai tunda dai an riga da angama, Ammar ko gidan baije ba, sun riga sun shirya yin dinner sai dai Zahra ce da Junaid kawai zasu.
Jalal kam suna kwance, sai can Seemah ta farka, tana ganin Jalal idanunsa biyu da sauri ta mik'e tsaye tare da wayancewa da hmm ina toilet din ne? Tafad'a tana dubawa da gudu tai nufi kofa ta bud'e ta shige.
Jalal ya bita da dariya ganin yanda ta rikice.
Tunanin wayarsa ce tazomai yasa ya jawo wayar Seemah ya kira Abbansa.
Abba ya daga, Jalal ya gaidashi.
Cikin zumud'i Abba yace " Jalal kaji abin alheri ko? Bansan mezancema Ammar da Isma'il ba."
Jalal yadanyi murmushi yace " Zainab fa?"
Abba yai shiru, Jalal ya danyi murmushi kad'an nasan bazatai farinciki ba.
Abba yace " Jalal kayi tunanin inda Seemah zata zauna?"
" hmm ina tunanin tambayarta ko nan kaduna ko kuma nan, ni abin ne banbarakwai nake jinsa."
Abba yai dariya yace " ba wani banbarakwai Allah ya riga ya tsara Seemah matarka ce."
Jalal ya kalli kofa inda yaji motsin Seemah, yace " Abba sai anjima wayar Seemah ce."
Nan sukai sallama tare da kashewa, Seemah ta harareshi kad'an tare da cewa " wa yace a d'aumin waya?"
Jalal ya dan yi murmushi yace " yayarki na kira."
A zabure ta karaso kusa dashi tace " wacce yayata?"
Kallanta yai yace " haka ake jinyar baza'a bani abinci ba? Yunwa nakeji."
Ranta a b'ace ta bud'e kular da ta gani a d'akin fatan dankali ne yaji kifi sosai, ta zubamai a plate sannan ta mikamai, tace " wacce yayata?"
Jalal yadan rik'e ciki kadan yace " haka ake kula da miji ko abincin baza'abarshi yaci ba?"
Juya kai tai aranta tace " su miji manya."
Yana gama ci ta kalleshi tace " wacce yayata? "
Hannu yasa ya riko ta tare da zaunar da ita kusa dashi yace " Meemah bamuyi tunanin inda zaki zauna ba?"
Ta turo baki tace " inafa zan zauna?"
Ya kalleta yace " inda zamu zauna nida ke a kaduna ko anan."
Ta mik'e tare da cewa " ni yazanyi iyi sallah ko mayafi ban fito dashi ba, kallanta yai yace " ai kuwa sai dai kiyi waya a kawo miki dan bazaki fita a haka ba......"
Kusa dashi ta matso tace" to ya kakeso inyi?"
Yace " bana fadamiki ki sa a kawo miki ba nidai matata bazata fita a haka ba mutane su kalleta."
Ta sa dariya sai data tsagaita ta kalleshi tace " lalai mai mata."
Lumshe ido yai yace " sosai ma, Ammar ne ya bani matar da nakeso wacce ji nake duk numfashina tana tattare dani."
Dariya ta sakeyi tace " Kai Deen yaushe ka zama haka?"
Jawota yai jikinsa yace " ke kika maidani haka, mu zauna a abuja ko? Kinga kusa da Dad d'inki."
Ta turo baki tace " bayan bani kad'ai bace matar ka?"
Yai ajiyar zuciya yace " Meemah amma kinsan ai...."
Saurin cusa kanta tai a kirjinsa alamar kunya tace " na sani amma a da dan rannan tafiya kai ka barni."
Ajiyar zuciya yai yace " Meemah banasan zama a asibitin nan mu roke likitan ya sallamemu please kinji?"
Tace " naki wayan baka warke ba ta ina zamu tafi? Kuma ni banshirya tarewa yanzu ba."
Hararta yai yace " a ina? Ai kafata kafar matata Amnar yamin abinda ban taba zatoba ta ina nikuwa zan barki kije wani gida? Mu tafi gidana inyaso sai insa a nemarmana gida."
Baki ta turo tace " an fa kai min kayana can gidan Ya Ammar kuma kwasowa za'ai ko me?"
Jalal ya rungumeta yace " bakomai sai musai wani."
Ta mik'e tace naki wayan.
Washe gari kuwa sai da Jalal ya matsa aka sallameshi duk lokacin abinci ana aikowa daga gidan su Dad.
Ammar kam hotel ya koma kawai ya tare, su Dad basu sani ba ashe yayi booking d'in jirgi, washe gari da safe yazo ya sanar da Dad zai koma England amma ba dadewa zaiyi ba, ba musu Dad ya amince saboda yasan halin da Ammar din ke ciki.
Bayan Jalal ya warke da kanshi ya kaita gun Abdul, nan ya nemi yafiyarta tare da alkawarin canza halayensa, sunyi ziyara har garin iyayenta nan sukaje taga 'yan uwanta.
Jalal ya kama gida a Abuja inda suka zauna shida Seemah, kulawa kaunar dake tsakaninsu ta wuce duk yanda zan kwatanta muku, Yau yakama wata tara kenan da auren su, duk karshen mako yake tafiya kaduna Seemah ita ta tsara mai hakan saboda tana ganin yanda yake rashin damuwa da Zainab hakan bazai mata dadi ba, shikanshi yanzu yana daidai kokarin kwatanta adalci a tsakaninsu, sam Zainab bata jin haushin Seemah ita gani take ma auren da Jalal d'in yai shine sanadiyyar kulata da Jalal yake, Seema na d'auke da tsohon ciki, itakuma Zainab laulayi takeyi.
Jalal ya shigo gidan ganin yanata sallama ba'a amsa ba, a rude ya shigo gidan ya fara neman inda Seemah take, har daki ya shiga batanan, d'akinshi ya nufa, yana budewa yaga ta fesheshi da wani farin abu, baya yai yana mamaki, nan ta matsamai ya kalli d'akin, candle ne kanana an jera shi a kasa anyi kwalliyar I♡U dashi kwaliyar tayi kyau, ya kalleta cikin mamaki, kayan bacci ne a jikinta shara shara ya sakar mata wani sansanyar murmushi tareda karasowa ya rungumeta, murmushi itama tai tace " My Deen kardai a manta da babynmu."
Sassauta rikon yai sannan ya d'ago a hankali ya kai bakinshi cikin nata, wani irin salon kauna sukema junansu, jitai kafarta naneman kasa d'aukanta, Jalal ya riko kugunta nan suka cigaba da aikama juna sakwanni, a hankali Jalal ya jata kan gado sannan ya tare neck tie d'insa ya cigaba da sumbatarta, cikin salo a kuma hankali ya bakinshi na nata ya zare mata 'yar rigar dake jikinta, itama mab'allin rigarsa ta dinga cirewa har ta cire su duka, sumbatar kirjinsa ta fara nan fa suka shiga cikin wani yanayi wanda su kadai sukasan halin da suka shiga.
Sai da suka gama sannan ta kwanta akan kirjinsa, shikuma yana shafa kanta, yace " Meemah wannan gyaran fa? Decoration d'in yayi kyau, kara kwanciya tai a kirjinsa tace " a internet na dubo yanda akeyi."
Yai ajiyar zuciya yace " Meemah in miki wani alkawari?" Ta d'aga kai, tare da juya fuskarta saitinshi, yace " indai mace kika haifa sunan Mahaifiyarki zamusa mata Fatima, in kuma namiji ne to sunan Ammar ko Dad sai kizab'a a ciki."
Murmushi tai tace" nagode sosai Deen, amma ya maganar Ya Ammar?"
Yace " yace next week zai dawo."
Tai ajiyar zuciya tace " kaii nayi missing d'in yaya."
Mikewa yai ya sunkuceta sukai toilet, kafin suyi wanka sai daya wanke mata kai da kanshi, dan tace bata iya sunkuyawa, nan sukai wanka suka fito a tare, shi ya shafa mata mai sannan itama ta shafa mai tana shafamai tana tambayar yasu Ya Zainab?" Yace suna lafiya.......
Ammar ya zaune a cikin jirgi yana karanta jarida watace a zaune a kusa dashi ta zake sai bacci take, haushi ya kama Ammar ya juya kansa jikin window, tana gama baccin ta mik'e tare da yin mika, ta kalli Ammar tace " dan Allah awa nawa mukai?"
Kallanta yai yace " ke agoggonki tsayawa yai?"
Agoggon hannunta ta kalla ashe da agoggo a hannunta da sauri ta juya fuskarta, yai murmushi sannan ya juya, mai service ce ta karaso ta kallesu tace " mai kukeso a kawo muku? Tea ko coffee? "
A tare sukace " Coffee."
Kallan juna sukai sai sukai dariya, matar tai dariya itama tace " da alama ku couples ne kunyi matching sosai."
A tare suka kara cewa " a'a."
Tai sake dariya sannan ta tafi, tana tafiya Ammar ya kalleta kadan kyakyawa ce sosai, juyawa yai jiyai tace " A Abuja kake?"
Yace " eh kefa?"
Tace nima...........
Murmushi sukama juna a tare.
Zahra ma ankusa haihuwa, Dad da Abban Jalal aminta ta dawo sosai, yanzu Abban Jalal yananan yana kasuwancinsa a babban shagon da Jalal ya bud'e mai.
Zaid ma saura wata d'aya ya auri Zaheeda wacce ta warke sumul, har malami Jalal ya d'aukar mata yana koya mata karatu.
Abdul kuma an sakeshi yana zaune a dan karamin gidansa shida matar sa 'yar uwar Sagir, Ya canza kamar bashi ba.
Jalal da Seemah masha Allah kauna kam suna san junansu sosai........nace To Allah yasauketa lafiya
Nima nace mu had'u a wani littafin nawa in Allah ya yarda.......
GODIYA TA MUSAMMAN GAREKU
Yan Group d'ina
THE QUEEN BEE
AYUSHER FAN CLUB
Sannan ina godiya gareku 'yan
*NAGARTA*
BEELY BADARU GROUP
'YAN SAUYI NA KCK
EXCELLENT HAUSA WRITERS
MU SAN JUNA
TALENTED HAUSA WRITERS
MARYAM MAI DALA
HAUSA NOVEL
MY BLOG FANS
HAUSA NOVELLA
BE A LADY WITH FASHION
Da kuma ragowar group d'in da duk nake ciki ina godiya gareku.
Ina alfahari daku
MY BEELY BADARU
SIS PHARTY
ASY KHALEEL
MAMAN SHAHEEDA
MUNAY
SADNAS
AUNTY KYADY
FATTY
Ahh gaisuwa gareki babbar Aminiya AISHA M.UMAR....
NI AYUSHER MUHD ke muku fatan alkairi��������