JÅĹÀĹÙĎĚĚN
Na AYUSHER MUHD
ayushermohd.blogspot.com
_Ina bawa masoyana hakuri najina shiru da kukai, kuyi hakuri amma insha Allahu zanyi kokarin ganin na kammala littafinan acikin satinnan, nagode kwarai da san da kukema littafin nan....Luv U Ol ❤_
No.7⃣4⃣
Abdul zaune yana kallan uwargidansa kallan tsananin mamaki yace " Rabi kinsan me kike fada kuwa? Ban gani in sakeki ba ina cikin wannan yanayin ba?"
Wata dariyar rainin hankali tamai tace " me? Kana tunanin soyayya ce tasa na aureka?"
Tai wata dariyar rainin hankali tace " are you naive or fool? Kai kana tunanin duk mutanen dake kusa dakai saboda suna sanka ne ko suna san kudinka? "
Abdul cikin mamaki ta kalleta yace " Rabi da kikazo na dauka abu na farko da zaki fara tambaya shine meya faru a shekara 20 din? Da gaskene? Sannan ki tambayeni halin da nake ciki a gidan yarin nan amma......"
Katseshi tai cikin fada tace " so kake inzauna ka fadamin wani shirme dakai a baya? Ko ce maka akai na damu da halin da kake ciki? Takardata nake bukata dumin inasan barin kasar nan cikin gaggawa kafin laifinka ya fara kokarin shafata."
Abdul ya kalleta cikin tsananin mamaki yace " me ne? 'Ya'yan mu fa? Ko kin manta da 'ya'ya a tsakanin mu?"
Rabi ta saki wata dariya taban haushin mai sauraro tace " 'ya'ya? Ahh haka ne ashefa kai baka sani ba ko? Amma ina mamakin ina hankalinka yake, sai dai kayi hakuri 'ya 'ya nawa ne ba ka da hadi dasu."
Abdul cikin mamaki yace " me kike nufi nufi da kalamanki? "
Tai tsaki tace " malam inka ga dama ka saken in bakaga dama ba kai ta ajiye da sakinka zan koma dubai da abokinka Marfuz wato uban 'ya'yana inka ga dama ka aiko mana da takardar saki can." Tana kainan ta mike, cikin zafin rai ya riko hannunta yace " marfuz? Abokina? Me kike nufi?"
Hannu tasa ta fizge hannunta da karfin gaske tace " matsalarkace, tana kaiwa nan tai waje."
Kai ya shiga girgizawa ya tuna shine sanadiyar arzikin marfuz kuma shine abokinsa da ya dinga zigashi akan abubuwa marasa kyau ciki kuwa harda fyad'en dayama fatima.
Ihu yasa cikin tsananin takaici ya rike zuciyarsa dake kuna tare da tsugunnawa a kasa, lalai kuka ma rahama ne, jiyai sam ya kasa kuka, sai wani irin zafi da zuciyarsa keyi.
Guard din dake bakin kofa ya kalla yace " dan Allah......."
Ai bai karasa ba yaji numfashinsa ya rike, nan guard din ya matso da sauri ya shiga danna mai baya, dakyar numfashinsa ya dawo.
Abdul sam ya kasa cin komai, a zaune kawai yake shikadai yasan me yakeji.
Jalal kam ya zama celebrity a gari ko ina ka duba kaga hutunshi a magazine ko a jarida ansa Jarumin da baya tsoron hukuma sai gaskiya, duk shirin dayace zaiyi kuwa a gidan tv to lalai zakaga mutane sun zako akan ganin me jarumi kuma matashi zak gabatar.
Biki ya matso, sai dai Zahra ce kadai take shirin bikin amma sam Seemah batasa baki a harkar in Zahra tazo mata da xancen ya zasuyi kaza, kya kacinta kawai tace to, dama ba fita take ba inba gidan Ya Habib taje ba, yau saura sati daya biki, gida ya fara cika, hakan yasa yau Seemah ta tattara kayanta kamar yanda Dad yace akan ta koma gidansa saboda matarsa tazo itama, ta gana cikin gada kayantane ta ci karo da agoggon ta kurama agoggon ido tai nan fa ta fara tunano rayuwarsu ita da Jalal, kallan agoggon take ta kuma zarfafa cikin tunani, Ammar dake tsaye a jikin kofa ya taho da saurinsa zai nuna mata katin biki na dinner daya amso, ganinta a zaune tasa a goggo tana kallo yasa ya tsaya, hannu a harde tare da jingina da jikin kofar, basai Seemah ta fadamai ba yasan agoggon da take kallo me yake nufi dan kuwa agoggon dake hannun Jalal kenan kullum, ya kuma gansu iri daya sak, jiki a sanyaye ya juya harzai fita sai kuma ya fasa ya koma ya tsaya tare da cewa " Kanwata ko in juya ne?"
Kallansa tai da sauri tare da juyawa ta goge hawayenta ta mike tace " yaya yaushe kazo?"
Ammar yadan hade rai kadan yace " nafi awa biyu fa anan."
Cikin tsananin mamaki ta kalleshi tace " da gaske? "
Dariya yai yace " lalai taya za'ai ki yarda?"
Harararsa tai tace " Yaya wato dai kai na kula inba tsokanata kaiba sam bakajin dadi ko? "
Shiga ciki yai kusa da ita ya tsugunna kasa ya dauko agoggon data yar tana saurin mikewa, kallan agoggon yai sannan ya mike tare da mika mata, kallansa tai batare da ta amsa ba, kallanta ya sakeyi yace " amsa mana nasan abune mai mahimmanci a gunki."
Kallansa tai tareda shan jinin jikinta tace " Yaya ba......"
Murmushi ya mata yace " ansa mana."
Hannu tasa cikin sanyin jiki ta amsa, yace " me? Kinaso ki mai sallama ne kafin biki?"
Kallansa tai cikin tsananin mamaki, da sauri ta juyamai baya tace " bafa haka bane yaya, kawai ganin agoggon nai."
Ya dawo gabanta tare da daga kai yace " nasani Seemah nasan komai hakan ne yasa banaso kidinga boyemin komai, nine na tambaye ki bawai ke kika tambayeni ba."
Idannunta ne suka ciciko ta girgiza kai tare da cewa " how can I......?"
" I am okay!" Ya fad'a yana kallanta, tai kasa dakai, yace " banaso ki dinga tunanin bakimai sallama ba..."
Ganin tayi kasa dakai ya juya tare da cewa " in bakyaso shikenan."
Yana fada ya juya kamar zai wuce, jiyai ta riko hannunsa ta baya, ya tsaya batare da ya juya ba, duk da kishin dake damunsa amma bayaso yaganta cikin wannan halin saboda shi.
A hankali Seemah tace " Yaya zan iya?"
Bai juyo ba ya daga mata kai tare da daurewa yace " banine na ce ba?"
Ta goge hawayen ta da d'aya hannun tace " yaya zan mai sallama tare da ajiye duk wani ragowar abu dake zuciyata, bazan sake tunaninsa ba bare insa ka kaji ba dadi ba."
Ammar ya daure ya juyo ya kalleta tare da mata Murmushi yace " karki damu Kanwata farincikina bai wuce naganki kina farinciki karki damu dani farincikina na tattare dake."
Yai ajiyar zuciya tare da cewa " in har kinaso ki ganni ina farinciki to ke zan jira kiyi farinciki kafin ni."
Seemah ta share kwallarta jikinta yai mugun sanyin, tausayin Ammar ya kara shigar mata zuciya, zare hannunsa yai yace " kishirya in ajiyeki, in yaso sai ya dawo dake."
Yana kainan ya fita, kallon tsananin tausayi ta bishi dashi, zama tai a gun tare da runtse ido tace " Seemah meke damunki? Taya zakice zakije bayan kinsan koyace kije dolene yaji haushi?"
Ta dade a zaune kafin Ammar ya kirata yace tafito yana jiranta.
Jalal kam zauje yake a dan karamin gidan daya kama, saboda ya sai gida babba yanzu a kaduna inda Umma da kuma matarsa Zainab suke zaune acan, Zahida kam itama jiki ya fara sauki sosai Zaid kam kusan duk karshen sati sai yaje, tun Zaheeda na wase wa harta fara saki gashi ba laifi yanzu tana iya takawa kadan kadan inta rike sanda.
Takardu ya gama dubawa sannan ya mike danjin yunwa ta fara kamashi, kallan calendar dakinsa yai ya zagaye wata number da jan biro, karasawa yai jikin calender yace " saura 7 days?"
Ajiyar zuciya yai sannan ya kalli wayarsa dayaji tayi kara alamar text, dagata yai yaga sako ne ga mamakinsa daga police station ne, wai Abdul na nemansa, yataimaka ya ziyarceshi."
Wata iska ya furzar yace a fili " Allah yasa ya daidaita tunaninsa akan 'yarsa."
Window ya zuge ya kurama titi ido, yaushe rabansa da Seemah?
Kai ya girgiza tare da cewa " Ahhhh...."
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
♀
send ur detals i will design for u 09039016969 or email me abbagana79@gmail.com
ReplyDeleteOk I will send it, tnx alot
DeletePls waiting tnx
ReplyDelete