Saturday, 4 March 2017

JALALUDEEN 76

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 7⃣6⃣


      Ammar na tura kofar yaga Jalal a kwance a kasa cikin kid'ima shida Zaid sukai mota dashi, asibiti suka wuce dashi hankalin Ammar yayi dubu gun tashi gani yake kamar shine sanadiyar wannan ciwon, suna zuwa asibiti akai emergency dashi,  Ammar ya tsaya a wajen dakin jiyake kamar yai ihu, Zaid ya kalleshi yace   " kazo likita nasan ganinka."

Ammar jiki a sanyaye ya karasa ciki, likitan yace " kaine Guardian dinsa?"
" eh, wani abun ne?"

Likitan yace " me kukeyi har jikinsa yakai haka? Ga bigewar dayai abayansa baizo anyi treating dinsa ba sannan ga rashin cin abinci dan da alama rabonsa da abinci tun jiya da rana, ga damuwa mai karfi dake ransa, so kuke ku kasheshi ko me?."

  Yai ajiyar zuciya sannan ya kalli Ammar wanda gaba daya abinduniya ya dameshi likitan ya daure ya dafashi, yace " ba komai zamu dubashi dakyai."

   Ammar ya kurama Jalal ido, nan likitan yasa akaja gadon Jalal akai wani dakin dashi, Ammar ya kalli Zaid yace " ka fito da wayarka?"
Mikamai Ammar yai yana cewa ya kamata asanar da su Zahee ko?
Ammar bai amsa mai ba ya danna number Dad.
" Ammar kana ina ne kawu na nemanka?"
Ammar cikin sanyin murya yace " Dad ina asibiti."

A zabure Dad ya mike yace   " kana asibiti kamar ya? Me a sameka? Ciwo kaji?"

Ammar ya girgiza kai kamar yana ganinshi yace " Dad kazo please, Jalal na kwace ba lafiya sosai."

Mamaki ne karara ya bayyana a fuskar Dad yace " inalilihi wa ina ilaihi raji'un, Ammar meya sami Jalal din?"

  Ammar dake kallan Jalal yace " Dad nidai kazo please. "
Dad yai ajiyar zuciya yace bari na zo.
Jiyai Ammar yace " kazo kai kadai please Dad."
Dad ya amsa tare da fitowa.

   Sunyi shiru, a inda Jalal ke kwance, Dad ya kalli Zaid yace " tsaya anan Ammar ina da magana dakai."

  Sun fita waje can gun da ba mutane sosai, Dad ya kalli Ammar yace " meya sameshi haka? Duk ya canza?"

  Hawaye ne suka dan gangaroma Ammar yasa hannu ya cire yace " Dad ya zanyi? It's all my fault. "

  Dad yai shiru yace   " Ammar!"
" Dad."
Yai maganar cikin wata murya, Dad yasan halin Ammar da tausayi dafashi kawai yai yace " kaje gida nizan tsaya anan."

  Kai Ammar ya girgiza yace " bazan iya tafiya ba Dad sai naga Jalal ya ware."
Kai Dad ya jinjina yace " to Ammar amma kaga dare yayi ga gobe karfe 10 za'a daura auren nan baka tunanin ya kamata kaje gida?"

  Ammar yai shiru, can yqce " Dad in Seemah tasan Jalal bashi da lafiya ya zatai? Balle intasan ciwon a dalilinta ne?"

  Dad ya kalleshi batare da yace komai ba, Ammar ya cigaba " Dad ya zatai?"
Kai dad ya juya yace " Ai ba fada mata za'ai ba."

  Ammar ya runtse ido sannan ya bud'esu idanunsa sun cika taf yace " Dad baka gani muna shiga hakkin ta?"
Da mamaki Dad yace " Ammar me kake nufi haka?"

   Ammar ya had'iyi wannan abun yace " Dad babban bakin cikina aduniyar nan bai wuce inga Seemah cikin damuwar da harzai kaita gayin kuka, amma Dad kasan kukan da nasa Seemah ta dalilin yaron nan? Sau nawa ina ganinta tana kuka akan abinda baifi karfina ba ko ince akan abinda nine xan iya daidaitashi, amma haka nake ganinta tana kukanta bana iya tab'uka komai saboda wani buri na zuciyata."

  Hawaye ne suka gangaro kumatunsa, ya kalli Dad yace " Dad nan!!!!"
  Dukan inda zuciyarsa yake yai, da karfi yace " nan gun Dad ni kadai nasan ya nakeji inaga Seemah na hawaye, sannan ina tuna Sadaukar da rayuwarsa da Jalal yai saboda Seemah, kanwarsa batada lafiya amma baije gunta ba......"

   Dad ya dafashi yace " Amma ai ita Seemah itama ta zab'eka."

  Ammar ya girgiza kai yace " tadai zabi farin cikin ka ne Dad, yarinyar nan bataso ko kadan taji tama abinda bazai faranta maka rai ba ciki kuwa harda sadaukarwa da farincikin rayuwarta, na sani zan kula da ita, ina santa kamar raina sai dai nasan inda zuciyarta take  , Seemah na bala'in sona amma son 'yan uwantaka takemin."

  Dad yai shiru sai dai jikinsa yayi mugun sanyi yakasa furta komai.
  Ammar yacigaba tare da share hawayensa yace " Dad duk farincikin da Seemah takeso nima inasan shi sai dai ina bakin cikin zuciyata tana neman canza min tunani na."

  Dad ya kalleshi, Ammar ya tsaida hawayensa yace " Dad na tsaida solution gobe auren nan da Jalal za'a daura bazan iya ganin abokina da kanwata danafiso a duniya cikin damuwa ba nikuma ina farin ciki ba."

  Kallan tsananin mamaki dad yamai yace " Ammar kasan me kake fada kuwa?"
  Murmushi Ammar yai wanda kana ganinsa kasan na bakin ciki ne yace " Dad ka taimaketa ne saboda son da kake ma mahaifiyarta da kaunar da kake ma yarinyar ko?"
Dad ya daga kai tare da cewa " hakane amma...."
Ammar yace " ka taimakesu ne saboda Allah na sani Dad."

  Dad yai shiru, Ammar ya cigaba " in har munaso ladanmu ya karfafa agun Allah mu bawa Jalal Seemah sai kaga Allah yakara daukaka mu ya kuma biya mana da mafificin gidan Aljanna."

   Dad ya kalli Ammar cikin tsananin kulawa yace " Ammar kaifa? Ni gani nake kamar sai kafi Jalal shiga wani hali in aka rabaku da Seemah."
  Kai ua girgiza yace " a'a dacan a matsayin kanwata take yanzu ma a haka zata zauna, na sani sanda nake mata ya wuce duk yanda kowa ke tunani amma tunda ni kadai nake santa haka banaji wani abun zai sameni."

    Dad kam kalaman Ammar sun ratsa jinin jikinsa, yace " shikenan Ammar."

  Murmushi Ammar yai yace " Dad dan Allah karmu fadawa kowa sai Abba kowa yaji a gidan bayan an daura in ba haka ba wani sai ya nemi canzama ra'ayinka."

   Dad ya dafa Ammar yace   " Ammar ka tabbata ba komai?"
Kai Ammar yadaga yace " marainiyar Allah itace first ni daga baya, sannan sai kamin addu'a Allah yabani wata."

   Rungumeshi Dad yai yace " Ina Alfahari dakai d'ana ka fahimtar dani abinda ban yi tunani ba, Jalal yaron kirki ne tun yana karami, naji dadi sosai da kaunar da kukema juna kuna yara ta dawo muku yanzu."

   Sun dade agun suna hira kafin su koma ciki, dad da Zaid suka koma gida.

   Washegari kowa ya tashi anata hidima, Seemah ta rasa dalilin dayasa gabanta keta faduwa, Ammar ta kira sai dai taji Junaid ya d'aga, tace " yaya Ammar fa?".

  Junaid ya kalli Zaid wanda yace Ammar yace kar afad'a mata inda yake, yace " yad'an fitane."

  Ta kashe wayar tare da d'an had'e rai.
 
Zaune suke a massallaci an fara add'uoi za'a daura aure.
  Abba zaune yayi shiru yana tunanin kalaman Dad, na jiya daddare, ajiyar zuciya yai alokacin da akace waliyin Jalal yaji dad yace " ganinan."

  Dad ya riga ya sanarda mahaifin Jalal wato Amadu nan yai farin cikin da hakan har kuka sai dayai.

   An dauren auren Junaid da Zahra,  Jalal da Seemah akan sadaki dubu d'ari wanda da kudin da za'a bada na Ammar ne.

  Mamakine ya kama 'yan uwan mahaifin Dad dana mahaifiyarsa, Habib ya kalli Dad cikin mamaki sai dai aikin gama ya gama.

    Zaid ne ya kira Ammar dake asibiti gun Jalal yace " Ammar an d'aura."

  Runtse idanunsa yai jiyake kamar yasa ihu, dakyar ya daure yace " ka fad'awa Seemah mijinta na asibiti ba lafiya."


   Zaid yace " Ammar inzo in daukeka?"
Ammar ya d'aga kai, Zaid ya daga kai tare da cewa " Jalal din ya farka?"

  Ammar ya girgiza kai yace   " a'a ko ido ya bud'e sai dai inga ya maidasu, sai dai likita yace abarshi ya huta stress sunmai yawa ga damuwa."

  Zaid ya d'aga kai.



  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

2 comments: