*ZUCIYA*
_ĸowa da ιrιn тaѕa_
© *na Ayυѕнer Mυнd*
ayushermohd.blogspot.com
*Wattpad As_AyusherMohd*
{ *35*}
Yanda yake kallanta yasa ta had'e rai tare da maida kallanta wajen window, itakam batasan me zata cemai ba, ana san kashe ka? Kuma 'yan uwanka?? Itakam kalaman nan sun mata tsauri.
Ga mamakinta jitai yace " tunda karyar ciwo kikai yanzu ai sai ki koma gida."
Nafi ta kalleshi a tsorace tace " Sauka zanyi a haka??"
Kai ya d'aga mata alamar yes, idanunta ne sukai rau rau ta kalleshi sannan tace " taya zan iya fita ahaka komayafi fa babu a jikina, sannan bani da kud'in da zan tafi da kaina."
Ya d'aga mata kafad'a alamar wannan kuma ruwanta ne, Nafi ranta ya b'aci a zuciye ta matsa da niyyar bud'e kofa, har ta zura kafa d'aya zata fita sai taji yace " shigo in ajiyeki ba dan halinki ba inada abinyi."
Ta koma ta zauna kamar ba taso sai dai ko kallan inda yake batai ba, Ashraf ya tada mota zuciyarsa fal da tunani, har suka isa gida ba wanda ya sake magana, yana parking ta bud'e kofa zata fita sai kuma ta juyo tace " Yaya ina zaka?"
Kallanta yai yace " banaji wannan yana d'aya daga cikin damuwarki tunda dai baki fad'amin me kike nufi da kar inje aiki ba, kin kuma san halina ba a sani abu."
Nafi ta kalleshi cikin kulawa tace " Yaya tunda kaga na furta hakan ai kasan da dalili, in ba haka ba meye nawa da zance karkaje aikinka?ni ba matarka ba?"
Juyowa yai ya kalleta kalamanta na karshe sun tsayamai a wuya, sai dai ya share yace " ke nake jira zan fita ko?"
Nafi batasan sanda wani takaici ya kamata ba ta kafeshi da ido na takaici, kallanta yai sannan ya juya ya d'au wayarsa, bakin ciki ya hanata d'auke idanunsa daga kansa jitai ya tada mota, alamar zan tafi, takaici yasata ta fito daga motar a zuciye tana kallo yaja motarsa ya tafi, tabi motar da kallan takaici.
Wannan wani irin mutum ne, duk yanda na damu da rayuwarsa amma shi ko a jikinsa?? Sai ma rashin mutunci ne zai biyo baya?.
Sam ta kasa d'auke idanunta daga hanyar daya wuce, jitai an dafa ta a firgice ta juyo, Mumy ta gani tsaye itada Little.
Nafi tai saurin share kwallarta sannan ta kakaro murmushi tace " Mumy ina kwana???" tafad'a tare da risinawa, mumy ta amsa sannan tace " Nafi me kike yi anan? Little duk ta damu tanata nemanki?"
Nafi ta kalli Little sannan tai murmushi tace " Ayya My Sisto tuba nake."
Little ta harareta sannan ta juya tai b'angarensu, Mumy ta kalli Nafi databi bayan Little da kallo tace " Nafisa ina kika je???"
Nafi tai kasa dakai, Mumy tai murmushi sannan tace " shikenan, kije gun 'yar uwar taki dan hankalinta ya tashi."
Nafi ta d'aga kai sannan tai bayan Little da sauri.
A tsaye ta ga Little ta cire kaya daga ita sai towel da alama wanka zata shiga, Nafi ta karasa gunta ta zauna akan gado tana kallan Little wacce ta had'e rai.
Nafi tai murmushi tace " Little bazaki kulani ba?"
Little ta juya tai hanyar toilet, tanaji Nafi ta kara cewa " My Sisto tuba nake kinji kiyi hakuri."
Little ta wuce toilet ba tare da ta amsa mata ba, nan Nafi ta mik'e ta gyara d'akinsu ta gama shara kenan Little ta fito, Nafi ta kalleta zatai magana taji Little tace " ki je kiyi wanka Yusra tun d'azu take kira wai dan Allah muje yanzu."
Nafi ta mike ta karaso gun Little ta rungumeta tare da cewa " Little wlh wani abu ne ya taso min dayai gaba da duk tunanina."
Little tace " Shikenan Feena ni kin barni anan cikin tsoro tunda na tashi naga banganki ba na kuma fita kaf na zaga ban ganki ba."
Nafi tace " Sry nayi laifi."
Murmushi sukama junansu, nan Nafi ta saketa sannan itama tasa nata towel d'in ta nufi toilet, har taje zata bud'e kofar ta juyo tace " Little nikam a iya sanina ba wata matsala dake tsakanin Mumy da Umma ko?"
Little ta kalli Nafi tace " Feena kenan, a haka dai kamar babu, sai dai inaji a jikina kamar da wani abu."
Nafi ta kalleta tace " kamar me??"
Little ta d'an tab'e baki tace " kinsan a duniya in har akace kud'i to fa an gama komai, kud'i da kike ganinsu sune matsalolin komai na rayuwar duniyar nan, duk wata matsala inka dubashi daga kasa to fa lalai zakiga kud'i shine silar komai."
Nafi ta shiru tana mamaki, can tace " Amma dai nan banaji za'ai fad'a akan kud'i ko? tunda dai naga kowa yanada shi."
Little ta furzar da iska sannan tace " Feena kenan ai a gidan da ake da kud'in anfi samun matsala akan kud'in tun balle in dukiyar da mai ita."
Nafi ta mata kallan mamaki, Little tai murmushi sannan tace " share kawai."
Jiki a sanyaye Nafi ta shiga wanka, sam wanka take amma tanata nanata kalaman Little dukiyar da mai ita? Kawu kenan? To in shine meye na neman kashe Ya Ashraf?"
Ta dad'e kafin ta fito, tana fitowa taga Little ta ciro musu dinkin Less anko ne shima, Nafi ta zauna itama ta fara shafe shafe.
A b'angaren Ashraf kuwa yana fita daga gidan ya nufi gidan abokin babansa ko ince lawyer d'in babansa, bayan sun gaisa yace " dama so yake ya d'auki mota d'aya daga cikin motocinsa dake gidan.
Nan ya d'auko masa keys d'in Ashraf ya d'au d'aya sannan sukai sallama ya fita.
Hanyar Company d'insu ya nufa, yasha kwanar karshe ya hango wasu mutane kusan su goma a cikin wata katuwar mota baka kirin sai dai sun sauke glass d'in motar sannan wasu sun zuro kansu suna duba hanya, bakaken kaya garesu haka kuma baza'a ganesu ba saboda tabarau baki dake fuskarsu.
Ashraf ya rage gudu dayazo kusa dasu, sam sukam sun d'auke kai daga kallan motarsa ganin ba irin ta bace wanda aka basu umarni.
Hakan ya bashi damar ganin yawan mutanen dake ciki, sannan ya wuce, lalai ya tabbatar shi suke nema saboda yazo giftawa yaji wani yace "wai ya haryanxu banga mota kirar Marcedes_Benz C300, wai ya tabbatar nan zai biyo??"
Ashraf ya giftasu zuciyarsa fal da mamaki, meke faruwa? Me Nafeesa ta sani? Me taji????
Ya karasa gun aikinsu nan ya tadda 'yan team d'insa sun dad'e da zuwa, nan ya zauns suka fara abinda ya kawo su.
Su Nafi ansha kwalliya, suna fitowa Habib na yin parking, tundaga nesa Little ta hangoshi ta saki wani lalausan murmushi na farinciki, Nafi ta kalleta sannn ta kalli inda take kallo ganin Ya Habib yasa tai murmushi itama tace " Little a dinga kokarin dannewa irin wannan nuna soyayya kirikiri haka??"
Little ta harareta sannan tace " haka nace miki?"
Nafi ta d'an rangwad'a kai tace " Little kenan."
Juyowa yai shima ya hangosu, nan ya tsaya tare da kurawa Nafi ido, gaskiya yarinyar nan type d'insa ce ba karya, har suka iso gun yana kallanta, Nafi ta d'an had'e fuska tare da kawar dakai ge.
Little ta matsa gunsa tace " Ya Habib daga ina haka?"
Idanunsa nakan Nafi yace " wlh wucewa nazo yi shine na shigo."
Little ta kalli Nafi dan taga yanda yake kallanta, sai dai bata kawo wani abu ba tace" Nafi tayi kyau ko yaya?"
Habib yai murmushi yace " Sosai ma kuwa."
Nafi ta matsa daga saitinsa sannan tace " inafa wani kyau dan kowa yaganki yasan kece kikai kyau."
Ta fad'a tare da cewa " Ya Habib ko ba haka ba?"
Ya kalli Little kunya tad'an kamashi yai wani murmushin burin kunya yace " dama ai Princess daban ce."
Little ta saki murmushin farin ciki.
Little ta kaleshi cikin kauna tace " Ya Habib yaushe zaka tafi?" yace " zuwa la'assar dan inasan ganin Ashraf."
Kai little ta d'aga tace "Allah yasa mu dawo mu sameka."
Yace Ameen tare da satar kallan Nafi.
Nan sukamai sallama suka shiga motar Little sukai gaba.
Su Umma kam da Asim suna zaune a falo suna jiran good news tunda sunga fitarsa daga gidan da motar mercedes wanda hakan yasa Asim ya sanar dasu sunan motar da number ta, sai dai jin shiru har shad'aya ba labari yasa Asim ya kira, sun sanar dashi har yanzu motar bata wuce ba, nan suka kara jinkirtawa zuwa azahar, nan ma akace motar bata wuce ba, cikin takaici Asim ya kira wani ma'aikacinsu na company ya tambayeshi Ashraf yazo? Ga mamakinsa jiyai ance tun d'azu yana nan.
Haushi da takaici suka turnukeshi ya kirasu ya hau su da fad'a sannan yace " su tafi daga gun kafin ma a zargi wani abun.?"
*THE INNOCENT TEAM*