Saturday, 14 January 2017

JALALUDEEN 43

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 4⃣3⃣

  Seemah kam tunda suka shiga mota ba wanda yai magana kowa da abinda ke damunsa, har suka isa gidan itadai Seemah kanta na kasa bayan sun isa mami da kawo suka fita Seemah ta kalli Ammar tace " yaya ni kad'ai zan kwana anan?"

  Murmushi ya mata yace " ke kad'ai ce anan d'in? Ga Zahra ga mami nan?"

Tace " kasan bamu saba ba please ka shigo kaima saika kwana gun Ya Zaid inkananan sai hankalima yafi kwanciya."

  Yai shiru shidai sam bayasan kwana a gun Zaid saboda Zaid hana shi bacci yakeyi ya d'inga mai surutu kenan sannan in 12 tayi kuma sai ya shiga waya da 'yan mata sam ya hanashi bacci, amma ya zaiyi? Bazai bari Seemah ta takura ba.

Seemah ta kalleshi jin shirun yayi yawa tace " Yaya na!!!!"

Ya kalleta yace " to kanwata muje ko?"

Wani dad'i ne ya kamata sannan ta bud'e motar ta fito.
Tare suka shiga Falon, Zara na tsaye a bakin window dama tunda mami tace da Ammar sukazo take lek'ensa, ganin ya fito yasa ta kara gyara fuskarta ta tsaya a bakin kofa.

  Suna kwankwasa wa ta bud'e tare da wayancewa tace " Seemah na d'auka sai nazo na d'aukoki da kaina." Seemah tad'anyi yake tace " Zara ya kike?" Lafiya ta fad'a sannan  ta kalli Ammar tace " laaaa Ya Ammar ai ban kula da kaiba."

  Hararar wasa ya mata yace " anya kuwa kanwata? Bayan naga haske d'azu ta mota kamar da mutum a tsaye ta labule yana lek'e?"

Idanu ta rufe tace " kai yata bansan waye yake lek'e va."

Dariya Ammar yai yace gaskiya kam da alama ku 2 ne a falon.

  Ta turo baki tace " yaya ai ko ka sani sai ka basar haka fa akeyi."

  Seemah tai kasa dakai tana wasa da 'yan yatsunta, Ammar baiba Zahra amsa ba yace " kanwata kuje ciki kiyi sallah nima bari nai sai in dawo muyi hira ko?"

Kai Seemah ta d'aga alamar eh, Ammar ya kalli Zahra yace " Zara a kuma kularmin da kanwata."

Bai jira amsartaba yai waje, Zahra tabi bayanshi da kallo tana Murmushi sai daya fita sannan ta kalli Seemah tace " muje ciki." bata amsa ba kawai itama ta fara binta sun shiga d'aki Zahra ta nuna mata toilet, Seemah ta wuce ta shiga.

    Tsaye tai a toilet tana kallan kanta a madubi, itakad'ai tasan me takeji a zuciyarta, Deen zai yi aure? Ta maimaita kalaman Zainab data mata a waya, hawayene ya ziraro mata ga mamakinta jitai kuka ya b'arke mata sosai, tsugunnawa tai kawai tana kuka.

  Zahra dake d'aki ta na jiyuta matsowa tai jikin toilet d'in tace " Seemah menene?"
  Kuka sosai takeyi Zahra mamaki ya kamata ta dad'e tana bugawa amma bata bud'e ba, Seemah kam ta dad'e tana kuka kafin ta daina, ita dana saninta d'aya dama batazo kasar ba kwata kwata da bata had'u da Jalal ba bare har sanshi ya kamata haka.

  Alwala tai ta fito, Zahra ta kalleta tace "Seemah menene?" Jijiga mata kai kawai tai alamar a'a ta wuce ta d'au sallaya.



   ☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆

  A asibiti kuwa Hajiya ta samu bacci mai karfi saboda allurar da aka mata, da daddare Habib da saninshi ya kwanta yai lamo kamar bai bacci, Abba ganin kamar Habib yayi bacci ya kalli Dad yace " Isma'il inada magana da kai."

  Dad ya kallleshi yace " inaji."

  Abba yaja numfashi sannan yace " Isma'il tambayar dai dana maka shekara ashirin da suka wuce ita nakesan in sake maka, Isma'il tsakaninka da Allah bakasan mahaifin Seemah ba?"

   Dad ya kalli Habib ganin da alama bacci yake yace " yaya wlh wlh bansan komai akai ba, sau nawa kakesan in rantsema." Ajiyar zuciya yai sannan yace "yaya kasan wa nagani yau?"

  Abba ya girgiza kai, Dad yace " Amadu nagani."

  Mik'ewa Abba yai yace " dafatan kasa an rufe mana shi?"

  Dad yai tsaki yace " ai ni abinda nagani yasa ma nakasa mai abinda ya kamata, kasan mahaifin waye?" Abba ya girgiza kai, Dad yace " wai mahaifin Jalal d'in da Seemah keso ne."

  Da mamaki Abba ya koma ya zauna yace " mene? JALAL? Taya hakan zata faru?"

  Dad ya runtse ido yace " kabari kawai Yaya abin ya d'auremin kai, ko ya akai Jalal har yazo company d'in mu yana aiki har suka had'u da Seemah? Har hakan ta faru?"

  Abba yace " Ikon Allah kenan, amma ai yanzu komai yazo gidan sauki, shi kansa Amadun ai ko kace ga Seemah ka bashi bazai aminta ba."

  Dad ya kalli Hajiya bai kara magana ba.

  Habib kam ya gama daskarewa agun da yake, meke faruwa? Ba Dad bane mahaifin Seemah kenan, sannan me? Bai masan mahaifin Seemah d'in ba? Meke faruwa kenan? Sannan mahaifin Jalal mene?"

   Inaaaaa ai ko mai zai faru dole ne gobe a bashi amsoshin tambayoyinsa d'an kuwa shine babban d'a kuma dolene yasan sirrin gidan su, bazai kara bari a sashi a cikin tunani haka ba.





 

    Jalal kam kwata kwata idanunsa basuga bacci ba zuciyarshi cike take da tunanuka kala kala, me ake nufi da Abba yasan Dad? Fitowa yai daga d'akinsu bai damu da daren dayai ba a waje ya zauna yai shiru yanaso zuciyarsa ta bashi amsar tambayoyinsa sai dai sam ya kasa lissafo komai abu d'aya dai daya tabbatar ma ransa shine, tabbas Dad yasan Abba kuma alak'ar dake tsakaninsu ba wai alak'ace ta mutunci ba, yazaiyi da auransa da ake shirin yi ranar asabar?



    B'angaren Seemeh kuwa tana zaune a falo kusa da Ammar, Zahra nata jansa da hira, itakam Seemah a zaune kawai take ba ta sa musu baki ba, can Ammar shirun Seemah yafara damunsa ya kalleta yace " Kanwata menene?"

  Kallansa tai batace komai ba, Zahra cikin zolaya tace " ba dai kuka zaki sake mana ba ko?"

  Seemah ta kalleta kawai tai kasa da kanta, Ammar jin haka yasa ya kalli Seemah yace " kanwata kuka ki kai?" Shiru tai hakan yasa Ammar yagane matsalar, Zahra ya kalla yace " Zahra d'an bamu guri muyi magana please. "

  Zahra ta kallesu sannan ta mik'e jiki a sanyaye ta fita, Ammar ya kara matsowa kusa da Seemah yace " Kanwata menene?"

  Idanunta ne sukai rau rau tace "yaya kaima kasani ai."

Goshinsa ya rik'e yace "oh God Seemah akan Jalal ne?"

  Kallansa tai cikin kalar tausayawa tace " yaya dama banzo kasar nan ba."

  Murmushi yai yace " Seemah kenan."

Ta kalleshi tace " Yaya inasan intambayeka wani abu, d'azu naje shiga d'aki naji ana zancen Dad duk abinda suka mai wai kuma ya rik'e yarinyar amana."

  Tai ajiyar zuciya tace " Yaya ban gane kalaman me suke nufi ba."

  Ammar yai shiru can yace " Seemah ni kaina ban fahimci inda kalaman nan suka dosa ba, a farko na d'auka da ni suke to amma daga baya na gane ba ni bane, to amma me kalaman suke nufi?"

  Ta jinjina kai tace " mu tambayi Dad gobe sai muji ko?"
Kai ya d'aga alamar eh
...









© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

  ��‍♀

1 comment: