*ZUCIYA*
_ĸowa da ιrιn тaѕa_
© *na Ayυѕнer Mυнd*
ayushermohd.blogspot.com
16
Habib shima mamakin ganin Yarinya ta fito daga d'akin Ashraf yake, itakam Nafi duk ta rikice duk da bata kawo komai a ranta ba amma ganin ga mumy da su Ashraf yasa jikinta ya shiga tsuma.
Mumy a zuciye tace"Ashraf wani salon iskanci ne kuma hakan? Kanada hankali kuwa? "
Ashraf ya mike tsaye sannan yai wani murmushi ya kalli Mumy sannan ya kalli Nafi yace "Me kike nufi da kalamanki Mumy? "
Cikin takaici da fada tace "au tambaya ma kake? Yarinyar da ka kawo inganta ta fito daga d'akinka kace wai me nake nufi? "
A zuciye ta karaso kusa da Nafi wace ta rakub'e da jikin bango jikinta banda tsuma ba abinda yake, hannu ta d'aga a zuciye zata kai mata mari, Ashraf da sauri ya rike hannunta sannan ya kalli Nafi wacce kana gani kasan a gigice take ya maida dubansa gun Mumy yace "in kuma kika daketa ba da hakkinta ba fa? "
Mumy ta kalleshi cikin takaici tace "hakkinta?"
Ashraf cikin takaici yace "kina tunani ni Ashraf zanyi tarayya da wacce ba matata ba? Bare wannan? Me take dashi? Me kuma nagani? Dan kawai yarinya ta fito daga d'akina bazakiyi tunanin komai ba sai zargi??"
Mumy ta kuramai ido sai dai da alama bata gamsu ba.
Ashraf ya runtse ido zuciyarshi ba dadi, Habib ya kalla ya mai alama daya fita da Nafi, nan Habib ya matso yace mata muje.
Nafi duk ta gama rud'ewa tama manta mai ma ya kawota Ashraf kawai take kallo idanunta a hankali suka fara zubarda ruwa.
Suna fita Ashraf ya kalli Mumy idanunsa shima sun kada sosai ya shafi kansa sannan ya matsa kad'an daga inda take, yace " Ko a mafarki ban tab'a tunanin haka kika d'aukeni ba. "
Yana kainan yai waje a zuciye, jikin Mumy ne yai sanyi sai dana sani ya shigar mata, sai a lokacin ta kula da tsintsiya da abin mopping, kai ta dafe tace "dama yana nisanta kansa dani yanzu kuma na kara jan wani layin. "
Nafi kam suna fita kanta kp d'ankwalli babu tafiya kawai take, Habib ya kalleta yace " Karki damu ba abinda zai faru. "
Juyowa tai ta kalli Habib sannan ta tsaya tace "Ba abinda Mumy zata mai ko? "
Hawaye suka biyo bayan kalamanta, dariya Habib yai yace "wa? Ashraf? Ke kiji da kanki bawai ki tsaya tunanin wanda kila yanzu yama manta abinda akai ba. "
Juyawa tai kawai ta cigaba da tafiya, Habib ya matso yace "ban sanki ba amma. "
Nafi tace "tare muka dawo da yaya taimakona yai. "
Dariya sosai Habib yasa anda sai da Nafi ta tsaya tana mai kallan mamaki tace "menene? "
Sai daya tsagaita yace "taimako? Wa? Ashraf? Don't make me laugh. "
Nafi ta juya batace komai ba dan bata fahimceshi ba.
Habib yace daga wani gari kike?
Rigar Datti.
Maimaitawa yai cikin mamaki yace " ina kenan? "
Ita kanta batasan ina zata ce ba dan bata sani ba, ganin sun iso ta kalleshi tace "Nagode."
Murmushi ya sakar mata sannan yace "in Little ta dawo kice mata Habib yazo sai dai yanzu zan koma zan dawo nextwk. "
Kallansa tai a ranta tace "shine Habib d'in kenan? "
Ido d'aya ya kashe mata yace "what? Badai har kinji labari na ba? " ya d'aga mata gira yace "ahh kinsan nid'in akwai farin jini ga masoya. "
Batasan sanda ta murmusa ba, Habib ya nuna ta da hannu yace" kinyi dariya ko? "
Juyawa tai da sauri tai ciki wani sansanyan murmushi ya saki yace " she is soo beautiful and funny. " gashin kanta ya tuno wanda aka mai kitso manya sak dai ya kwanta har bayanta, yai murmushi sannan ya juya a ransa yace "inta girma za'ai mace anan. "
Nafi kam tana shiga ta zauna a kasa, kalaman Ashraf ne kawai ke dawo mata, Me take dashi? Me na gani? Me yake nufi da kalamansa?
Shiru tai kawai, Jitai ana kwankwasa kofar cikin zafi, ta mike da sauri ta bud'e, batai auni ba bakuma ta kula da waye ba taji mari gauu a fuskarta, da sauri ta rike gun wanda marin taji kwarai kuma har idanta na hago, dage idan tai cikin tsoro ta d'ago, jitai ance "Dan kut........ Ke har kin isa in saki aiki yau ki k'i zuwa? "
Nafi ta kalli Umma sai dai ta kasa cewa komai sai kai kawai datake jijigawa, Umma ta sa kafa ta turata ciki, tace"wlh kinji ma fada miki ko da wasa akace kinyi fashin zuwa gun aiki sai na sa an kwantar dake a asibiti saboda duka. "
Tana kainan ta juya, Nafi ta zube a gun sai kuka, sosai take kuka tana kuma tuno mahaifinta da mahaifiyarta, sai dataci kuka ta koshi sannan ta mike tai kitchen dan basu hakuri.
Sai dai me? Idanta kankace me ya kumbura saboda marin datasha a gun.
A b'angaren Ashraf kuwa yana fita ya fizgi mota da gudu kawai yana tafiya meyasa Mumy zata mai haka? Ita fa Mahaifiyarsa ce inda wani ne da sauki amma mahaifyarsa? Meta d'aukeshi? Ko zinar zaiyi mai zaiyi da wannan kwailar? Yar kauye? Wacce kila bama tasan me tarayya yake nufi ba.
A zuciye yai wani Rv ya kwantar da kansa a kan sitiyari wanda yaji yana saramai sosai.
Nafi kam bayan taje kitchen Goggo ta taso da sauri ta karaso gunta tace "Nafi me ya sami idanki? "
Nafi tai murmushi tace "bigewa nai. "
Shiru Goggo tai sannan tace "d'azu Hajiya tazo nemanki, amma da alama wani munafikin ne a nan ya fada mata bakizo ba. "
Nafi tai murmushi tace " Laifinane ai Goggo daban zo ba "
Cikin tausayi Goggo tace "Nafi idan nan naki fa ya kamata ko kankara asa a tsumma ki dan gasa ko kuma kisa lemon tsami kiyi ta mulmulawa. "
Nafi tai kasa da kai tace "Kiyi hakuri Goggo. "
Hannunta ta kama tace "kamar 'yata haka nakejinki karki damu da komai kinji? Ki kula da kanki. "
Nafi ta d'aga kai sai ha hawaye sun silalo mata, nan Goggo ta shiga bata hakuri, ta dad'e kafin ta amso abincinsu itada little ta fito.
Tazo wucewa ta ga motar Ashraf ya gangara yai parking tsayawa tai tare da yin kasa dakai dan karyagaidanta, sai dai ga mamakinta gani tai ya d'auke kai yayi gaba, Nafi ta kakaro murmushi kawai tayi tabi bayansa da kallo, ta sani laifinta ne mai ya kaita yin bacci? Ita kanta batasan ya akai ba.
Tana shiga d'aki Little tace "Nafi tun d'azu nake jiranki. "
Nafi ta ajiye abinci, zata zauna Little ta taso da sauri ta riketa tace "Nafi meye hakan? Meya sameki? "
Nafi tace "bigewa nai. "
Little zatai magana taji karar wayarta ta d'aga ganin Yaya, bayan sun gaisa yace "Little in anyi magrib ki d'au Nafi kuje asibiti sannan kice ta bar aikin sai ta warke. " abinda ya fada kenan ya kashe wayar.
Nan Little ta fada mata gani tai Nafi ta shiga yin murmushi tana kasa da kai, zuciyarta taji tayi wasai kenan ba haushinta yaji ba? Kenan zata cigaba da mai aiki? "
Little ta saki baki tana kallanta, me kenan? "
*THE INNOCENT TEAM*
Allah shikara basira littapi yana dadi sosae da sosae
ReplyDeletePlease ki yi completing din NI DA PRINCE
ReplyDelete