Saturday, 4 March 2017

JALALUDEEN 77

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

  
*Luv u oll my fans.......*

   No.7⃣7⃣


   Seemah na zaune tayi wanka tana jira agama ma Zahra kwalliya sannan a mata, rigace doguwa ta atamfa a jikinta aiki ne a jikin rigar har wajen ciki d'inkin yayi masifar kyau, a zaune kawai take amma gaba daya batajin jikinta daidai, jitai an fara kud'a hakan yasa gabanta ya sake fad'uwa, suka shigo d'akin sukace an d'aura, Seemah kasa tai da kanta ganin wayarta tai kara yasa ta daga, Zaid ne da sauri tace   " Ya Zaid ina ya Ammar? Jinake kamar wani abu ya sameshi."
  Zaid yace " Seemah ki fito ina waje mijinki ba lafiya."
" Naam? Me kake nufi?"
  Kashe wayar yai dan jiyai baisan me zai ce mata ba,  A zabure Seemah ta mik'e ko hijab bata dauka ba d'ankwalin data yafa akanta kawai ta sura tai waje ko takalmi batasaba.

  A waje taga mutane sun taro anacewa " waye kuma Jalal?"
Tsayawa tai turus, can kuma sai tai tunanin ko ba Jalal d'in ta suke nufi ba, waje tai da sauri ta fada mota Zaid ya kalleta sannan ya ja motar, duk ta rikice tace " Ya Ammar meya samu Ya Ammar d'in?"
Kallanta yai jiki a sanyaye yace " Kunyi magana da dad?"
Ta girgiza kai tace " a'a yadai kirani da safe yacemin, ko mai na rayuwa mukaddarine, haka kawai yacemin."

   Suna isa asibitin suka fito, duk Seemah ta rikice, harsunje shiga d'akin wayar Zaid tai kara, ya kalleta yace " nan ne ki shiga."

  Ko kula shi batai ba ta fada dakin, daga nesa tafara ganin kamar ba Ammar ba, jiki a sanyaye ta karasa kusa da gadon, turus tai ganin Jalal a kwance duk ya rame sai bacci kawai yake.

   Hawayene suka fara zubo mata a hankali takai hannu gefen fuskarsa hawayenta ne suka shiga d'iga kan kuncinsa, sai zubowa sukeyi ta kasa magana sai hawaye kawai take.

   A hankali Jalal yad'an bud'e ido jin ruwa na d'igarmai, kallan Seemah yadauka mafarkine yasa ya kara lumshe ido, hawaye kawai takeyi, can ya sake bud'e ido daidainan ta kalleshi, idanu suka had'a yad'an motsa bakinshi kad'an yace " Meemah?"

  Hawayene ya cigaba  da zubo mata tace " Deen? Me ya sameka haka?"

   Sai a lokacin ya tabbatar ba mafarki yake ba kallanta yai tare da cewa " me kike anan?"
  " Naam?"
Tafad'a tare da kallan d'akin sai a lokacin ta tuna kamarfa Ammar ne yakamata ta gani ba shi ba, ta d'an juya tace " Ni cemin akai inzo in duba mijina na d'auka ya Ammar ne bashida lafiya."

  Jalal ya d'an juya ido yace " meya sami Ammar d'in?"

  Ta d'aga wayarta ta kira Zaid ga mamakinta Ammar ne ya d'aga.
Cikin tsanin damuwa tace " Ya Ammar kana ina?"
  Yace " Seemah?"
   Yanda ya kira sunanta yasa jikinta yai sanyi ta kasa amsawa.

  Cikin wata murya yace " ki kula da mijinki, ke yake bukata a wannan lokacin."
Da mamaki tace " ban gane ba? Kana ina?"
  Yai shiru can ya daure yace " An daura muku aure da Jalal karki damu dani ko kiyi tunanin wani abun, kawai ki kulada lafiyar mijinki."

   Jitai kalaman sun shigar mata kunne banbarakwai sai dai kafin ta sake magana Ammar ya kashe wayar.

  Kallan Jalal tai sai dai ganin yanasan tashi ya kasa saboda cikin dake bayansa, yasa ta daure matsowa tai zata taimaka mai, kallanta Jalal yai yace " bashi kawai, ki nemomin likita."

   Bata kulashi ba kawai ta shiga taimaka mai, tana gamawa ta duba ga kayan shayinan da abinci hakan yasa ta hadamai shayi ta mikamai tace " ina zuwa."
Kallanta yai yace " kina zuwa ina? Me zaki dawo yi anan? So kike ran Ammar ya sake b'aci?"
  Kallan yanda ya rame tai ta kauda kai tare da cewa ni kaina ban fahimci abinda ya Ammar d'in yake nufu da an d'aura mana aure dakai bane shiyasa nakesan ganinsa.

   Bata jira mai zaice ba tai waje, Jalal ya kara maimaita kalamanta.

   Seemah na fita taga Dad yana tahowa shida Abba, da sauri takarasa gunsa yace   " Seemah muje ciki."

Kallan mamaki tamai sai dai ba zata iya musu ba.
D'akin Jalal suka koma bayan sun zauna shiru, nan Dad ya warware musu duk abinda ya faru jiya zuwa yau.

  Seemah kuka take sosai, yana gama maganar yace " dan haka ki zauna anan ki kula da mijinki ki bar sha'anin biki su Zahra sayi."
  Ta kasa magana haka ma Jalal wanda yakejin maganar kamar ta tsuniya, ganin halin da suka shiga yasa Dad ya mik'e shida Abba sukai waje.

  Seemah ganin sun fita yasa ta mike da gudu ta bi bayan Dad ta baya ta rungumeshi tana wani irin kuka, Dad ya daure ya juyo da ita setinsa yace " Seemah?"

  Cikin tsananin kuka tace " Dad meyasa ka bar Ya Ammar yai haka? Kamanta nace na hakura? Sannan babban burinka ne fa?"

  Dad yad'an shafa kanta sannan ya kalli kafarta da ko takalmi babu yace "  a haka kika fito ba ko takalmi?"

   Hawayenta ne ya karo tace " Dad ina Ya Ammar d'in? I have to meet him. "

Dad yai murmushi yace " karki damu yayanki yace ki kulada Jalal."

  Yad'an zareta daga jikinsa yace " karkiyi tunanin komai sai mijinki."
Yana kainan ya juya ya fara tafiya.

   Tsugunnawa tai a gun ta shiga kuka, ta dade agun sosai mutane sai wucewa suke suna kallanta dakyar ta daure ta mike tai cikin d'akin ga mamakinta Jalal ta gani ya mik'e yana sa rigarsa, da sauri ta karasa inda yake? Idanunta duk sun canza tace " Ina kuma zaka?"

  Kallanta yai yace " me Ammar yake tunani? Ni zanje in mai magana."

  Cikin kuka tace " ni ina zansan me yake tunani, amma kaidai bazan barka ka fitaba bayan ba lafiya gareka ba."

  Kallanta yai cikin wani yanayi yace   " Meemah tunanin halin da Ammar yake ciki nake."

  Ta goge hawayenta tace " naji wannan amma ka koma ka kwanta sai inkira Ya Ammar d'in."

  Jiki a sanyaye Jalal ya zauna, ta mikamaj wayarta tareda dialling d'in number Zaid.

  Ammar ya d'auka, Jalal yace " Ammar meke faruwa?"

  Ammar yad'anyi murmushi kad'an yace  " meke faruwa dame? D'an na bar maka Seemah ko dan kana tare da ita?"

  A zuciye Jalal yace " Ammar meke damunka ne? How can u joke now."

  Ammar yai ajiyar zuciya yace " kai dai dakake lovesick yanzu sai ka ware."

  Jalal yace  " Ammar ban aminta da...."
Katseshi yai da cewa " ka saketa to."
Yanakai nan ya kashe wayar, shiru Jalal yai yana maimaita kalmar saki.

  Seemah ta zauna kusa dashi kadan tace " me Ya Ammar d'in yace? Wasa yake ko?"

  Jalal ya kalleta cikin mamaki yace " da alama dagaske yake tunda haryake cemin wai in sakeki ."

  Ta kalleshi da mamaki, mik'ewa tai da sauri tace " Me Ya Ammar yake tunani?" Tafad'a tare da hura iska.

  Jalal ya daure yace " taimaka min in kwanta please. "
  Harararsa tad'anyi tace " akan me?"
Kallanta yai sannan ya daure yace  " hmm kiramin ko nurse ne."
Ta d'an tab'e baki tace " nurse d'in ai kala biyu ne, maza da mata wacce kakeso a kira ma?"

  Jalal ya kalleta tunowa yai da masifarta ta da yace " auu kiramin koma waye ai ni patient ne."
Ta makamai harara tare da turashi gado da d'an karfi, zafi yasa sai daya saki kara yace " me kuma nai kinsan dai ba lafiya ce dani ba, irin wannan tureni?"
  Ta harareshi tare da komawa gefe ta zauna, Jalal ya juya kai kamar mai bacci dan jin abin yake banbarakwai.

  Text tama Ammar kamar haka.
_Ya Ammar na sani sarai kayi haka ne dan farin ciki na sai dai Ya Ammar aikin gama ya gama bani da abincewa a wannan lokacin, kalma daya zan iya fadama shine Allah ya sakama da mafificin gidan aljanna ya kuma baka matar data fini._

   Tana turawa ta kwantar da kanta jikin kujera tana kallan Jalal dake kwance kamar mai bacci, jitai yace   " Kallan fa?" Ya fad'a a hankali tare da bud'e idanunsa."

   Bata d'auke idanunta daga kansa ba tace " wai me ya sameka?"
  Ya kalleta shima yace " Ni kaina bansan me ya sameni ba, kawai ganina nai a asibiti." 

   Ta lumshe ido sannan tace " ban tab'a tunanin zan ganka haka ba."
  Shiru yai can ya daure yace " Meemah ina farinciki a raina kuma ina bakin ciki."
  Name fa?

  Kallanta yai yace " ina farincikin kasancewa dake sai dai ina tausayama Ammar danasan yana sanki kamar ransa."

  Seemah jitai idanunta sun ciciko tad'an daga kanta tare da sasu a jikin cinyarta tana hawaye.

  Jalal yace " tunda nake ban taba tunanin zan aureki ba ko a mafarki shiyasa nakejin abin kamar ba gaske ba."

  Seemah kam hawaye kawai takeyi, Jalal ya daure yace " Meemah zo nan."
A hankali ta d'ago ta kalleshi idanunta duk sun kumbura, hannu ya miko mata yace " please! "
  A hankali ta mik'e kamar wacce kwai ya fashema ta karasa kusa dashi, hannu yasa ya jawota jikinsa ya rungumeta, idanunsa sunyi jaa yace a hankali cikin kunnenta " Meemah dagaske ke matata ce? In mafarki ne banasan na farka in kuwa gaskene to lallai zan baki farincikin da zaisa hankalin Ammar ya kwanta ya kuma ji dadin had'in dayai."

  Kanta ta kara cusawa cikin kirjinsa mamaki take yanda wata zuciyar ke neman sanyata cikin wani shaukin dabai kamata tai ba a wannan lokacin.

  Sun dad'e sosai a haka, har Jalal bacci ya fara d'aukansa.

  Seemah dataji haka yasa ta barshi sai da barcin ya kamashi sannan ta zare jikinta a hankali, kallansa ta tsaya yi, a hankali takai hannu gefen fuskarsa ta shafa.

  Kasa d'auke hannunta tai daga fuskarsa, zuciyarta sai bugawa takeyi lalai tanasan Jalal itakanta ta sani to amma ya zatai? Haka zata amshi auren nan ta manta da hallacin Dad? Shiru tai tana tunani kala kala.

    

     Ta dad'e a haka ta fara kokarin mek'ewa taga ashe Jalal na rik'e da d'ayan hannunta.
   Kwantar da kanta tai saitin inda Jalal yake kwance, bata sani ba itama sai gani tai bacci ya d'auke ta.


   Can Jalal ya bud'e ido a hankali ya kalli Seemah dake kwance a saitinsa, kura mata ido yai yanajin wani shaukin santa na d'ebarsa.


   Murmushi yai sannan yace " Ammar anya ya kamata inbi abinda zuciyata ke raya min?  "

Bakinsa yakai saitin goshinta a hankali ya sumbata tare da lumshe idanunsa.

 





   © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

No comments:

Post a Comment