🏵🏵🏵🏵🏵
iLHAM😪
🏵🏵🏵🏵🏵
Na Ayusher Mohd✍🏼
1⃣2⃣
Ilham ta share hawayenta tare da mikewa tsaye tace yaya dazan shiga makaranta mafa maimakon Fatima Ashiru sai mumy tasa akasamin Fatima mahmud yai shiru shikanshi yasan akwai wani abu kuma kwakwalwarshi nasan tuno mai wani abu daya faru yana yaro sai dai hkn ya faskara suna cikin hk meenal takara zuwa da gudu tace yaya kazo yaya bilal yazo dasauri ya mike yace ilham zo mu shiga ciki tace tab ni ai banasan ganin wannan abokin naka mara mutunci ina nan khalil yai murmushi sannan yai cikin gida itakam nan ta zauna tana hango wannan ginin da aka kewaye kuma umma ta musu gargadi karsu kuskura suje gun mutum daya ne yake zuwa wani likita tai ajiyar zuciya tare da mikewa
Sam ta manta bilal nannan tai cikin gida shikuma ya mike zai tafi khalil na bayanshi zuciya daya ta shigo shima yazo fita ai kuwa sukai gware yana dagowa a zuciye ya hankadata yace dama nasani ai bazaki taba ganina ki wuce ba sai kim batamin rai jiyadda kikamin da kaya ya shiga duba rigarshi ba wani abu yai ba amma bilal da fitina khalil yace hb bilal kamata ahankali yarinyace kuma daga gani tafika jin jiki ya fita ya dagata yana kade mata jiki
Ilham ta kafeshi da kallan tsana idanta yai jaa bilal yace kin dauke idan daga kaina kosai na tsokaleshi tace wai ni mena maka ka tsaneni yace kinfi kowa sani ya fito ya bigeta takusa faduwa khalil ya tareta ta mike tai cikin gida
Khalil ya biyo bilal yace wai abokina mai kanwata ta maka? Yace kai kake ganin yarinyar nan salaha batada kunya rannan bakaga dukan da sukawa meenal ba yarinyarnan duk yanda nai tabata hakuri sai tace ita batai laifin komai ba shiyasa nisam ta fita daga raina khalil yace kaii ban yarda ba ina ilham ina dukan meenal? Bilal yace kaika sani ya wuce ya shiga mota driver din gidansu yajashi sukai gida
Ilham ce da safe bayan sun tashi daga barcita gyara dakinsu yanda ta saba sannan ta shiga dakin mumy ta gyara ta share sannan tai wanka tasa uniform din makaranta dakarfi taji meenal na kiranta ta fito rike da safa tace menene? Tace kije inji mumy tace to tare da karasawa falom a zaune taga dadynsu ta tsugunna tace dady ina kwana yace ilham kim tashi lafiya tace eh yace good tace mumy fa yace tana daki hkn yasa tai cikin dakin ashiru yabita da kallo zuciyar shi na tunomai fatimarsa
Tana shiga hadiza tace zo nan takarasa tace kira nai intuna miki karfa kimanta meenal yayarkice duk abinda tafada amakaranta kiyi hkri tace mumy amma meyasa zata dinga cewa mutane ni mai aikinsu ce? Ran hadiza yafara baci amma tadaure tace to meye dan ta fada basai ki share ba? In sun yarda kansu in basu yarda ba su suka sani Tace shikenan tace yauwa kidinga yi mata class work kuma sannan intace kimata abu kidingayi kece karama dole kiyi tace to sannan ta mike tafito tai gun umma tagaisheta sukayi breakfast suka tafi skul
Sam ilham batada kawaye dan makarantar masu kudice da a wata makaranta take sai dady yamaidata tasu meenal da khalil yanzu batafi 2 month a makarantar ba
Meenal bataso ba dan tun tana karama mumy ke nuna mata ba matsayensu daya ba hkn yasa tafadawa yan ajinsu ilham yar masu aikinsu ce
Ilham na sauka daga mota taiwa khalil sallama tai class dan bangarensu ba daya ba su suna primary 2 ne itada meenal
Suna shiga malamin english ya shigo ba raba musu takardar test din daya musu jiya kaf class din ilham ce highest dan malamin sai dayasa a tafamata haushi gun meenal kuwa kamar me. ALLAH yabawa ilham baiwar mahaifinta duk abinda takaranta ko ta saurara ya zauna
Lokacin break nayi da gudu tai bangaren su khalil dan ta nunamai paper dinta taga wani class mate dinsa tace dan Allah inka shiga ka kiramin yayana kace mai ina baya yace to tai bayan class din da gudu ta juya baya tana jiran tawa khalil surprise shikuma dan aiken dayaje yace bilal ina khalil? Yace yaje shop yace eyya dama kanwarshi ce ke nemanshi tana bayan class shikam yadauka meenal ce yai baya yana zuws yaga ta juya baya yace ya akai? Ilham ta juyo dadan tsallanta yace yaya suprise tare da ware takardar sai dai ganin bilal yasa ta sauke takardar tare da turo baki yadan yi karamin tsaki bilal ya matso daf da ita ya kama kunanta da karfi ta fizge tace da zafifa yace matsonan ni kikawa tsaki? Tace nifa ba tsaki nai ba yace ko tace eh ya kamo hannunta da karfi ya matse yace wato dan ba khalil bane ga marainin wayon ki ko tadan kwala kara tace hannuna yace sai kim fadan mekikai ta juyakai tafara cin lebenta hk take in taurin kan ya motsa ya saketa ganin tafara abin ya rankwasheta akai ya wuce ta bishi da harara tai hanyar class jitai an rufe mata ido tace waye kuma? Khalil ya juyo ta gabanta yace oh god waya tabamin sister ta kafin tabashi amsa yaga lebenta na jini dasauri ya ciro handkerchief ya goge mata yace muje ki kuskure baki waya tabaki? Tace bakomai sannan ta mikamai takardar ta yagani yace wow good girl kai wannan kanwartawa tana jaa tace menake jaa yai dariya yace kanki na jaa tace niban gane ba yai murmushi yace no hausa hk sukai tayi harta manta abinda bilal yamata
suna komawa gida taga meenal tayi gun mumy da gudu batasan meta cemata ba itadai taga mumy taxo a zuciye tace ina paper dinki da aka rabamuku ta mika mata taga taci 10/10 tace amma kinji jiki dan bakin ciki meenal taci 5 ke kice 10 shine dan kinsan abu bazaki fada mata taci ba? Tace mumy ba hk bane umma dake zaune tace zo nan ilham ta mike taje tace daga yanzu karki kuskura ki kara wuce meenal kota menene kuwa ilham ta kallesu dukansu sannan tai waje da gudu khalil ya bita
By Ayusher Mohd📚
No comments:
Post a Comment