🏵🏵🏵🏵🏵
ILHAM😪
🏵🏵🏵🏵🏵
Na Ayusher Mohd✍🏼
2⃣
Tana isa taga ya fado kasa takarasa da sauri takarasa tafara kokarin dagashi dakyar ta samu tamaidashi sai numfashi take alamar wahala tace nadauka kayi bacci doctor ya kalleta yamata alama da hannu waye? Tace bafa kuwa umma ce taxo taji ya jikinka yake ya kalleta alamar ina? Baxai yiwu ba tace kwanta nima wanka zanyi inzo inkwanta yadaga mata kai tayi hanyar toilet ilham tasa kuka ta juyo ta karasa gunta tashiga jijigata ganin kamar yunwa takeji ta fara shayar da ita mahmud kurii yai da ido yana kallanta yana tuno tsantsan soyayyar dasuka nunawa juna ya lumshe ido kamar yana bacci ita kam fatima ganin ilham takoma bacci yasa ta kwantar da ita tai toilet.....
Washe gari da sassafe ta tashi tai cikin gida tafara girki dan wannan aikintane inji umma daga sanda mahmud yakwanta ciwo tace girkin gidan yatashi daga gun matsu aiki ya koma kanta haka take aikin ilham nabayanta sai data gama komai ta jera a dinning sannan hadiza tafito rike da yarta a hannu taba ilham wata 2 tayiwa fatima wani mugun kallo sannan tace umma tace kije inkin gama aikin ko kulata fatima batai ba haushi yakama hadiza tai cikin daki
fatima ta rike kugunta jin bayanta ya amsa sannan takalli agoggo karfe 8:00 tasan lokacin tashin mahmud yayi gashi umma nakiranta hk tayi part din umma jiki a sanyaye
Tana shiga tatarad da umma a kishingide takarasa tace umma ina kwana ta kalleta a wulakance tace dan iskanci kwashe kudin account dinki kikai? Tace umma ban gane ba umma tace zan haska miki mari wato kina bakin ciki dan hadiza na amfani da kudin ko? Kudinkine ? Ko guminki ne? Fatima tace a'a amma ni umma inama nake zuwa bare in cire kudi tace to kina nufin hadiza ce ta cinye?tace banceba umma tace to kisan yadda zakiyi mahmud yatura miki kudi ko kuma in saki kisaida filin dayasai miki fatima tace umma😳 ai kamar jira take tahauta da fada fatima kuwa ko gezau batai ba tana gamaji tamike batare datace komai ba tana fita tasauke ilham ta rungumeta tace ilham yazanyi?itakam ilham batasan ma me ake ba sai murmushi take
Tayi part dinsu taji anrikota ta juyo ciki da mamaki Ashiru tagani dasauri ta kwace hannunta tace malam meye hakan? Ashiru yace fatima dakin yarda dani da duk wannan abun bazai faru ba ta kaleshi shekeke tace ko😏? Yace Allah fatima ni nasan meyakamata tace Ashiru kasan Allah idan baka fita daga idona ba xakasha mamaki ta wuce tai part dinsu tana isa tai gun mahmud idanshi 2 yasa laptop agaba yana abu dasauri ta ajiye ilham tai kusa dashi tace doctor am sorry ya girgiza mata kai alamar ba komai ta dauko kujerar guragunsa tasashi sannan ta turashi toilet har wanka ta taimakamai yai sannan tadawo tadau ilham itama tamata
Saii datagama shiryasu sannan tai cikin gida dan dole sai sun gama break fast zatazo tadau ragowar gashidai mijinta ne mai kudin gidan da kudinshi ake komai amma bayadda xatai 😪
Wannan rayuwa tana bata wahala sai dai fatanta Allah yashige mata gaba hk tadau abincin takaima mahmud yagama ci sannan taci tai wanka
Wannan kenan.....
By Ayusher Mohd📚
No comments:
Post a Comment