Tuesday, 14 February 2017

JALALUDEEN 64

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ
     ๐Ÿพ *Jร…ฤนร€ฤนร™ฤŽฤšฤšร‘*๐Ÿพ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ






 Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com


   No. 6โƒฃ4โƒฃ


  Seemah ta shigo falon itada Ammar da Zaid, kowq ya tattara hankalinsa akan Tv d'an ganin me Jalal ke kokarin isarwa.


   A b'angaren Jalal kuwa bayan sun gama shirya komai, Senate Abdul ya shigo cikin isa directors da producers d'in kowa ya fito yana gaidashi, Jalal kam na zaune akan kujerar da zai gabatar da shirin, bayan sun gama gaisawa ne Senate ya kallesu yace " da wa zamu gabatar da shirin ne? Ban samu na ganshi ba."

  Abbas ya juya yana neman Jalal can ya hangoshi gaba d'aya ma hankalinsa baya kansu, da karfi yace " Jalal?"
 Juyowa yai ya kalleshi, Senate ma ya kalli inda director d'in yake kallo, Jalal ya musu murmushi sannan ya d'aga musu hannu, Senate ya kara kallan Jalal yace " waye shi dabazai zo gaidani ba?"

  Abbas yai gyaran murya yace " hmm dashi zaku gabatar da shirin takardun da zakuyi amfani yake dubawa, ai shi haka yake bashi da magana." Abbas kam yai kokari gurin kare Jalal.

  Abdul yai murmushin jin dad'i a ransa yace indai bashida magana ai hakan sai yafi dad'in yin shirin.

 Kara kallan gun da Jalal yake yai kamar yasan fuskar amma a ina? Watsar da tunanin yai nan ya karasa ya zauna a kujerar dake kallan ta Jalal.
  Jalal ya sakar mai murmushi tare da gaidashi, Abdul ya aksa tare da cewa lokaci yayi mu fara? Ina d'an sauri ne.


  Jalal ya d'aga kai sannan ya mik'e ya duba komai, sai daya tabbatar komai yayi sannan karfe 2 dot da buga, suka fara gabatar da shirin kamar haka.

  Jalal ya gaida mutane sannan ya sanar musu da sabon shirin su na yau da kuma babban bakon da suka gayyata wato *Senate Abdullahi* wanda yake tunanin neman kujerar shigaban kasa.

  Bayan Senate ya gaishesu ne shima Jalal ya kalleshi yace " Honourable Senate kayi mukamai da dama tun daga kan Chairman har zuwa matakin da kake yanzu, shin ka tab"a fuskantar wani matsala a harkar siyasarka?"

 Senate yai murmushi yace " hmm gaskiya ban tab'a samun matsala ba sai ma kaunar da talakawa ke nunamin inajin dad'i kwarai da yanda suke bani had'in kai."

  Jalal yai murmushi yace " Gaskiya ne mutane na sanka, Allah ya kara d'aukaka."
 Senate ya amsa da Ameen.

 Jalal yace " Yanda mutane kesanka baka tunanin ka tab'a bata ma wani rai ko musgunawa talakawa da saninka ko cikin rashin sani?"
  Senate ya had'a hannayensa biyu tare da kara sakin fuska yace " a iya sanina ina kokari gurin kyautatawa talakawa da mutane ina kuma kaunar talakawa kamar yanda nakesan nawa 'yan uwan to menene zaisa ni na wulakantasu? Bayan sun zama jinin jikina."

  Jalal ya saki wani mugun murmushi ba shakka wannan mutumin ya iya siyasa Jalal ya cigaba " Gaskiya ne kam kana kokari gurin kyautatawa mutane, sai dai ina fatan Allah yasa yanda kakesan talakawa 'ya'yanka ma su so ka haka."



   Gaban Senate ya fad'i me mutumin nan yake nufi? Bai amsa mai ba Jalal yai saurin cewa " yanzu 'ya'yanka nawa?"
  Abdul ya kalleshi me ya kawo zancen 'ya'ya nan?
 Amma ya daure yace " 'ya'yana uku mata 2 sai namiji yanzu yake primary 6."
 Jalal ya jinjina kai yace " Allah sarki, Allah yaraya manasu."

  Abdul ya amsa da Ameen.
  Jalal ya kalli Camera yace " Kada ku manta kuna tare da babban d'an siyasan nan wanda talakawa ke kaunarsa wato Senate Abdul. "
 Nan aka sake nuno Senate yana murmushi.
 Jalal ya kalleshi yace " Sanda ka fara siyasa kayi aure ne?"
 Abdul ya girgiza kai yace " A'a lokacin dai an kusa yin auren."
  Jalal ya jinjina kai yace " munji labarin matar da zaka fara aura Allah baiyi auren tsakaninku da ita ba ko?"
  Abdul ya bugama Jalal wani kallo tunawa dayai live ake d'aukansu yasa ya saki murmushi yace " gaskiya ne, matsala aka samu aka fasa auren."


   Jalal ya d'an gyad'a kai alamar tausayi yace "Ayya!!! Na tabbata matsalar badaga kai bane."
  Abdul ya d'anyi kasa dakai kamar me shirin kuka yace " amanata taci."

  A ran Jalal yace " thank God."
  Jalal ya kalleshi da mamaki yace " Amana kamar tame fa? Na tabbata masu kallo suna san ji."

  Abdul ya had'iyi yawo yace " Amanata taci da wani banasan tuna asiri irin wannan a bainar jama'a."

  Jalal yace " gaskiya ne ai tona asiri ma bashi da dad'i sai dai muce Allah ya rufa asiri."

 Abdul yace " Ameen."

  Jalal ya kalleshi yai murmuaji yace " Yanzu amma nasan ka yafe mata ko?"

 Abdul ya kalli Jalal yace " na yafe mata d'an ni mutum ne mai saukin kai banasan kulatar mutum."

 Jalal yace " I see, amma shi wanda yaci Amanar taka fa? Kana da wani sako zuwa gareshi ne ko kuwa shima ka yafemai?"

  Abdul ransa ya fara b'aci ya kalli Jalal sannan ya daure yace " ba wani sako danake dashi, Amanata ya riga yaci nikuma na yafemai ."

  Jalal ya d'an rangwab'ar dakai sanar ya murza ido, yana bud'e idanunsa Abdul yaga idanunsa sun kad'a sunyi Jaa kana ganinsa kasan b'acin rai ne karara a bayyane a idanunsa tsoro ya fara kama Abdul.
  Jalal ya kalleshi da jajjayen idanunsa yace " Amma a binciken da mukai sai mukaji kamar fyad'e akama matar da zaka aura?"

  Ba Abdul ba hatta ragowar masu recording sai da suka kalli Jalal cikin tsananin mamaki, a falo kuwa gaba d'aya sun kame kallan tv kawai sukeyi.

  Abbas ya rasa yanda zaiyi yama Jalal magana tunda dai abin live ne.

  Abdul ya kasa magana, Jalal ya d'an murmusa ta gefe yace " Ina mamakin namijin dazai iya yafema wada yama matarsa fyad'e ana saura kwana biyu auransu."

  Abdul idanunsa shima suka fara canza kala, tsoro ya fara kamashi, Jalal ya kara wani murmushin yace " gaskiya na jinjina maka ba kowani namiji bane zai iya yafemasa."

  Abdul hannunsa ya fara rawa cikin rawar murya yace " haka ne ni amma daga baya nai tunanin rashin d'aukan abin da zafi hakan ne yasa na yafemai."

   Jalal ya d'aga kai tare da had'e fuska yace " amma sai naji kamar wanda akace yayi fyad'en shi kuma yace sharri aka mai"

  Abdul ya zazzaro idanuwa cikin tsananin tsoro yace " me kake nufi da kalamanka?"
 Jalal yai murmushi yace " ni d'an jarida ne ba lawyer ba bincike ba nawa bane sai dai a labarin da mukaji Kamar fyad'an ba shine yai ba sharri akamai,  zai iya yiwuwa wanda ya mata sharrin ko bayasan auranka da ita yarinyar ne ko kuma santa yake, ko kuma......"

  Jalal yai d'an karamin hucci yace " nayi mamaii a binciken ku da bakuyi bincike ba cikin wannan al'amarin."

  Abdul ya mik'e a zuciye yace " me kake nufi? Wani nakusa dani ne dan bayasan na aureta ya mata fyad'e ko kuwa so kake ma kace ni na mata gaba d'aya , gayyatata kukai d'an ku wulakantani ko me? a iya sanina Fatima ta rasu, to waye zai ce nine na......."

    Murmushin da Jalal ya sakar masa ne yasa yai saurin rufe bakinsa sam yamanga abin live ne, Jalal ya rike baki irin abin mamakin nan yace " badai kaine ka.....ahhh nasan haka bazai faru ba da kaije da tuni ka nemi 'yarka tunda ance har haihuwa tayi sannan da ka sanar damu 'ya'yanka 4 nasan ba kaibane to amma ban fah........"

  Abdul ya fusata a zuciye ya d'aga hannu zai wankama Jalal mari, murmushi Jalal ya masa sannan yace " karka bari mutane su fahimci b'oyayen halinka da kake kokarin b'oyewa."

   Cikin tsananin takaici da bakin ciki Abdul ya fita.


  Jalal ya kalli Camera yace " muna sa ran kuto zatai kokari wajen gano mana gaskiyar wannan al'amarin kar muzu mu zab'i shugaban da ake kokwanto a kansa Bissalam."

  Abdul ya fita a zuciye sai dai me? Yana fita zai shiga mota yaga mutane dayawa da ragowar 'yan gidan wasu tv d'in da gidan radio suna juranshi.

   Jikinsa ne ya shiga rawa ya kasa tunanin komai...

  Seemah kam da gudu ta mik'e tabar falon.






ยฉ *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

2 comments: