JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ
Na *AYUSHER MUHD*
ayushermohd.blogspot.com
No.6⃣9⃣
Jalal ya fito daga fadar mai martaba gunsu Ammar ya nufa, Ammar na ganinsa ya taho da sauri, hannunsa ya rik'e yace " Jalal menene?"
Jalal yai murmushi yace " ba wani abun, kawai dai I am gambling with my life ne, I don't trust him sannan banida solution a wannan lokacin daya wuce in yarda dashi."
Ammar yace " Jalal akan Abdul ne?"
Jalal ya jinjina kai sannan yace " turowa sukai amin hukuncin da bazan iya sake magana ba, sai dai bazan iya ba."
Ammar yai shiru, Jalal ya dafashi yace " karka damu Ammar dolene musa mutumin nan ya biya laifin daya aikata tun a duniya, inba haka ba banaji Seemah zatayi rayuwar farinciki har abada."
Ammar kallanshi kawai yake, Jalal yai murmushi kamanta alkawarin dana maka ne? Na cewar kafin bikinka sai na sa Abdul ya tsugunna agaban Seemah ya nemi yafiyar abinda yai."
Ammar yace " amma Jalal......."
Jalal ya katseshi da cewa " ba abinda zasu iyamin nasan bazaka bari wani abu ya sameni ba."
Ammar ya makamai hararra yace " in wani abun ya sameka banaji zan iya yafema kaina."
Jalal yai murmushi tare da cewa "bama abinda zai faru."
Waya Jalal ya fito a ita ya kira Umma, ringing 2 ta daga cikin farinciki tace " Jalal kai nake nema ai tun dazu ai, albishirinka."
Jalal yace " goro."
Tace " Jalal jiya da daddare anma Zahida aiki yanzu ta fara magana a hankali."
Jalal cikin tsananin farin ciki yace " Da gaske? Yanzu Zahii tana magana?"
Umma tai dariya tace " dazun nan likita yasata ta fara gwadawa."
Jalal ya shiga cewa " Alhamdulila."
Umma tai murmushi tace " Sai dai muna bukatar abubuwa na amfani ga mahaifinka bayannan."
Jalal yace " bakomai zan turo a kawo muku ."
" toh Jalal Allah yamaka albarka."
Yace Amin.
Yana kashe wayar ya kalli Ammar cikin tsananin farinciki yace " Ammar Zahii tafara magana."
Murmushi sosai Ammar yai yace " Naji dadi sosai, Allah ya kara mata lafiya."
Jalal yace Ameen sannan ya furzar da wata iska yace "Yarinyar nan tun tana karama akace za'a mata aiki mai tsananin cin kudi, duk yanda Abba yaso ya tara kudin amma inaaa, ko kwatan kwata bamu isa hadawa ba, haka muna ji muna gani take a kwance ga kudi suka cigaba da karuwa."
Yai ajiyar zuciya, Ammar yai murmushi yace " Allah ya riga ya kaddara sai a wannan lokacin zata samu lafiya, amma naji kana maganar sako ya za'ayi?"
Jalal yace " shine ai, tana wani babban asibiti ne a kaduna na Dr Bilal to yanzu ga abinda ya faru."
Ammar yace " bakomai ni sai inje da kaina."
Jalal ya kalleshi yace " anya kuwa? Da so nakeyi ka nemo mana manyan 'yan jarida wadanda kasan masu amana ne ko ta hanyar su Dad ne, akwai abinda nakesan a dauka bayan Abdul yazo, sannan inasan a inda za'a kulleni a sa camera yanda zata dinga daukan komai dazai faru tsakanina dashi inyazo."
Ammar ya jinjina kai yace " Amma Jalal daukan evidence ba tare da mutum ya sani ba, ba illegal bane?"
Jalal yai dariya yace " a'a a law ai in har wanda ya dauki rahotan, dashi a cikin video din yazama legal, ai abinda ba'aso shine daukan shaida a boye ba tare da sun sani ba su dukansu "
Ammar ya jinjina kai yace " hmmm na gane yanzu."
Jalal yai murmushi yace " Zaid fa?"
Ammar yai tsaki yace " ya fita daga ganin wata yarinya ta fito daga gidan ya bita."
Jalal ya girgiza kai yace " Kaiii Zaid sai a hankali."
Jalal yacigaba" Ammar dan Allah ka taimaka kahe gida ka fadama Zainab nace ta koma gidansu, in komai ya kammala zanzo in daukota."
Ammar yace " gwara kam, zamanta ita kadai shima matsala ne bamusan me wannam mutumin zai yi ba."
Nan suka zauna Jalal a dinga fadama Ammar plan din yanda abin zai kasance, Kwarai Ammar ya gamsu, fatansu dai daya kar Sarki yaci amanarsu.
Nan Jalal ya koma ciki, shiru Ammar yai yana tunani baima san Zaid yazo kusa dashi ba, Zaid ya tabashi yace " Ammar me kake tunani?"
Ammar ya kalli Zaid yace " Zaid me kake tunani akan sadaukar da komai da Jalal yai dan ganin yaba Seemah farinciki?"
Zaid yai dariya sosai yace " Tsananin san da yake mata ne."
Ammar yai shiru can yace " tare muka taso da Seemah shekararmu Ashirin tare, shiyasa nake jinta a kowace gaba ta jikina amma ina mamakin ya za'ayi Jalal daya hadu da Seemah kwata kwata na wata daya yake neman sadaukar da rayuwarsa saboda ita?"
Zaid ma yazauna tare da cewa " nikaina ina mamakin wannan soyayyar, sai dai ita soyayya nasan a ganin farko ma take shiga zuciya, sai dai irin wannan soyayya ce ban sani ba."
Ammar yai shiru, a ransa yanata maimaita Shekara 20, da wata 1.
Can ya daure yace " Zaid me kake gani a naka tunanin? Dani da Jalal waye yafisan Seemah?"
Zaid ya kwashe da dariya yace " ina zan sani? Inba zuciyarku aka tsaga na duba ba?sai dai nasan dukanku kuna santa kuma dole dayane zai aureta."
Yanakainan ya mike yai hanyar waje, Ammar yai shiru yana tunanin da ni kaina ban sani ba.
Jalal kam agabanshi Sarki ya kira Abdul bayan sun gaisa ne yace " Senate na kama yaran kamar yanda kuka ce amma me za'amai?"
Senate yace " ni kawai ayi yanda za'ayi yabar kasarnan ko a turashi niger."
Sarki ya kalli Jalal wanda wayar a handsfree take kuma suna recording sarki yace " Amma yaran nada taurin kai fa, dan da alama akwai shaidu daya tara akanka ina tsoron kar ya yad'asu a kafafen yad'a labarai ba tare da mun sani ba."
Gaban Abdul me ya fadi yace " Wannan wani irin jarababben yaro ne? Me yake so danine?"
Sarki ya kalli Jalal sannam yace " nidai bansani ba amma yace tabbas in gobe bakazo ba yasa abokinsa ya kai shaidun kuto da kuma gidan tv."
Abdul ya mike yace " what? Nashiga uku wannan wani irjn jarababe ne? Ko kudi zan bashi mai uban yawa?"
Sarki yace " nidai bansani ba sakonshi dai daya ne tabbas gobe kazo ko kuma kaga takarda."
Abdul yai shiru can ya kalli PA jikinsa sai rawa yake yace " naji zanzo gobe dan Allah karka barshi yai abinda bai kamata ba."
Sarki yace " to shikenan."
Nan sukai sallama Sarki ya kalli Jalal yace " yaro wai baka tsoro?"
Jalal yai shiru can yace " ko inajin tsoro ai tunda na fara ban isa ingudu ba ballema banaji, ni yanzu taimakon da zakamin shine kataimaka kasa 'yan sanda suzo gobe dan nasan inhar ba mutum mai matsayi irinku bame bazasu zo ba."
Sarki yace " insunzo kana tunanin akwai abinda zasu iya yima Senate guda?"
Jalal yai murmushi yace " nima babban burina shine karsuyi komai din kamar yanda suka saba."
Sarki yace " Jalal u are really smart ko ni bana fahimtar komai da kake nufi sai dai kar ka bari smartness dinka ya lalata ma rayuwa."
Jalal ya kurawa wani gun ido baice komai ba.
Shidai abu guda daya yasani kuma yasa a ransa, dolene Abdul yaba Seemah hakuri sannan yaba mahaifinsa da Dad hakurin abinda ya musu, sannan in anzo bikin Seemah ace mahaifinta ya hallarta, ya sani ko bata fadaba dole ne kasan zuciyarta zaiyi radadin wannan al'amarin, ko bata nuna ba zataso ko da mahaifinta mutumin banza ne ace a tarihin rayuwarta ace mahaifinta dai ya hallarci bikinta.
Hawaye ne yaji yana neman zubomai, da sauri ya mike tsaye, Sarki ya bishi da kallo, ba shakka irin wadannan mutanen kasarmu take nema, sai dai a wannan lokacin bayaji akwai namijin da zai sadaukar da rayuwarsa saboda hukunta wanda yafi karfin hukuma.
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
��♀
Thanks Ayusher, we are really appreciating you...keep it up, Allah ya kara taimakawa.
ReplyDeletetanks a lot we appreciate ur effort
ReplyDelete. but don Allah a rika yo post mai yawa