*JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*
Na *AYUSHER MUHD*
ayushermohd.blogspot.com
No. 6⃣8⃣
Kallan kayan yai gaba daya ma kayan sun tsufa kamar irin kayan bulan nan, yabi kwanukan Umma da kallo idanunsa ne suka ciciko, yanaji tun kayan auranta ne a gidan, sai yan kwanukan da aka dinga siya a hankali daga baya in an dan samu wani abun, Ammar ne ya matso ya dafa kafadar sa, jiki a sanyaye Jalal ya juya ya kalleshi, Ammar yace " Jalal me kake tunani?"
Jalal ya kalleshi sannan ya kalli kayan, yace " Ammar duba kagani, me nakeyi har kayan mahaifiyata suka kona haka? Kalli kwanukan da kayan sawarta?"
Hawaye ne suka gangaro ta ta gefen idansa yasa hannu ya goge, Ammar ya kalli kayan shima jiki a sanyaye, sannan yace " me kakeyi kamar ya? Jalal in baka da halin canza musu satowa zakayi ko me? Kayi iya naka kokarin suma sun sani Allah ma ya shaida, kudi kake dashi a lokacin ko me?"
Jalal ya runtse ido ganin kayan Abba ma duk sun kod'e yace " Amma Ammar ban nemi kudi bane a da sosai, ai da zan iya....."
Ammar ya jijiga mai kai, yace " Jalal don't make ur life hard, na sani duk dabansan yakai rayuwa ba da nasan da kanada hali bazakabar iyayenka haka ba, sai dai yanzu da ka samu aikin dayafi waccan nesa ba kusa ba sai kayi kokarin cika burin dake ranka."
Jalal yai shiru yana kallan Ammar, Ammar ya sakeshi tare da cewa " me kakeyi a tsaye? Munfara gyara gun ko?"
Murmushi ne ya bayyana a fuskar Jalal, nan ya sukunya suka fara kwashewa, Zaid dake waje yana waya ne yashigo da sauri yace " Jalal wasu mutane ne sunzo wai hakimi ya aiko ana kiranka."
Jalal yace " ni kuma? Dama akwai wani hakimi a nan garin?"
Zaid yace " to nidai gasu can a waje."
Ammar ya kalleshi yace " muje mu duba mana."
Zainab dake tsaye ta window tana kallansu, ta sulale ta zauna a jikin bango, hawaye suka zubo mata a fili tace " Allah na rokeka Allah kasa ba wani abun Ya Jalal yai ba."
Jalal na fita ya kallesu kayan fadawa ne a jikinsu, ya mika musu hannu suka gaisa, sukace " a cikin ku wanene Jalaludeen?an isar mana da sakon ya iso garin nan yanzu."
Jalal ya kallesu yace " nine, menene?"
Suka kalleshi dayan yace " Hakimi ne ke nemanka zakuje gurin sarkin birnin gwari tare."
Jalal yace " ban gane zamuje gun sarki tare ba a wani dalilin kenan?"
Suka hade rai dayan yace " kai dan gidan talakawa in an baka umarnin abinda zakace kawai shine to bawai ka dinga tambayar wanu abu daban ba."
Jalal zai yi magana Ammar ya katseshi yace " bakomai muje."
Jalal ya kalli Ammar fuska a hade, Ammar ya ja hannunsa gefe, bayan sun dan matsa ne ya kalli Jalal yace " Jalal calm down, muje sai muji me zasuce ai basu isadai su hukuntaka ba akan abinda bana gaskiya ba."
Jalal yai tsaki yace " ni rainin hankali ne banaso, me ya damen da wani sarki dazasuzo su sani a gaba?"
Yai shiru can yace " muje."
Ammar ya danyi murmushi.
Sunje gun hakkimi aka wuce dasu gidan sarki, Zaid ya kalli Ammar yace " amma dai ba hukuntamu za'ai bako?"
Ammar ya fizge hannunsa yace " kayi wani abun hukunci ne ko kuwa?"
Sunje shiga fadar hakkimi ya kalli Jalal yace " wadannan su tsaya a waje."
Ammar yace " ban gane ba?"
Jalal yamai murmushi yace " nima banasan mu shiga tare, at least in laifi nai I won't drag you down. "
Ammar zai sake magana, Jalal ya kalli Hakimin yace " muje."
Nan aka musu iso suka shiga, Sarki na zagaye da fadawa, sai dai bayan sun zauna yamusu umarni su fita,nan suka fita dukansu akabar Jalal da Sarki sai hakkimi.
Sarki ya kalli Jalal yace " kaine Jalal?"
"Nine Jalal." Yafada tare da kallansa.
Sarkin ya dan gyara nadin rawanin daya kusa rufemai baki ya kalli Jalal yace " an turo sunan ka daga sama ance kayi babban laifi na wulakanta Senate dakai shine aka bani umarnin hukuntaka ba tare da hukuma ta sani ba."
Jalal ya kalleshi yace " in kace Sama kana nufin....."
Kai sarki ya daga mai, Jalal yai wata dariya yace " lalai mutanen nan basa tsoron Allah." Ya kalli Sarkin yace " I don't think kanada shirin hukuntani."
Sarki ya kalleshi yace " meyasa kace haka?"
Jalal yai murmushi yace " in har hukuntani kakesan yi bana tunanin zaka aiko a kirani kuma har ka sanar dani ai aiko a hukuntani."
Hakimi ya kalleshi yace " kai gyara yanayin kalamanka ko ka manta a gaban Sarki kake?"
Sarki ya kalli Jalal yace " indeed u are smart, ba hukuntaka zan farayiba harsai naji abinda ya faru a kasata shekara Ashirin din daka fada a jarida ko gaskiya ne."
Jalal ya kalleshi cikin rashin tsoro da sadaukarwa yace " zan iya fadama amma sai in har na tabbatar zaka taimakeni gurin bada hukunci ga wanda yai lefi duk matsayinsa kuwa."
Sarki yai shiru can yace " idan kuma na kasa yin hukuncin fa? Ko kuma sai ka gama sanar dani incanza shawarata?"
Jalal ya kalleshi tare dayin ajiyar zuciya yace " Ka sa a kulleni kamar yanda aka fadama."
Sarki ya kalli Jalal da mamaki yace " kamar ya?"
Jalal yai murmushi yace " haka nake nufu kasa a kulleni sannan ka sanar da wanda ya ya bugoma wayar ina da evidence akan laifin da Senate Abdul ya aikata, sannan in har baizo gobe ba na ba Abokina zai aika kuto."
Sarki ya kalli Jalal cikin tsananin mamakin kalamansa yace " Jalal ban fahimceka ba."
Jalal yai murmushi yace " kai ma mutum ne mai matsayi sannan akwai mutane dayawa da suke samanka kamar Senate Abdul, bazan iya sanar dakai komai ba tukunna, in ka amince da olan dina to in kuma ba haka ba shikenan sai in tashi in tafi."
Shiru sarki yai na wasu 'yan dakiku yace " Don't trust me, dan bansan me kake shirin yi ba, kar inje daga baya inga bazan iya ba inyi betraying dinka, daga baya kazo kace ban fadama ba."
Jalal yai murmushi yace " I don't trust you, sai dai daga sanda kace fadawanka su fita nasan at least kai ba kamar su bane hakan na nuna bakasan aji maganar da zamuyi."
Sarki ya jinjina kai yace " okay na aminta da shawarar ka sai dai baka tsoron Abdul?"
Jalal yace " inada 'yan uwa a waje tare mukazo dasu ba kuma na tunanin zasu bari wani abu ya sameni."
Sarki yace " shikenan zan kulleka kamar yanda ka bukata, zan kuma yi abinda kace in har baifi karfina ba sai dai inaso ka fadamin kalma daya, da gaske Abdul ne yai fyaden dayaja matsaloli da dama a shekarun baya?"
Jalal ya dago yace " Zan iya rantsuwa akan shine yai wannan fyaden."
Sarki yace " Na aminta dakai, ka birgeni sosai na dade banga wanda ya zauna dani yai magana kanshi tsaye ba haka kamar kai, ba ka tsoron in an gama in ma hukunci?"
Jalal yai kasa dakai yace " In har na gama abinda nakeson yi ba wani abu bane in ka hukuntani."
Hakimi kam ya zama kurma dan ya kasa sa baki a wannan al'amarin shikam sam bai fahimci me suke nufi ba shiyasa ma yai shiru kawai.
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
♀
More grease to your elbow, more ink to your pen, more ideas to your mind and more initiative to your brain...
ReplyDeleteThanks alot
ReplyDelete