Wednesday, 17 May 2017

ZUCIYA....kowa da irin tasa 23

*ZUCIYA*
       _ĸowa da ιrιn тaѕa_

© *na Ayυѕнer Mυнd*
    ayushermohd.blogspot.com

*Fatie Shafi'u ina tayaki murnar kammala Jarabawarki. May Almighty Allah help and protect u.... ILYSM*

    Washe gari da safe Habib yaje makarantar mahaifinsa yama Nafi takardun karya na primary da kuma Js 1 and 2, sai dai takardun sun nuna sam batada kokari.

   Nan ya taho da shi gidansu Ashraf.

   Yau gidan an tashi kowa zuciyarsa ba dadi musamman ma Umma da Aneesa, Little kam ta fita makaranta.

Itakam Nafi tana kitchen ta zake sai aikin girki take,  sunayi suna 'yar hirarsu da Goggo.
  Suna gamawa ta fito duk jikinta ya d'an baci Amra ce ta karaso gunta da gudu tace " Wai kizo inji yaya. "

  Nafi ta kalleta cikin zak'uwa tace " Ya Ashraf?  " kai Amra ta d'aga mata ai kam Nafi da sauri ta nufi b'angarensa tana tafe tana gogee fuskarta da hannu,  tun jiya takesan ganinshi sai dai ba yanda zatai.

   Fuskarta a sake ta kwankwasa kofar, ta saba in yana ciki sai dai yace ta shigo in dai har ba makulli yasa ba,  sai dai yau gani tai anzo an bud'e da fara'arta ta kalli mai bud'ewa tace " Yaya ina kwa...... "kalamanta ne suka tsaya ganin Habib a tsaye yana mata murmushi.

  Jin ta tsaya da magana yad'an kanne ido cikin salonsa yace " Haba Nafi ba ni kika so gani bane? "

  Da sauri ta girgiza kai alamar a'a sannan ta d'ora da cewa " ba haka bane Ya Habib. "

  Habib ya d'an matso kad'an hakan yasa ta d'an kara matsawa,  kara matsowa yai itama ta kara matsawa,  sam bata kula tazo karshe ba tayi baya zata matsa kawai taji zata fad'i,  da sauri yasa hannu a kugunta ya tarota.

   Nafi kam har ta runtse idanta kam,  jin an riketa yasa ta bud'e ido a hankali,  Habib ya sakar mata wani lalausan murmushi,  sannan ya matso da fuskarsa yace " Me yasa kika tsaya da maganar ki to? "

  Yawu ta had'iya da karfi sannan ta d'an motsa baki tace " Ya Habib d'an sakeni. "

  Jin ta waske bata bashi amsa ba yasa ya d'agota tare da sake cewa " Shikenan na hakura da gaisu.... "
Bata jira ya karasa ba tace ina kwana? "

  Dariya ya d'anyi sannan yace " Nafi kina burgeni na rasa me yasa. "

  Kasa tai da kai dan itakam tasan wasa ne ace tana burge wani.

  Ashraf dake zaune a kujera duk yana kallan me sukeyi kasancewar kofar a bud'e Habib ya bata yaja wani karamin tsaki tare da girgiza kai yace " in kun gama sai ku shigo,  dan ni inada abinyi. "

  Nafi ta kalli inda Ashraf yake haka kawai taji gabanta ya fad'i tare da tsananin takaicin ganin ta dayai.

Habib ya matso da niyyar rike mata hannu da sauri ta b'oye hannun a baya kallanta yai fuska a sake sannan ya d'anyi gaba yace " Ki shigo. "

  Da sauri ta shige jikinta duk yai sanyi.

  Ashraf na zaune yana kallo ta karasa tare da zama a kasa,  Habib ya kalleta yace " zauna a kan kujera mana? "

  Ashraf ya bugamai wani mugun kallo yace " Mu sa'aninta ne? Kai meyasa kake kokarin zubar mana da mutunci agurin yara kanana? "

  Nafi wacce ko alamar tashi dama batai ba ta d'ago ta kalleshi sai dai zuciyarta ta d'anji ba dadi.

  Ashraf ya d'auke idansa,  Habib ma kasa magana yai,  Shiru ne ya d'an biyo baya kafin Ashraf yace " Nafisa! "

  Gaba d'aya tun daga kan yatsar kafarta har zuwa kanta sai dataji wani abu ya wuce mata, d'agowa tai a hankali ta kalleshi.

Ashraf kam ko a jikinsa yace " yau zuwa gobe zakuje da Little da kuma mumy xakuje siyayyar kayan makarantarki. "

  Kallonsa tai cikin mamaki batasan sanda tace " naam? "

Ya had'e fuska sosai yace " bakiji me nace ba? "

  Tace " Naji kace makaranta. "

Yace " eh,  in kun gama siyayya da komai zuwa jibi zaki wuce makarantar kwana dake kazaure. "

  Nafi kam idanunta ne suka ciciko,  wani irin farin ciki ne wanda ita kanta batasan irinshi ba yake ratsata,  Ashraf yace " meye hakan? "

  Hawayenta ta goge wanda suka zubo,  ta girgiza kai tace ba komai.

Habib cikin damuwa yace " Bakyaso ne? "

Kai ta girgiza da sauri tace "a'a ba haka bane. "

  Ashraf ya d'an kuraa mata ido kamar yanasan gano wani abun,  idanunta tai saurin yin kasa dasu tace a hankali tace " Yaya babana fa?"
  Jiyai ransa ya b'aci ya ce " Bansan inda yake ba,  kuma bana fata insani, sannan in har da haka kike tunanin yin karatun to gwarama karkije,  dan ni na tsani mutum mai raunanniyar zuciya. " ya mike yai ciki.

  Kallo ta bishi dashi zuciyarta tana dana sanin tambayar datai,  sai dai duk yanda taso da daurewa ai dole ne tai rashin mahaifinta.
A ranta ta maimaita Raunanniyar Zuciya? Me kenan?

Kamar Habib yasan meke ranta yace " karki damu da fadan Ashraf dan shi yawancin maganarsa haka take. "

  Nafi tabi d'akinsa da kallo tanasan ta bashi hakuri ta kuma tambayeshi ciwon sa,  daurewa tai ta kalli Habib tace " Ya Habib meye raunanniyar zuciya? Ma dai san me zuciya take nufi"

  Dariya yai yace " rauni fa? "
Tace " na sani. "

Ya sake dariya yace " to sai ki had'asu guri d'aya ki gani. "

Tace " Rauni Zuciya? "
  Wannan karan dariya sosai Habib yai yace " lalai Nafi inkinje makaranta cikin mutane a hankali zaki fahimta. "

  Tace to,  sannan ta sake kallan d'akin Ashraf sai dai ba yanda zatai, mikewa tai zata fita,  Habib yace " aiki kikai ne?  Naga kayanyi sun b'aci kamar daga kitchen kika fito. "

  A'a kawai tace tai saurin fita.

Tana gaba kad'an sai ga Aneesa wacce tasha kwalliya tana tafe kamar sarauniya.
Idanunsu ne suka had'u,  gaban Nafi ne ya fad'i bawai dan tsoro ba a'a sai dan ganin kyan datai,  a cikin zuciyarta tace " Dole Ya Ashraf yasoki. "

   Tun datazo gidan bata taba ganin Aneesa ta d'au kwalliya irin haka ba,  ba namiji ba ko mace ce ta wuce dole ne ta kalleta dan tayi kyau sosai,  Aneesa wacce takura ma Nafi ido cikin tsananin takaici ta karaso.

  Kwalliya tai dan taje su shirya da Ashraf amma me take gani haka?
A zuciye ta karaso tare da kallan Nafi cikin tsananin takaici tace me kike anan? "

  Nafi ta kalleta sai dai ta kasa cewa komai,  Aneesa ta sake kuluwa tace " ke dan gidan ku ba magana nake miki ba? "

  Nafi ta daure kawai jitai ta sami kanta da cewa" Ya Habib ne ya kirani. "

  Aneesa wacce bata gamsu da zancen ba tace " Nafi karkiga jiya nazo da niyyar dukanki ki d'auka wai ko kishi nake dake ko wani abun. "

  Ta d'anyi dariyar kissa tace " Tausayi kike bani,  kinfi kowa sanin ni dake ba d'aya bane sannan ke da kanki zaki iya warewa kisan wa ya dace da Ashraf ko ince wa Ashraf yake so,  dan haka ina baki shawara in ma da wani shirme ko yarinta akanki gwara tun wuri ki cireta dan kinsan wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa, ke ko masu aikin gidan nan sun fiki daraja. "

Ta bangaje ta tai gaba,  jitai ranta yayi sanyi ta tuno maganar Umma datace " ki nuna mata ita ba komai bace ta hakan ne inma da wani munafircin a ranta zai sa ta shiga hankalinta."juyowa tai ta kalli Nafi tana nan a inda ta barta, ta sake dariya sannan tai gaba.

  Nafi kam sai juya kalamun take a ranta,  tafi kowa sanin Ashraf yafi karfinta,  ta kuma sani ko kata sun kare ba abinda zaiyi da ita sai dai meyasa takejin zuciyarta ba dadi? Wata zuciyar tace kema Nafi kina ganin mai mace kamar Aneesa me zaiyi dake? Jiki duk a rame?  Gaki yar kauye wacce ake neman biyan bashi da ita? "


   Da kyar ta karasa d'aki tai wanka sannan tasa abinci a gaba, da kyar takeci ta rasa me yasa batajin dadin abincin sam.

    Aneesa kam tana shiga taga Habib zaune a kan dinning yana cin abinci,  tai murmushi tace " Yaushe a gari d'an uwan Ango? "

  Habib ya kalleta yace " Amarya irin wannan kwalliyar kamar yauce ranar? Ko dai anzo seducing d'in d'an uwa nane? "

  Aneesa ta d'anyi dariya har hakoranta suka fito ta d'an karkace kadan tace " me?  Kana tsoro ne?  Ko kuwa kishi kake ba kada me ma?"

  Habib ya rike haba yace " tab lalai d'an uwana yana cikin tashin hankali gwara muyi sauri mu kawoki kafin ki burkice mana d'an uwa."

  Aneesa ta d'an fara tafiya cikin salo tare da cewa " ah to wayace kukai bikin da nisa?"

  Habib ya bita da kallo yana murmushi.

  D'akin Ashraf ta murd'a,  kai tsaye ta shiga, Ashraf wanda ke kokarin shiga wanka ya kalli kofar kansa tsaye ya d'auka ko Habib ne, ganin Aneesa yasa ya had'e fuska tamau,  ta sakar nai wani murmushi tace " Sorry Hubby ashe wanka zakai. "

  Ya kalleta yace " Aneesa bakisan ya ake sallama ba ko kwankwasa kofa ba? "

  Ta shagwab'e tare da shiga ta zauna a bakin gado tace " nida d'akin mijina? "

  Ya girgiza kai cikin takaici yai hanyar toilet sannan ya tsaya ya kalleta tare da cewa " nine mijin kuma banaji na bada sadaki bare a shafa fatiha,  dan haka ki kiyaye shigomin d'aki kai tsaye." yana kainan ya shige toilet.

  Aneesa ta turo baki cikin jin haushi sai dai ta kasa cewa komai sannan tana kunyar fita kar Habib ya mata dariya......





  *THE INNOCENT TEAM*

No comments:

Post a Comment