*JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*
Na *AYUSHER MUHD*
ayushermohd.blogspot.com
No. 5⃣8⃣
Sagir na dawowa daga raka Jalal mai gadi ya mikamai wata takarda, kallan sa yai yace " nameye?"
Mai gadin yace "d'azu da zaku fita wanda kuke tare ya bani yace in kun dawo in baka."
Sagir ya amsa yana mamakin takardar miye acikin envelope?
Yana shiga d'aki ya fito da farar takarda, abinda idanunsa suka fara gani nai ya kad'ashi, letter of resignation an yi rubutun da manyan harufa ankuma ja layi, wasik'ar barin aiki?
Hannu yasa a aljihu ya kira Jalal, Jalal kam sun d'au hanya ya d'aga wayar, Sagir yace " Jalal me nake gani haka? Ban gane wasik'ar barin aiki ba?"
Jalal yai shiru, Sagir yace " Jalal menene hakan?"
Numfashi yad'an ja kad'an sannan yace " Please kamin submitting d'in takardar, bazan iya zuwa dakaina bane."
Cikin rashin fahimta Sagir yace " aiki ka samu? Ko me?"
" ba wani aiki akwai babban dalilin dabazai sani na cigaba da aiki a company d'in ba."
Sagir ransa ya b'aci yace "saboda soyayya zaka hallaka rayuwarka ko me? Jalal wai me yasa kek neman barin soyayya ta rufema ido?"
Jalal ya d'anyi murmushi inama ace soyayyarce kawai ba wannan babban al'amarin bane? Ya daure yace " Sagir kenan."
Haushi ya kama Sagir ya kashe wayar tare da jefata kan gado, shikam yana mamaki ace wai mutum yabari soyayya ta nemi hargitsamai rayuwa?
Zahra ce ke ta shiga d'akuna tana kaima mutane abincin safe, ta taho da flask d'in abincinsu Junaid tai d'akin, takalman dake bakim kofa ta kalla, takalmin Zaid ne kawai hakan yasa tai sallama tare da tsayawa a kofar d'akin, Junaid dake kwance ya amsa a kasalance, zuciya d'aya ta shiga tana cewa " kai dai ya Zaid kaji jiki ace kowa ya tashi amma kanannan akwance kamar ba namiji ba."
Junaid jin maganarta yasa ya fara murmushi tare da kara shiga bargo, ta matso cikin tsokana tafara jan bargon daya rufu dashi, Junaid ya zaro ido tare da kallan kayan jikinsa, vest ce sai gajeran wando, da sauri shima ya ja bargon nan suka fara jaye_jaye, tana ja tana cewa " Allah yau sai ka tashi kai ko kunya bakaji Yaya?"
Junaid ya kara jan bargo, hannu ta hard'e tare da sa kafarta a kan gado ta kamo bargon da karfinta, ai kam ta fizgo bargon, Kallan mamaki tama Junaid tare da bud'e baki cikin mamaki, Junaid ya fizgo bargon da karfi, itakuma gaba d'aya nauyinta nakan bargon, ai kuwa tabi bargon ta fad'a jikinsa, Ta d'ago ta kalleshi cikin mamaki murmushi ya mata na karfin hali dan shima kunya yaji, yace " Zahra kece?"
Mik'ewa tai da sauri tare da juyawa tai waje da gudu, Junaid ya bita da kallo fuskarsa na wani irin murmushi, Zahra d'aki ta fad'a da gudu tare da sama d'akin makulli ta matso kusa da Seemah dake zaune rik'e da agoggon Jalal, Zahra ta fado kusa da Seemah kamar mai shirin kuka tace " Seemah an kashe ni?"
Seemah ta kalleta tace " an kashe ki kamar ya?"
Zahra ta mik'e ta fad'a gado tai rufda ciki tare da rufe fuska tace " Seemah naga Ya Junaid da vest."
Tana fad'a tare da tura kanta jikin katifa, dariya Seemah ta kyalkyale dashi wanda rabon datai dariya haka harta manta, dariya sosai tai sai data tsagaita tace " Haba? Kuramai ido kikai?"
Zahra ta bubuga kanta tace " Eh mana?"tafad'a kamar mai kuka.
Seemah ta kara sa dariya tace " lalai Zahra wato ba kunya? Kika kuramai ido?"
Zahra ta mik'e zaune tace " wayyo wlh ba da sanina bane nifa bansan shi bane."
Seemah ta guntse dariyarta tace " kyama fad'i gaskiya da alama ma dama haka kika so, yanzu Zahra ko kunya? Hmmm"
Zahra ta mik'e da sauri ta matso gun Seemah ta rik'e hannayenta tace " Seemah yazanyi? Shima zaiga kamar banda kunya ko? Nashina da wani idon zan kalleshi?"
Seemah ta kara guntse dariya tace " gaskiya kam wannan kam fitsira ce."
Zahra kula datai Seemah cinnata takeyi yasa ta kalli Seemah tace " tsaya! Shi yayan naki waya ce yaki fad'amin shine? Ai ni banida laifi."
Seemah tai dariya tace " ahhhh gaskiya ba laifin yaya na bane a dai duba."
Haka tai ta tsokanar Zahra.
Jalal kam har ya isa zuciyarsa ta rasa bashi mafitar alkawarin daya d'auka, yana isa gida yaga mutane a cike, shiga yai duk da ransa ba so yake ba, nan suka shiga gaisawa da jama'a wasu 'yan uwan Zainab ne wasu nashi, yana gama gaisawa ya wuce d'akinsa ya kwanta, Abba ne ya shigo d'akin ya tsaya a bakin kofa yace " Jalal?"
Jalal bai juyaba yace " Naam"
Abba yai shiru cikin sanyin jiki yace " kaga Abdullahin?"
Jalal yace " eh amma...."
Sai kuma yai shiru, Abba ya kalleshi yace " Jalal mutumin nan ba mutunci gareshi ba ka karfi na dukiya da mulki dayake dashi bana tunanin kanada hanyar dazaka sashi abinda baiyi niyya ba."
Jalal yai shiru, tabbas yasan haka abin yake, Abba ya cigaba " Kai ba Lawyer ba, ba kuma D'an jarida ba mai zaka iyayi? Bayan ko shari'a yafi karfinta?"
Da sauri Jalal ya mik'e ya yace "d'an jarida? Lawyer?"
Kallansa nai nima cikin mamaki mai yake nufi?
*HUSSYLURV, BILLY, AENART, AMAL, HADIJA, ZEE BALA, UMMU NAFISA, RAMBI. DAFATAN KUNYI WEEKEND LAFIYA.*
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
♀
Thanks
ReplyDeleteGracias....
ReplyDeleteSpecial thanks 2 u ayusher.
ReplyDelete