Sunday, 29 January 2017

JALALUDEEN 54


     *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*



Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 5⃣4⃣

   Jalal ya d'ago ya kalli Abba yace " Shugaban kasa ne shi ko me?"

Abba ya kalleshi yace "Jalal Sanate ne yanzu wanda kuma ake ji dashi haka kuma mutane na sanshi, ina tsorace maka abinda zai biyo baya."

   Wata muguwar dariya Jalal yai wacce sai da abin ya tsorata Abba, sannan ya tsagaita yace " mene? Sanate? Wasu mahaukatan ne suka zab'eshi? Kuma shi ko kunya mutumin dabai san darajar d'an Adam ba harya iya cigaba da siyasa?"

  Abba yai ajiyar zuciya yace " nidai yanzu kabar komai kaga gobe za'a kawo Zainab."
  Jalal ya kalli Abba shi harya manta da wani auren Zainab, ya juya kai batare dayace komai ba.

Ganin haka yasa hankalin Abba yad'an kwanta, mutane mak'ota ne suka fara zuwa halan yasa Jalal ya koma ciki, shiru yai yana tunani can ya d'auko wayarsa yafara duba senate na kasa, kan wani yazo *ABDULLAHI UMAR*
Ya kalli hoton mutumin dakyau gabansa ne ya fad'i ba shakka wannan shine mahaifin Seemah bawai kama sukai sosai ba sai dai in har ka kalleshi ka kalli Seemah zakasan akwai alak'a ta jini sannan ga tarihinsa daya karanta, ransa yakai k'oluluwar b'aci sanda yaga yanda ake ji dashi da kuma yanda mutane ke masifar sanshi wasu har so suke ya tsaya a matsayin shugaban kasa na zab'e ma gaba.
  Haushi ya ishi Jalal ya cilar da wayarsa kan gado sannan ya mik'e cikin zafin rai kawai wayarsa ya d'auka ya fita.

Tasha ya nufa kawai ya shiga motar abuja, sam idanunsa sun rufe.

   Dad da Abba da kuma kawo ne zaune a d'aki, Abba ya kalli kawu yace "Wani hukunci ka yanke?"
Dad yai saurin cewa " Kawu nidai dan Allah kadawo nan da zama me zakayi a suleja yanzu? Dama can ba garin mu bane."

  Kawu yai shiru cam yace " naji amma dai kai Isma'il kaima ina fatan kadawo nan da zama kenan?"
  Dad ya d'ago ya kalli Kawo sannam ya kalli Abba jikinsa yai sanyi, Abba yace " gaskiya kam ya kamata kaima ka dawo kazauna anan."

  Dad a hankali ya furta "karatun Seemah fa? Ina tunanin yimusu baiko itada Ammar sai in koma can inyaso in ta gama karatun sai mu dawo gaba d'aya."

  Abba yai shiru can kawu yace " naji bayananka sai dai nima na yanke nawa hukunci na."
  Ya kallesu sannan yace " In akai bakwai d'in marigayiya nakeso wahsegari ai baikon Junaid da Ammar, in yaso sai ka d'auki matarka ku koma England har zuwa sanda zata gama karatu, da zarar ta dawo za'a had'a ayi auren."

  Dad ya jinjina kai alamar gamsuwa sannan can ya kalli Abba sannan ya kalli Kawu yace " Amma junaid yanada budurwa ne?"
  Nan Abba ma ya kalli kawu da mamaki, Kawu yai murmushi yace " ba wani taro za'ai ba saboda rasuwar da akai mana kawai dai za'asa rana ne a kuma bada kud'in gaisuwa."
  Abba ya kalli Kawu yace " amma kawu......"
  Kawu yai murmushi yace "Mahaifiyarku babban burinta bai wuce tayi had'in aure a tsakanin 'ya'yan ku ba, tunda shi Ammar yanada Seemah shiyasa nake tunanin had'a auren Junaid da Zahra."

  Kallan juna Dad da Abba sukai, Kawu yace " na amince da auran Ammar da Seemah sai dai kamar yanda mahaifiyarku tace dole ne kafin ranar auren asan mahaifinta."

  Dad yai murmushi tare da cewa gaskiya ne naji dad'in had'in nan, Abba ma yai murmushi.

   

   Jalal sai bayan magrib ya iso Abuja, wayar Umma ce ta shigo sai alokacin ma yai tunanin ashe bai fad'a musu ba, da sauri ya d'aga wayar yace " Umma?" Tace " Jalal kana inane? Tun d'azu ana nemanka."
Jalal ya kalli cikin garin Abuja yace " Umma kiyi hakuri d'an Allah wani uzuri ne ya tasomin ina Abuja yanzu."

  Tace " Abuja kuma?gobe fa za'a kawo Amarya."
  Jalal ya runtse ido jin an anbaci Amarya yace " kiyi hakuri Umma."
Tace " naji amma ka tabbatar gobe ka dawo da wuri banasan mutane su fara zargin wani abun."
Yace "insha Allah." Nan suka kasje wayar.

  Yana sauka yai sallah sannan ya nemi d'an machine yace " kasan gidan Sanate Abdullahi?"
  D'an machine d'in ya kalli Jalal daga sama har kasa sannan yai dariya yace " kasan me kake cewa kuwa?"
Jalal ya had'e rai yace " mahaukaci ne ni dabazan san me nake cewa ba ko me?"
D'an machine yace " A'a muje inkaika." Aransa yace ko mai aiki ne a gidan?
  Sun isa wata had'ad'iyar unguwa manyan gidajen dake gun da kuma tsarinsu zai tabbatar maka da guri ne manyan mutane.
  A kofar wani had'ad'an dank'araren gida yai parking, Unguwar shiru kamar ba mutane, d'an machine ya juya yatafi bayan ya cemai nan ne gidan.

  Jalal yabi gidan da harara yace " Dama irinkune masu hana kasar mu cigaba, kun tara zunubai a kanku kuma kunzo d'an yaudarar mutane."

   Kofar Gate d'in ya karasa tare da tunanin ta inda zai fara, wani security ne ya fito tare da kallansa yace " me kake anan?"
  Jalal ya kalleshi yace " Gidan Sanate Abdullahi ne?"
  Mutumin ya kara had'e rai yace " eh amma kai waye?"
  Jalal ya d'an daure tare da sa hannu a aljihu yace " nemansa nakeyi."
  Security d'in ya jara kallansa yace "baka da hankali ne? "
Jalal yace " what?"
Nunashi da bindiga yai irin doguwar nan yace " waye kai?"
  Nan fa idanun Jalal sukai tsuru tsuru, husur security d'in ya hura nan da nan wasu securities d'in suka fito, ya kalli Jalal yace " a dubashi da kyau ban yarda da shiba."

  Jalal haka suka ririk'eshi suka shiga lalubamai jiki kamar yai ihu d'an bakin ciki, suna gamawa suka sakeshi tare da cewa " nothing suspicious Sir."
  Ya kalli Jalal yace " tashi ka kara mai karkuma insake ganinka anan."
  Jalal ya dake zuciyarsa yace " ganina kuwa dolene d'an bazan tafi ba harsai naga mutumin gidan nan inkuwa kuka hanani to sai dai ku fita da gawata."

  Mutumin ya kalli Jalal yai murmushi yace " I wish kayi karatun Soja da anyi jarumi."
  Jalal ya juya kai, mutumin ya cigaba sai dai inhar baka tafi ba zakuwa a fita da gawarka.

  Jalal ya kara dakewa tare da jingina da katangar gun, ran mutumin ya b'aci ya d'aga kasan bindiga zai bugama Jalal, sai sukaji karar horn, da sauri suka jeru aka bud'e gate, motoci uku ne suka shigo Jalal ya kalli motocin har sukai parking sannan wata yarinya ta fito daga motar sanye da riga da wando sun matseta, tana tafe tana jijiga kai alamar rawa, Jalal yaja karamin tsaki yace "Allah ya shirya."
Juyowa tai d'an taji alamun kamar ana kallanta caraf suka had'a ido da sauri Jalal ya d'auke idanunsa, d'an takaici aransa yace "yanzu wannan kanwar Seemah ce fa ko?"

  Baisan tazo kusa dashi ba sai jiya tace " waye wannan?"
Securitin ya kalli Jalal yace " Sorry madam."
Yanda take magana ma ya tabbatar ma Jalal ba'a hayyacinta take ba, ta nuna Jalal tace " Kai."
  Jalal ya kalleta tare da girgiza kai yarinya karama dabata wuce shekara 18 ba amma.......
  Zata sake magana taji daga saman beni ance "Me kikeyi anan?"
Da sauri Jalal ya d'aga kai, baban mutum ne da dukda baikai su Abba ba amma kasan baba ne, Jalal ya kara cusa ido ya kalleshi tabas mutumin da yake nema ne.
Dabara ce ta fad'o mai,
  Yarinyar zatai magana Jalal da karfi yace " Sannu Dad dama cewa tai inzo gunka akan maganar soyayyarmu."

  Securities suka kalleshi da mamaki itama ta juyo duk da a bige take ta nuna shi sannan ta nuna kanta, murmushin rainin hankali ya mata yace " Ko Sweety?"
  Kai ta d'aga sannan ta kalli Mahaifinta wanda ransa yai mugun b'aci yace ku shigo ciki.
Jalal yai wani murmushin rainin hankali sannam ya kalli Securities d'in yace " Sorry bansanar daku da wuri ba."

 


THE SEEMAH'S LOVE TEAM

Saturday, 28 January 2017

JALALUDEEN 53

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   _*This Page is Dedicated to you ��herty�� wish u ol the best in ur Exams..... Thanks once again*_

   No. 5⃣3⃣


     Jalal jikin bango ya jingina a sulale ya tsugunna hawaye ke malala a kuncinsa, Umma dake zaune itama tana kuka ta taso ta matso kusa dashi tace Jalal! Wani irin kara yayi da duk sai da suka tsorata kuka ya wuce da shi kamar wani karamin yaro, Umma tsoro ya fara kamata ta kalli Abba tace " Meyasa ka fad'amai? Yanzu in wani abu ya sameshi fa?"

   Abba ya kalleta cikin wani yanayi, yace " daga sanda Isma'il yazo gidan nan nasan ban isa in b'oye sirrin nan ba, da wani a waje ya fad'amai mahaifinsa yaci amanar Amininsa gwara ni dakaina insanar dashi. "

  _Nikaina Ayusher yanda naga Jalal na kuka sai da naji hawaye ya zubomin a hankali nayi waje d'an bazan iya zama ba._

  A b'angaren Seemah kuwa bayan mutane sun ragune Ammar ya shigo d'akin, ya kalleta a rak'ub'e a gefen gado, tausayinta ya kara kamashi ya matso inda take tare da d'agata, kallanshi tai kamar wacce hankalinta baya jikinta tace " Ya Ammar am d'aura ko?"

  Kallanta yai idanunsa suka ciciko, hannu yasa a kafad'arta yashiga jijigata yana cewa " Get hold of your Self Seemah, please. "

  Ya d'ad'e yana jijigata kafin ta kalleshi tace " Yaya ya zanyi?"
  Yace " Seemah England zamu koma ranar bakwai inajin shi kad'ai ne zai sa ki manta komai."
   Ta d'aga kai tace " na yarda Yaya ni kaina haushin kaina nakeji."

  Nan ya mike yai waje, bai dad'e ba sai gashi ya dawo rik'e da plate na abinci, Zama yai kusa da ita tare da d'ebo abinci a cokali da niyyar ba ta, ta kalleshi sannan ta amshi cokalin tace " Zanci da kaina Oppa."

  Murmushi ya mata sannan ya mik'a mata spoon d'in, ta fara ci, yace " Matar Dad tazo ta dubaki?"
  Ta d'an tab'e baki har zatai maganar rashin kunya ta tuna ashefa ta fita matsayi yanzu, tai kasa dakai tare da cewa " Ta l'eko d'azu."
  Ammar yai d'an karamin tsaki yace " bansan ya akai Dad ya aureta ba, sam batada kara."
  Seemah tai shiru can tace " Ka manta Yaya? It is all my fault, bakaji Dad nacewa saboda ni ya aureta ba? Na sani saboda yanaso akula da......."
  Kasa karasawa tai saboda hawaye, Ammar ya kallera yai murmushi yace " Oh yazanyi da wannan kanwar tawa mai saurin kuka?"

  Ta kalleshi tare da share hawayenta tace " Yaya?"

  Yad'an rangwab'ar dakai yace " Seemah rufe idonki."
  Ta kalleshi tad'an turo baki kad'an, sannan ta rufe, hannu yasa a aljihunsa, sannan yace "bud'e."
  Da sauri ta bud'e tanasan ganin menene, kwalin waya ya mika mata, ta kalli wayar Iphone 6 ce, tace " yaya inafa da waya?"

  Yace " Dad ne yace kar abaki waccan."

  Tai murmushi sannan ta amsa tace " Thanks Bro."
  Yai murmushi shima yace " Ahhh naji dad'i kinyi murmushi, sannan kinci abinci."

  Ta kalleshi tace " saboda Deen ne ba'asan abani d'ayar wayar?"
  Ammar ya kalleta bai amsa ba, ta kara murmushu tace " karkadamu yaya, yama za'ai in sake ganinshi? Sannan bazan bari effort d'inka ya tafi ba yanda kasa naji zuciyata tayi sanyi ba."

  Ammar kallanta kawai yake, ta kara sakar mai murmushi sannan ta hure mai ido tace " Yaya kallan fa?"

  Mik'ewa yai da sauri tare dasa hannu a aljihu duk ya rikice yace " Ehem dama dama fita zan d'anyi, nan zafi ko bakya ji?"

  Batasan sanda tasa dariya ba, tace " Zafi kuma yaya? Nan d'in?"

  Kallanta yai yace " Seemah just now dariya kikai ko? Badai hallucination na gani bako?"

   Tai kasa dakai tana murmushi tace "kai yaya kai d'in ne wai zafi."

  Kallan yanda take murmushi yasa ya farajin zafin na karuwa, da sauri yai waje, yana fita daga d'akin ya fara furzar da wata iska yanacewa " Cool down Ammar."

  Can kuma yace " meke damuna?"

  Junaid ne ya dafashi yace " Ammar agidan gaisuwar ba kunya kake soyayya?"

  Kallan Junaid yai a tsorace, Junaid yai murmushi yace " Ya Habib ya fad'amin komai karka damu."

  Ammar yai ajiyar zuciya sannan ya kuma kalleshi da mamaki yace " ban gane soyayya ba kuma?"
  Junaid yace " in ba soyayya ba me kake a d'akin?"
  Ammar ya kalleshi da mamaki yace " What? Seemah ce fa a d'akin."

  Junaid ya d'an jinjina kai yace "ai sanin Seeman ce yasa na fad'a, Ammar ka nutsu ka tambayi zuciyarka, wacce irin soyayya kake mata?" Junaid na kainan ya juya yai gaba yabar Ammar da binsa da kallo.

  


   Jalal kam bayan su Abba sun fita yana nan dai a gun da yake, ya dad'e agun kafin ya daina kukan, yafara cewa " ya zanyi Seemah?"

  Jin ba amsa yasa yai shiru can yace " Abdul?"
  Cikin zafin nama ya mik'e yai waje,  a waje yaga Abba, Abba na ganinsa wani dad'i ya kamashi da alama harya sauko kenan, Jalal ya kalleshi cikin d'aure fuska yace " Abdul d'in yana ina yanzu?"

   Abba ya girgiza kai yace " Jalal ka rufamin asiri d'an Allah wannan mutumin yafi karfin mu bani ba har Isma'il d'in dayake da kud'i."

  Jalal ya kalli Abba yace " Abba ina Abdul d'in yake yanzu? Dole ne ya nemi yafiya agun Seemah da iyayenta, kaima kuma Abba dani dolene mu nemi yafiya, duk da ba lalai a yafemana ba, wayasan wace irin rayuwa suka shiga akan kalaman nan guda d'aya?"


   Abba ya kalleshi a tsorace yace " Jalal ninaji zan bada hakuri ko mai za'amin bazan damu ba amma Jalal ba ruwanka da harkarnan, dama tun farko baka san komai ba, d'an haka yanzun ma ka nuna bakasan komai ba."

  Jalal idanunsa suka ciciko yace " Me kace Abba? In nuna bansan komai ba? Taya zan iya?"
Hawaye suka zubo mai yacigaba " akan Mahaifiyar Seemah ne fa da kuma Wanda ya rik'eta kamar 'yarsa Amininka kuma."

  Yai ajiyar zuciya sannan yai d'an murmushin yake yace " Tunda naji labarinnan nasan ban cancanci auran Seemah ba, ko da kuwa iyayenta zasu amince dani, Ammar shine ya dace da ita koda har karshen rayuwata zan kasance cikin tsananin begenta bazan kuskura inkara gangancin cewa ina santa ba."

  Kalaman Jalal sun ratsa zuciyar Abba shima ya share kwallarsa yana kallan Jalal, cigaba da magana yai da cewa " Shiyasa nakeso ko ban aureta ba insamu in mata wani abinda zaisa ta rage tsanar datamin hakan ne zaisa ta manta dani."
  Ya kara share kwalla sannan ya kalli Abba yace " Abba kataimakeni inma Seemah abu guda d'aya a rayuwar duniyar nan."

  Abba bai san sanda ya rungume Jalal ba, yace " Jalal a koda yaushe ina alfahari dakai, kafi wannan mahaifin naka tunani mai tsawo."

  Jalal idanu kawai ya runtse, shikad'ai yasan rad'ad'in dayakeji a ransa.










  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

JALALUDEEN 53

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   _*This Page is Dedicated to you ��herty�� wish u ol the best in ur Exams..... Thanks once again*_

   No. 5⃣3⃣


     Jalal jikin bango ya jingina a sulale ya tsugunna hawaye ke malala a kuncinsa, Umma dake zaune itama tana kuka ta taso ta matso kusa dashi tace Jalal! Wani irin kara yayi da duk sai da suka tsorata kuka ya wuce da shi kamar wani karamin yaro, Umma tsoro ya fara kamata ta kalli Abba tace " Meyasa ka fad'amai? Yanzu in wani abu ya sameshi fa?"

   Abba ya kalleta cikin wani yanayi, yace " daga sanda Isma'il yazo gidan nan nasan ban isa in b'oye sirrin nan ba, da wani a waje ya fad'amai mahaifinsa yaci amanar Amininsa gwara ni dakaina insanar dashi. "

  _Nikaina Ayusher yanda naga Jalal na kuka sai da naji hawaye ya zubomin a hankali nayi waje d'an bazan iya zama ba._

  A b'angaren Seemah kuwa bayan mutane sun ragune Ammar ya shigo d'akin, ya kalleta a rak'ub'e a gefen gado, tausayinta ya kara kamashi ya matso inda take tare da d'agata, kallanshi tai kamar wacce hankalinta baya jikinta tace " Ya Ammar am d'aura ko?"

  Kallanta yai idanunsa suka ciciko, hannu yasa a kafad'arta yashiga jijigata yana cewa " Get hold of your Self Seemah, please. "

  Ya d'ad'e yana jijigata kafin ta kalleshi tace " Yaya ya zanyi?"
  Yace " Seemah England zamu koma ranar bakwai inajin shi kad'ai ne zai sa ki manta komai."
   Ta d'aga kai tace " na yarda Yaya ni kaina haushin kaina nakeji."

  Nan ya mike yai waje, bai dad'e ba sai gashi ya dawo rik'e da plate na abinci, Zama yai kusa da ita tare da d'ebo abinci a cokali da niyyar ba ta, ta kalleshi sannan ta amshi cokalin tace " Zanci da kaina Oppa."

  Murmushi ya mata sannan ya mik'a mata spoon d'in, ta fara ci, yace " Matar Dad tazo ta dubaki?"
  Ta d'an tab'e baki har zatai maganar rashin kunya ta tuna ashefa ta fita matsayi yanzu, tai kasa dakai tare da cewa " Ta l'eko d'azu."
  Ammar yai d'an karamin tsaki yace " bansan ya akai Dad ya aureta ba, sam batada kara."
  Seemah tai shiru can tace " Ka manta Yaya? It is all my fault, bakaji Dad nacewa saboda ni ya aureta ba? Na sani saboda yanaso akula da......."
  Kasa karasawa tai saboda hawaye, Ammar ya kallera yai murmushi yace " Oh yazanyi da wannan kanwar tawa mai saurin kuka?"

  Ta kalleshi tare da share hawayenta tace " Yaya?"

  Yad'an rangwab'ar dakai yace " Seemah rufe idonki."
  Ta kalleshi tad'an turo baki kad'an, sannan ta rufe, hannu yasa a aljihunsa, sannan yace "bud'e."
  Da sauri ta bud'e tanasan ganin menene, kwalin waya ya mika mata, ta kalli wayar Iphone 6 ce, tace " yaya inafa da waya?"

  Yace " Dad ne yace kar abaki waccan."

  Tai murmushi sannan ta amsa tace " Thanks Bro."
  Yai murmushi shima yace " Ahhh naji dad'i kinyi murmushi, sannan kinci abinci."

  Ta kalleshi tace " saboda Deen ne ba'asan abani d'ayar wayar?"
  Ammar ya kalleta bai amsa ba, ta kara murmushu tace " karkadamu yaya, yama za'ai in sake ganinshi? Sannan bazan bari effort d'inka ya tafi ba yanda kasa naji zuciyata tayi sanyi ba."

  Ammar kallanta kawai yake, ta kara sakar mai murmushi sannan ta hure mai ido tace " Yaya kallan fa?"

  Mik'ewa yai da sauri tare dasa hannu a aljihu duk ya rikice yace " Ehem dama dama fita zan d'anyi, nan zafi ko bakya ji?"

  Batasan sanda tasa dariya ba, tace " Zafi kuma yaya? Nan d'in?"

  Kallanta yai yace " Seemah just now dariya kikai ko? Badai hallucination na gani bako?"

   Tai kasa dakai tana murmushi tace "kai yaya kai d'in ne wai zafi."

  Kallan yanda take murmushi yasa ya farajin zafin na karuwa, da sauri yai waje, yana fita daga d'akin ya fara furzar da wata iska yanacewa " Cool down Ammar."

  Can kuma yace " meke damuna?"

  Junaid ne ya dafashi yace " Ammar agidan gaisuwar ba kunya kake soyayya?"

  Kallan Junaid yai a tsorace, Junaid yai murmushi yace " Ya Habib ya fad'amin komai karka damu."

  Ammar yai ajiyar zuciya sannan ya kuma kalleshi da mamaki yace " ban gane soyayya ba kuma?"
  Junaid yace " in ba soyayya ba me kake a d'akin?"
  Ammar ya kalleshi da mamaki yace " What? Seemah ce fa a d'akin."

  Junaid ya d'an jinjina kai yace "ai sanin Seeman ce yasa na fad'a, Ammar ka nutsu ka tambayi zuciyarka, wacce irin soyayya kake mata?" Junaid na kainan ya juya yai gaba yabar Ammar da binsa da kallo.

  


   Jalal kam bayan su Abba sun fita yana nan dai a gun da yake, ya dad'e agun kafin ya daina kukan, yafara cewa " ya zanyi Seemah?"

  Jin ba amsa yasa yai shiru can yace " Abdul?"
  Cikin zafin nama ya mik'e yai waje,  a waje yaga Abba, Abba na ganinsa wani dad'i ya kamashi da alama harya sauko kenan, Jalal ya kalleshi cikin d'aure fuska yace " Abdul d'in yana ina yanzu?"

   Abba ya girgiza kai yace " Jalal ka rufamin asiri d'an Allah wannan mutumin yafi karfin mu bani ba har Isma'il d'in dayake da kud'i."

  Jalal ya kalli Abba yace " Abba ina Abdul d'in yake yanzu? Dole ne ya nemi yafiya agun Seemah da iyayenta, kaima kuma Abba dani dolene mu nemi yafiya, duk da ba lalai a yafemana ba, wayasan wace irin rayuwa suka shiga akan kalaman nan guda d'aya?"


   Abba ya kalleshi a tsorace yace " Jalal ninaji zan bada hakuri ko mai za'amin bazan damu ba amma Jalal ba ruwanka da harkarnan, dama tun farko baka san komai ba, d'an haka yanzun ma ka nuna bakasan komai ba."

  Jalal idanunsa suka ciciko yace " Me kace Abba? In nuna bansan komai ba? Taya zan iya?"
Hawaye suka zubo mai yacigaba " akan Mahaifiyar Seemah ne fa da kuma Wanda ya rik'eta kamar 'yarsa Amininka kuma."

  Yai ajiyar zuciya sannan yai d'an murmushin yake yace " Tunda naji labarinnan nasan ban cancanci auran Seemah ba, ko da kuwa iyayenta zasu amince dani, Ammar shine ya dace da ita koda har karshen rayuwata zan kasance cikin tsananin begenta bazan kuskura inkara gangancin cewa ina santa ba."

  Kalaman Jalal sun ratsa zuciyar Abba shima ya share kwallarsa yana kallan Jalal, cigaba da magana yai da cewa " Shiyasa nakeso ko ban aureta ba insamu in mata wani abinda zaisa ta rage tsanar datamin hakan ne zaisa ta manta dani."
  Ya kara share kwalla sannan ya kalli Abba yace " Abba kataimakeni inma Seemah abu guda d'aya a rayuwar duniyar nan."

  Abba bai san sanda ya rungume Jalal ba, yace " Jalal a koda yaushe ina alfahari dakai, kafi wannan mahaifin naka tunani mai tsawo."

  Jalal idanu kawai ya runtse, shikad'ai yasan rad'ad'in dayakeji a ransa.










  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

Thursday, 26 January 2017

JALALUDEEN 52

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 5⃣2⃣

   A goggon dake d'aure a hannunsa ya kalla, sannan ya jawo wayarsa dake gefensa, number Seemah ya kurama ido, ya bude gun da nufin aika mata da sako, sai dai sam ya rasa mai ma zai ce mata, a goggon wayar ya kalla karfe 1 na dare, ya runtse ido da nufin yai bacci sai dai inaa, sam ya kasa sai ma wani irin ciwo dakan ke yi masa, zama yai, yaji zaman ba dad'i ya mik'e tsaye can kuma ya kwanta, tunawa yai ashefa daren jiya baccin awa d'aya da rabi ya samu.

  Shawara d'aya ya yanke, a yanda yakejin San Seemah a ransa yana tunanin zai iya sadaukar da farincikinsa ita ta samu, indai har auren shi kad'ai ne mafitar da zaisa Seemah ta san mahaifinta ta kuma yi farinciki da ganinsa, to ba shakka zai iyayin abinda ya fi wannan, sannan shi yasani bai isa ya take hukuncin mahaifinsa ba, sai dai a da yaso gwadawa ya rok'eshi akan ya hakura da auran sai dai bukatar Seemah yasa bazai iya tambayar hakan ba.

  Ya rik'e kansa dake rad'ad'i tare da rufe ido, ya dad'e yana tunani kala kala kafin Allah ya taimakeshi bacci yai gaba dashi.

    Washegari.........

  Ranar Alhamis kenan ya kama kwana d'aya da rasuwar Hajiya sannan a d'aya b'angaren kuma yau ne ake shagalin kamun Zainab, sai dai itama Zainab ba wani farin ciki take sosai ba ga kawayenta sai tsokanarta suke, wai basuga tana waya da angon ba bare ma har yazo ganinta, murmushi kawai takeyi a ranta tace " inafa zanganshi bayan ba nice a ransa ba?"

  Jalal kam da bacci ya d'aukeshi sai karfe 10 ya tashi, shi kansa yayi mamakin ganin karfe 10, da sauri ya mik'e Alhamdulila yaji ciwon kan ya tafi, ya fad'a toilet yai wanka sannan ya zura kaya ya fito, yayi mamki daya shiga cikin gida ya taddasu suna ta hidimar su ta biki, wasu kuma suna shirin wai tafiya gidansu Amarya, Jalal ya had'e rai sannan karasa ya gaidasu Goggo ta kalleshi tace " Ango anya ma kuwa kaje ganin Amarya?"
Ya d'ago ya kalleta yace " Goggo sai kace ban santa ba? Ganinta kuma name?"
  Goggo ta shiga tafa hannu tace "lalai wannan shine bagidajen, kai an fad'ama ko a kauye ana haka ne?tsaya ma anya kuna d'an tab'a wayar nan kaji matsalarta?"

  Jalal ya kalleta yace "Goggo kenan, wace matsala zata samu yarinyar dake gidan iyayenta?"
  Goggo ta shiga salati sannan tace " oh ni yau me nake ji haka? Ni ko d'akin da aka gyara muku ma banga kaje ka gani ba."

  Jalal ya kalleta zaiyi magana karar wayarshi ta katseshi, Manager d'insu ne hakan yasa ya mik'e tare da cema Goggo yana zuwa, yana fita ya d'aga wayar, Manager yacemai "Jakal ya? Ka tura takardar kuwa?"
Jalal yace " oh God wallahi na manta amma bari na musu sending yanzu."
Ran Manager ya b'aci yace " Jalal wai me ke damunka ne? Sam ka daina maida hankali akan aikin ka sannan yanzu kayi tafiya ba rubuto takarda nakasa fahimtar ka yanzu."
  Jalal yai kasa dakai baice komai ba, ganin haka yasa Manager ya katse wayar.
  Komawa yai kan dakalin kofar gidan ya zauna, Umma ta aiko yazo yaci abinci, ya kalli d'an aiken tare da cewa " banajin yunwa sai dai anjima."
  Daga bayama mik'ewa yai ya tafi can bayan gari ya zauna shi kad'ai.

    Rana bata karya, a yau ne ranar asabar uku ga mutuwar Hajiya haka kuma a wannan lokacin ne aka gama d'aurama Jalal aure a massalaci, kana ganinsa zakaga ya rame sosai, sannan sam ya canza Umma kam harta gaji da fad'an rashin cin abincinsa, ana gama d'aurin aure ya wuce gida ya shiga d'akinsa, abokai 'yan uwa da iyaye sai cigiyarsa sukeyi a d'au hoto sai dai an nemishi an rasa, shikam yana kwance cikinsa na mai wani irin ciwo, agoggonsa kawai yasa a gaba yana kallo.

  'Yan d'aurin aure sun watse, Abba ya taho gida shikanshi farincikinsa ragaggene d'an yana tsoron abinda zai faru a yau tsakaninsa da Jalal.
  Yana isa kofar gida kuwa yaga Jalal a tsaye, kallan mamaki yamai yace " Jalal meye hakan? Kasan dole ne a nemeka amma shine kayi tahowarka gida ko?"
  Yai kasa da kai yace " Yahkuri Abba banajin dad'i ne."
  Abba yamai kallan tausayi duk ya canza,  Jalal yace " Abba jiranka nakeyi, akan alk'awarin dakamin."

  Abba ya d'ago a tsorace yace "Jalal!!!."
Jalal yace " Abba d'an Allah na rok'eka daka cika alk'awarinka na fad'amin d'in dakace zakai."

  Abba yai shiru sannan yace " muje d'akinka."
  Nan suka juya suka shiga soro inda d'akin Jalal yake.

  A b'angaren Seemah kuwa tunda ta tashi da asuba, taketa maimaita wannan ranar a ranta, lungun gado ta samu ta rakub'e duk yanda Zahra tai da ita inaa abin yaci tura ga maza duk suna gun karb'ar gaisuwa, agoggon hannunta ta cire tare da rungumeshi a kirjinta, idanunta sun kad'a sunyi jaa.
Kalma d'aya ke yawo a ranta " *Deen an d'auramai aure da wata.*"
  Daga karshe Zahra da Aisha sai zuba mata ido kawai sukai.

 

  Jalal zaune a kasa, Abba nakan katifarsa dayake kwanciya, Jin kwankwasa kofar yasa Abba yace " Shigo."
Jalal yabi kofar da kallo, Umma ce ta shigo rik"e da tire, da samiru d'aure a kai, ta ajiye a gaban Jalal, Abba yace " Jalal bismilla."
  Kallansa Jalal yai yace "Abba amma ni......"
Abba ya katseshi yace " in har kanaso kaji sai kaci abinci, bansan inkaci wannan abincin kuma sanda zaka karacin wani ba."

  Jalal ya kalleshi da mamaki, Umma ta zauna a gefen Abba tare da bud'emai kwannon shinkafa da miyar da akai, nan Jalal ya fara cin abinci sai daya cinye tass sannan Abba yace " Habiba kema ki zauna ."
  Nan Umma ta zauna Abba ya kalli Jalal cikin tausayawa sannan yafara bashi labari tun daga farko........................
Har sai da yazo kan ranar da Fatima tazo shagonsa, Jalal hawaye kawai yakeyi na tausayawa Fatima.
  Abba yai ajiyar zuciya yace " Nafita kiran Isma'il ne a lokacin dana bar d'ana a shagona shida Fatima akan su jira ni, na fito naga maza guda 5 sun nufo shagon, karasawa nai kusa dasu tare da cewa  d'an Allah ina sauri ne amma in kunje akwai d'ana a shagon sai ku bashi kud'in.
   Sai a lokacin na kuka da kamaf abu suke sha, jin warin abin ma yasa na gane wiwi ce, na d'an ja baya sannan nace " hmm kuyi hakuri nad'auka shagona zaku.
  Ogan cikinsu dana kula shi bayashan komai ya matso kusa dani yace " Amadu Tambaya, Fatima wai na shagonka?"
Na kalleshi sai a lokacin na gane Chairman d'in garin mune wanda ake tunanin nad'awa a satin, kuma yaron gidan da Fatima ke aiki, kuma mijin da zata aura nan da kwana biyu. na kalleshi nace " Chairman nemanta kake?"
Yace " Eh yanzu abokaina sukace tun d'azu suka ganta a shagonka." sam har kasan zuciyata na d'auka ko k'iranta ake ko kuma shi ke san ganinta ko saboda wani abu, na kalleshi nace " Chairman kayi hakuri yanzun nan zata koma gida......."
Kafin na karasa maganata naji an kifamin mari, da sauri na kalli wanda ya naren d'aya daga cikin abokan Abdul d'in ne nace " Kai meye hakan kuma?"
  Wanda ya maren d'in yace " Wai Abdul kai wani irin mutum ne? Ya za'ai kana Matsayin Chairman ace wani banza mai shago har zai kalleka yad'inga ma tambayar banza? Banace ka barni nai handling d'in komai ba? Kobakasan ka d'ana ne?"
   Abdul ya kalleshi ga mamakina kamar me  tsoransa naga yaja baya, daidai nan cikin rashin sa'a ashe d'ana na kallanmu d'an muna kusa da shagon, ganinsa mukai yazo tare da kallan wanda ya maren d'in yace " Malam me Babana ya maka?"
  Wata muguwar dariya ya saki sannan yace " Good haka nake so."

Ban kawo komai a raina ba kawai sai gani nai an cafke min d'ana, an kuma samai wuka a wuya, nan fa ya shiga kuka.
   Na rikice sosai, kuka yakeyi sosai nima na shiga rokonsu,dariya suka samin na d'azun da ko sunanshi ban sani ba ya cilla ma wani d'an nawa tare da matsowa kusa dani yace " karkuma kai tunanin wannan ne kad'ai matarka tana hannunmu, ahh abin tausayi ko?"
    Sannan ya kalli Abdul d'in yace " kayi tafiyarka ko itama tafi karfin ka?"

Abdul ya girgiza kai yace " ai ko d'aureta ne sai nayi, ina gani ya nufi shagona ina ihu akan karyayi.......

  Kallansa nai duk na gana rikicewa nace d'an Allah kuyi hakuri, karku lalata mata rayuwa. Naga tashin hankali a lokacin kuma abin da yaban mamaki ba wanda yazo wucewa, gashi kamar sun tambaya, ba wutar nefa gashi dama a lokacin ba gen ake kunnawa ba.
    Dariya suka samin dashi sannan aka kwad'ama d'ana k'otar wuka a goshi wani ihu yasa kawai sai ga jini kankace mai......

Kuka nake sosak, suka cemin matarka da alama bata ma da lafiya ko? Na d'ago da mamaki d'an ko ni ban sani ba, suka kwashe min da dariya sukace dataji azaba cemana tai wai muyi hakuri karmu bari abin cikinta ya zube.

  Nan na matso tare da rik'e kafafunsu, tashin hankali ne ya karune a sanda suka fito da bindiga, suka nunani sannan suka nuna d'ana sannan sukace " kaje ka k'ira ma Fatima wanda take jira kayi sauri kafin Abdul ya mata ila."
  Na d'auka tausaya mata sukai hakan yasa da sauri na wuce na tadda ana fitowa daga masallaci nan na gyara fuskata na shiga cikin masu fitowar, Isma'il na gani na d'aure na sanar dashi Fatima na nemansa na gaggawa.
  
  Mun taho gabana sai faduwa yake, muna zuwa zan shiga sai naga sun min alamar inzo, hakan yasa Isma'il ya shiga shi kad'ai ni kuma na je gunsu, sukamin tafi sukace yauwa ka kyauta.
  Na kallesu nace d'ana fa? Mugun ya tab'e min baki sannan ya kalli Abdul da nima sai a lokacin na kalleshi yanasa wando, zaro ido nai nace " meke faruwa?"

    Hoton D'ana aka nunomin an saitashi da wuka sannan matata ansaita ta da bindinga, sukace abu d'aya zakai ka cecesu.
Kuka nake sosai ina rok'onsu, ban farga ba kawak naji karar mutanen gari, sukace cewa kawai zakai Abokinka Isma'il shiya mata fyad'e.

  Girgiza kai na shigayi ina kuka, mugun yace " to shikenan ka taimaki abokimka in yaso matarka da d'anka, da wanda ba'a haifa ba kwa had'u a lahira.

   Abba na zuwa nan yai share hawayensa, Umma ma haka, Jalal kam kukan ya kafe kaf kawai Abba yake kallo wani irin kallo daban fahimceshi ba ni kaina.
  Jinai cikin wata irin murya Jalal yace" Saboda tsoron kar ama matarka da d'anka ila yasa ka ce Amininka ne ya mata fyad'e?"
   Abba ya kalli Jalal sannan ya kara goge kwalla yace " Akan d'ana ba abinda bazan iyayi ba, ina ganin ansama d'ana wuka za'a yankashi mezai sa inkasa fad'ar kalma d'aya?"

  Jalal ya mik'e ya shiga jijiga kai sannan ya kalli Abba sai a lokacin wasu zafaffen hawaye suka fara zubo mai, Abba ya matsu tare da kokarin rik'e hannunsa Jalal yayi baya.




  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM.*

  *Gaisuwa ga duk Masoyan littafin nan ....I Luv u Ol*❤����

Wednesday, 25 January 2017

JALALUDEEN 51

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 5⃣1⃣


    Seemah zaune take kawai, a rakub'e a jikin gado, sai kallan y'an uwa take suna zuwa gaisuwa, sam ko magana batayi bare cin abinci, duk ta rame ta canza a kwana d'aya.
   Tana zaune tana jan carbi taji sallama, jin muryar yasa ta d'ago da sauri, Junaid ya kalleta tare da sakar mata murmushi, kuramai ido tai a hankali hawaye suka zubo mata ya matso kusa da ita tare da cewa " Kanwata ai saura kiris in kasa gane ki, wace irin jinya kikai haka?"

  Kallansa tai kawai ga mamakinsa sai yaga ta fashe da kuka, kallanta yai da namaki, sai kuma can yace " Seemah mutuwa fa ba'a san a d'inga mata irin wannan kukan, bare Hajiya da batasan kuka addu'a kawai zamu mata."

   Seemah ta d'ago a hankali tanasan mai magana, yace " anma wani irin cinwo kikai haka?"

   Zahra ce ta shigo ganin Mutum yasa tai kasa dakai tare da gaisheshi, Junaid ya d'ago ya kalleta yace" Badai badai ba?"
   D'agowa tai tare da nuna shi tace " yayana?"

   Kallanta yai yad'an kanne ido yace " badai badai ba?"
Tace " badai yaya bane wannan?"

  Dariya yai yace " na d'auka kin manta inkiyar tamu."
Tai murmushi tare da matsowa tace " yayana yaushe a gari?"
  Yace "d'azu na shigo ya hakurin mu?"
Tace " Alhamdulila"
Kallan Seemah yai yace " Kanwata mey........"
  Da sauri Zahra ta katseshi tace " tashi yaya muje ka gaida Mamie."
  Ya mik'e tare da kallan Seemah, nan sukai waje, Seemah ta share kwalla Allah sarki rayuwa, a da tad'auka 'yan uwanta ne na jini yanzu kuwa ta gane ashe bata da alaka da dukansu, itafa? Inane cibiyarta? Suwaye 'yan uwanta?.

    Jalal yayi sa'a a kofar gida yaga Abba, da sauri ya karasa gunsa, Abba ya kalleshi yace " Jalal kai nake jira ai, na shiga ciki aka sanar dani ka iso."
  Jalal ya kalli Abba tare da cewa " Ina Kwana?"
  Abba ya amsa tare da rik'o hannun Jalal yace " Nagode Jalal da baka bani kunya ba kazo tun kafin ranar bikin, nagode kwarai, Zainab ta koma gidansu acan zasuyi taron su."

     Jalal kallan Abba kawai yakeyi, can yace " Abba inada magana mai mahimmanci dakai."
  Kallansa Abba yai yace " Jalal wace magana ce haka da bazaka bari sai bayan biki ba?"

   Jalal ya girgiza kai yace " Abba banajin zan iya runtsawa sai naji abinda ke faruwa."
  Gaban Abba ne ya fad'i ya kalleshi cikin tsoro yace "Jalal me kakesan ji?"
  Jalal yai ajiyar zuciya sannan yace " Abba meye tsakaninka da Dad d'in Seemah?"
  Da sauri Abba ya juya baya gabansa ya cigaba da fad'uwa, Jalal ya kalleshi sannan ya matso ta gabansa, yace " Abba bai kamata ka cigaba da b'oyemin wani abu ba, me ka musu suka tsaneka haka? Meye tsakanin ka dasu dahar suke tunanin kafisu sannin abinda si basu sani ba?"

   Abba ya had'iyi yawu sannan cikin tsoro yace " Jalal banasan maganan nan na kuma hanek da karamin."
  Ga mamakin Abba kawai gani yai Jalal ya tsugunna a gabanshi, yace " Abba d'an Allah ka fad'amin bakasan yanda nakeji a zuciya ta bane a wannan lokacin."

   Abba yai ajiyar zuciya  yace "naji zan sanar dakai abinda yafaru amma da sharad'i sai ka min alkawari."

  Zuciyar Jalal ta matsu taji komai yace " na ma Abba koma akan menene."
  Abba ya kalleshi idanunsa sunyi ja, yace " tun ranar da Isma'il yazu gidan nan nasan sirrin nan dole ne ya bud'u, in har kuma kanasan insanar dakai sai kamin alkawari tsakaninka da Allah cewar ko menene tsakanin mu bazai hanaka auren Zainab ranar Asabar ba."

   Jalal ya d'ago da sauri ya kalli Abba yace "Abba me kake nufi?"
  Abba yace" bazan sanar dakai ba har sai ranar da aka d'aura muku aure da Zainab."

  Jalal ya mik'e a zabure yace " Abba d'an Allah......"
  Abba ya katseshi da cewa " In har kanasan kaji to sai ka jira ranar auranka, alkawari na maka kaima kamin, haka ya kamata mu barshi."

  Abba na kainan ya wuce cikin gida, Jalal bai kula bane amma hannun Abba rawa yakeyi.

  Jalal ya naushi bango da hannunsa yana huci ya rasa mai zaiyi.
  Wayar Sagir ce ta katseshi, ya d'aga da sauri tare da cewa " Sagir ya Seeman?"
Sagir yai shiru, Jalal yace Sagir ya kai shiru?
  Sagir yace " Jalal kakarta ta rasu."
  Jalal yafara " *Inna lilahi wa ina ilaihi Raji'un*"
Nan ya kashe wayar tare da silalewa ya zauna a dandaryar kasa, hannu biyu yasa ya rufe  fuskarsa zuciyarsa na k'una, wani hali Seemah take ciki? Ance in tambayi Abba mahaifinta shikuna yace sai na auri Zainab, idanu ya runste sai ga hawaye sun zubo, Seemah ya zanyi?

  Mutane sai wucewa suke suna kallansa.
  Ya dad'e a gun kafin ya mik'e ya fara tafiya, wayar Ammar ya d'aure ya k'ira, daga gun Ammar dake zaune gun amsar gaisuwa ganin k'iran Jalal yasa ya mik'e yai gefe tare da d'agawa, Jalal yai sallama Ammar ya amsa, Jalal yace " Ammar ya hakuri? Ya kuma jikin Seemah? Tanacin abinci kuwa?"

  Ammar yai shiru can yace" Jalal baka fahimci abinda muke nufi bane? Ko kuwa idanunka ne suka rufe?"
  Jalal yai shiru, Ammar ya cigaba " abu d'aya muke buk'ata agunka ka tambayar mana mahaifinka waye mahaifin Seemah shikad'ai mukesan ji daga gareka."yana kai nan ya katse wayar, tare da kasheta gaba d'aya.

   Jalal ya samu wani dakali ya zauna kamar maraya, kalaman Ammar kawai yake tunawa........




  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

Tuesday, 24 January 2017

JALALUDEEN 50

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 5⃣0⃣

 
       Jalal ganin Seemah a sume ya rasa inda zaisa kansa kuka kawai yake, yarasa meke faruwa shikem, addu'a kuwa duk wacce tazo mai yi yakeyi, kallanta yakeyi zuciyarshi sai kuna takeyi, Ammar ne yashigo da likita da sauri, nan likitan ya shiga duba Seemah, ya samu ta dawo daidai ya kalli Ammar da Jalal yace " ba nace kar a tada mata hankali ba? A barta ta samu nutsuwa ba? Ina tsorace muku abinda zai faru inbaku kiyaye dokukin nan ba."

  Yana kai nan yai waje, Jalal ya kalli Ammar da idanunsa da suka sha zubar da kwalla, yace " Ammar am.........."
Ammar ya katseshi da cewa " Jalal please get out."
  Jalal ya kalleshi cike da tausayi yace " amma......"
   Ammar ya d'aga mai hannu tare idanunsa taf da kwalla yace " Jalal kake kawai please. "
  A hankali Jalal ya karasa kusa da Seemah ya kalleta cikin tsananin tausayi da bege sannan ya juya harya kai kofa yaji muryar Ammar yace " idan kaje katambayi Mahaifinka waye mahaifin Seemah, shikad'ai ne abinda muke bukata yanzu daga gareka."

  Juyowa Jalal yai cikin tsantsar mamaki bai fahimci inda kalaman suka dosa ba, me suke ba Dad bane mahaifin Seemah ko me?"

   Dad ya gani a bakin kofa, wani irin kallo Dad yamai, Jalal yai kasa dakai tare da cewa " Yahkuri na sab'ama umarnink......"
  Hanya Dad ya nuna mai alamar yai waje, hakan yasa Jalal ya taka a hankali yai waje, yana fita yazauna akan dakalin gun, tare da rik'e kansa dake wainawa, agogon hannunsa ya kalla karfe 2 na dare ya buga, mik'ewa yai a hankali bayaji zama ya kamaceshi dole gobe da sassafe ya dira a birnin/gwari d'an jin me mahaifinsa ya sani dangane da abinda ke faruwa, kofar d'akin Seemah ya kalla tausayinta ya kara ratsashi, da alama yau tasan ba Dad bane mahaifinta sannan me ake nufi da Abbansa ya sani?
   Da alama Abba ne kad'ai yasan amsar tambayoyin nan.

    Seemah kam sai karfe hudu ta bud'e ido a hankali, Ammar ta kalla dake zaune akan kujera yana bacci, ta mik'e a hankali tare da yaye bargon da aka rufa mata, tai bakin kofa, a hankali ta bud'e kofar gudun karta tasheshi.
   D'akin Hajiya ta shiga, Dad na zaune shima yana bacci, ta karasa kusa da Hajiya tare da rik'e hannunta da hannuwanta biyu, Hajiya ta bud'e idanunta ta kalleta, Seemah hawaye suka zubo mata tai kasa da ido tace " Hajiya kiyi hakuri nasani dolene ki tsaneni, ko nice akama d'ana haka dolene in tsani duk masu hannu a harkar, sai dai nasani a kasan ranki baki tsaneni ba."
    Kallanta Hajiya tai da alamar tambaya, Seemah ta matse kwalla tare da kakaro murmushi tace " da kin tsaneni nasan da kin tilastama Dad ya rabu dani, da bazaki bari har ya rainani izuwa yanzu ba."

   Ta zare hannun hagunta ta share hawayen dake mata gudu tace " Nagode Hajiya da taimakonki, nagode sosai Allah ya saka da alkairi."

  Hawaye ke zuba a idanun Hajiya a hankali tasa d'ayan hannunta akan Seemah sai dai abinda takeji a kirjinta mai nauyi yasa ta kasa magana, Seemah ta girgiza mata kai tace " A'a hajiya basai kince komai."

  Tai ajiyar zuciya sannan tace " Hajiya na rok'eki ki yafema mahaifiyata da ni, d'an Allab ba dan mu ba."

  Seemah na kawo nan taji kuka na neman kufce mata, Seemah tasa kanta a jikin gadon ta shiga kuka mai tab'a zuciyar mai sauraro.

    Dad kam tunda ta shigo yanajinsu, kawai dai yayi shiru ne, Hajiya tasa hannu ta d'ago fuskar Seemah tare da share mata hawaye.

   Sun dad'e a haka kafin Ammar ya shigo da sauri, a firgice yake da alama yad'auka ko Seemah ta gudu me ko wani abun, ganinta kusa da hajiya yasa ya saki nannauyan ajiyar zuciya, Seemah ta kalleshi tare da mik'ewa.

   Bayan Sallah asuba su Dad sun tafi massalaci, suna dawowa suka ba kamar yanda suka barta ba, da sauri Dad ya karasa tare da tab'ata sai dai inaaaa.... Allah ya d'auki ran abarsa.

  _Allah yasa mu gama da duniya lafiya Amin_

  Ba karamin tab'asu tai ba wannan rasuwa, abu goma da ashirin.
  Sun dawo dukansu gidan Abba anan aka mata wanka, Seemah ma ta matsa dole itama ta dawo gida.

   Jalal kam yana sallar asuba ya wuce tasha, a mota a zaune kawai yake zuciyarsa taf take da tunani kala kala.
  Sun isa birnin gwari ya hau mashin ya karasa gida, yana sauka ya tsaya a kofar gidan tare da kwankwasawa, ba'ai minti 2 ba akazo aka bud'e, ga mamakinsa kanwar mamansa ce, tana ganinsa ta saki guda ya shiga tare da cewa " Goggo yaushe kika zo?"

  Ai ba gama rufe baki ba yaga 'yan uwan Abba da Umma suna ta fitowa ya kallesu da mamaki yace " toh! Taran me ake haka?"

  Goggo ta harareshi tace " Lalai wannan Angon ba kunya, watoma da alama bakasan a taru ayi zumunci a bikinka."

   Jalal ya maimaita kalmar Ango?
Umma ce ta fito fuska d'auke da fara'a tace " Jalal me kake a tsaye bazaka shigo ka kwashe gaisuwa ga 'yan uwa ba?"

  Ya d'anyi murmushi kad'an sannan ya shiga ya zauna sannan ya fara gaishesu, kowa sai tsokanarsa suke, ya mik'e tare da tambayar Umma ina Abba?, tace " ya fita d'azu zaije siyo kayan abinci." sai alokacin ya kuka da har fenti anyi a gida, badai da gaske suke ba?
  Yace "Zaheeda fa?"
Tace " tana d'aki." Nan ya wuce ransa duk a dagule, kusa da Zaheeda ya zauna, ta kalleshi tare damai murmushi yace " Kanwata da alama kina cikin farinciki, ko duk ganin 'yan uwa ne?"

Muryar Umma yaji tace " Dad'i takeji zaka auri 'yar uwarta Zainab."

  Jalal ya juyo ya kalli Umma yace " Wai Umma meyasa kuke min haka? Nifa ban d'auka abinnan da gaske kuke yi ba."
  Umma ta had'e rai tace " baka sani ba mai ya kawoka to? "
  Jalal yad'an furzar da iskar bakinsa yace " Zuwa nai muyi magana da Abba, ni banajin ma zan iya jiranshi ya dawo, Umma kawai fad'amin inda yake."

   Umma ta kalleshi tace " Ba dai cewa zakai ya janye auren ba?"

Jalal yad'an juya kai yace " ni auran nan ba'a gabana yakeba Umma, abun da ke damuna yafi karfin wannan auran."

  Umma ta kalleshi da mamaki tace " Badai......"
Jalal yai saurin cewa " Umma d'an Allah ina Abba?"
Tace" Yana lambun Basiru."
Jalal ya mik' e tare da kallan Zaheeda sannan ya juya, Umma ta matso kusa dashi tace " Jalal yanaga kamar ka fad'a? Sannan da alama akwai abinda ke damunka naga gaba d'aya fuskarka ta canza."

Kallanta yai sannan ya runtse ido yace " Umma banaso 'yan uwa susan abinda ke damuna shiyasa nake kok'arin b'oyewa kibari inje gun Abba tukun."
  Tai ajiyar zuciya tace " to sai ka dawo."


  Jalal ya fito, sai tsokanarshi ake, shikam sai yake kawai yake musu, yana fita Goggo ta shigo gun Umma tace " Yaya Habiba nikam kamar Jalal baya farin ciki."
   Umma ta kalleta tace " meyasa kikace haka?"
Goggo ta d'an rik'e hab'a tace " gaskiya bama haka Jalal yake ba sam, naga kamar ya canza, halayarsa ma kamar ta canza, Allah dai yasa ba wani abun bane."

  Umma ta kalleta sai dai ta kasa bata amsa, Addu'arta d'aya Allah yasa ba zancen nan Jalal zaina Abbansa ba.

   Jalal kam kai tsaye Lambun Basiru makocinsu ya isa, yanazuwa Basirun yace " yanzu kuwa yabar nan, ya koma gida."

Jalal ya juya yai hanyar gida, wayarsa ya rik'e wazai k'ira ya tambaya jikin Seemah?
  Da sauri ya k'ira Sagir bayan sun gaisa yace "Sagir d'an Allah ka dubomin halinda Seemah ke ciki."
Sagir yace " to, nan sukai sallama."


  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

Saturday, 21 January 2017

JALALUDEEN 49

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   *_This Page is for you my dearest Friend Umma, and also my Swt kanwa Somaya�� Miss Hot Purple luv u soo much_*


   No. 4⃣9⃣

   Jalal kam yana tsaye a gate d'in gidan su Habib, mai gadi ya kalleshi yace " Bawan Allah d'an Allah ka tafi na fad'ama Hajiya Seemah bata nan."

  Jalal ya kalleshi sannan yace " naji ai baba kuma na yarda to so nake naji tana ina?"

  Zaiyi magana sai ga Aisha ta fito da alama asibitu zata kai abinci ganin basket d'in kuloli a hannunta, kurama Jalal ido tai kamar tasan shi, can ta matso tare da mik'ama Bala basket d'in yasa a mota.
  Ta kalli Jalal tace " Kamar na sanka ko?"
  Jalal ya kalleta yace " anya kuwa? Amma da alama daga gidan kike, Seemah fa?"
   Sai alokacin ta tuna shine yaja Seemah rannan da suka fita tare, ta sakarmai murmushi sannan tace " tana gidan Yayan Babanta amma yanzu ya Habib yai waya yace wai ankaita asibiti da alama batajin dad'i."
  Jalal yace " mene? Meya sameta? Zazzab'i take?"
  Dariya Aisha tai tace " wanne zan amsa daga ciki? Bayan nima bansan komai ba? Yanzu dai zanje asibitin sai ku tafi tare."
   Jalal ya runtse ido sam hankalinsa ya gaza kwanciya, nan Bala ya fito da mota Jalal ya shiga gaba suka wuce asibiti.
  Seemah kam bayan ta farfado sai ta hau rawar sanyi, nan likitan yasa mata drip sannan ya roki da abarta ita kad'ai da alama taji abinda ya firgita tane.
  Abba, Dad, Kawo, Ammar, Habib, da Mamie suna zaune a d'akin da aka kwantar da hajiya, itama dai jikin ba dad'i a zaune kawai suke amma kowa da abinda ke ransa.
Sun isa asibiti, Aisha ta kalleshi tace " zamuje tare ne?"
  Jalal ya tuna kalaman Dad na d'azu hakan yasa ya kakaro murmushi yace " Jeki kawai karma asan tare muka zo."
Ta kalleshi da mamaki amma bata tambaya ba ta ce to, sannan tai gaba.
  Jalal kam zuciyarshi ta gama dakewa abu d'aya kawai yasa a ransa awannan lokacin shine bazai tafi ba tabbas sai yaga Seemah, saboda gobe yakesa ran zuwa Birnin/gwari d'an yaji menene tsakanin Dad da Abbansa.
  Karasawa yai bakin d'akin da aka kwantar da Hajiya bai shiga ba kuma bai kwankwasa ba kawai a tsaye yake, sam baisan d'akin kusa da Hajiya nan aka kwantar da Seemah ba.

Bayan Aisha takai Abincin ta fito ne wajen bud'e kofa yasa Habib ya hango Jalal, ransa ya k'ara tunzura a zuciye ya fito waje yazo kusa da Jalal ko kofar bai rufe ba, a lokacin ne hankalinsu yakai kansa.
     Habib na zuwa kusa da Jalal, kafin Jalal yai auni yaji an makamai naushi a kunci, dukan ya shigeshi d'an sai da gefen leb'ensa ya fitar da jini, Habib ya mik'e zai k'aramai wani Jalal ya rik'e hannun.
    Daidai nan 'yan d'akin suka fito, Kallan kallo suka fara kafin Jalal yace " Ya Habib mena maka kuma?"
   Fizge hannunsa yai da karfi sannan ya nunashi da 'yatsa yace " Jalal wallahi id'an har baka bar nan cikin minti 5 ba bansan me zan ma ba."
   Kallansa yai da alamar tambaya yace " na maka wani abin ne? A iya sanina ban ma abinda zan cancanci duka ba."

    Muryar Abba ce ta katsesu yace " Habib meye hakan kake?"

Habib ya bugama Jalal wani kallo sannan ya wuce d'akin, kowa ya koma d'akin aka rufe kofar, Jalal yabi kofar da kallo, jiyai ansake bud'ewa Ammar ne ya fito yazo kusa dashi tare da mik'amai handkerchief,  Jalal ya kalleshi da jajayen idanunsa sannan ya amsa, a hankali ya furta thanks.

   Ammar ya kalleshi yace " please Jalal ka tafi."
  Jalal idanunsa suka kara kad'awa yace " Ammar menai? ni Seemah kawai nakesan gani naji ance bata da lafiya, banaji zan iya tafiya ba tare da na ganta ba."

    Ammar ya runtse ido shima idanunsa suka ciciko, yace " Banaji itama Seemah zata so ganinka a wannan lokacin."
  "Meyasa? Taya akai kasani? Banaji itama akwai abinda zaisa takisan ganina."

   Ammar ya dafa kai sannan yace " ni kaina daurewa kawai nake amma basan magana dakai nakeba, ka koma ka tambayi mahaifinka waye ya rad'ama suna? Da wa aka haifeku rana d'aya? Sannan wani irin sakayya yama babban amininsa?" Yai ajiyar zuciya sannan ya cigaba" wad'annan amsoshin sune zasusa kagane meke faruwa."

  Ammar nakainan ya bud'e d'akin da Seemah take yasa kai, daidainan Jalal ya hangota kwance akan gado ana mata k'arin ruwa, daga nesa ya hango fuskarta jiyai kamar zuciyarsa zata fito, kofar ce ta rufe sakamakon turata da Ammar yai, Jalal yabi kofar da kallo idanunsa sunyi jaa ga sun ciciko, kurama kofar ido yai, ga magrib tayi.

   Wucewa yai yaje massalaci, suma sun firfito sallah, bayan sunyi sallah kafin su koma shi ya rigasu isa, harya sa hannunsa zai bud'e kofar, yaji bazai iya ba tabbas bazai shiga ba harsai ance ya shiga, kuma bazai tafi ba harsai ya ganta.

  Komawa yai ya tsaya a gunsa na d'azu, ga mamakinsu duk sun d'auka ya tafi sai dai ganinsa yasa suka d'auke kai suka shiga, Dad da Ammar sukai d'akin Seemah, suna shiga daidai nan ta bud'e idanunta a hankali, haryanzu jikinta zafi tsau kamar garwashi, ta kurawa Dad ido, ita kad'ai tasan me take tunani, kallanta yai tare da cewa " Swthrt kin tashi?"

  Ta k'ak'aro murmushin da kana gani kasan yak'ene ga leb'enta ya bushe, a hankali tace " Dad tambaya nakesan yi?"
"Inajinki 'yar Dad."
Had'iyar wani abu tai sannan tace " Jafar da aka haifa rana d'aya da Ya Ammar, wanda mahaifinsa yama sharri ya kuma cutar da mahaifiyata, shine........?" jitai ta kasa karasawa sai motsa baki take tanasan magana amma kuka ya hanata, Ammar ya share hawayensa tare da matsowa kusa da ita yace " Dad zan bata amsa jeka kawai."

    Dad ya mik'e jiki a sanyeye, Ammar ya matso kusa da ita ya zauna, tare da kallanta yace " Seemah sai me? Inshine Jafar d'in da kikeso? Meye zaisa ki k'ara tada hankalinki?"

   Kai ta shiga jijigawa tace " akwai komai kuwa yaya."
Hannu tasa a saitin zuciyarta tad'an buga kad'an tace " taya za'ayi zuciyata taso wanda d'ansa ya taimaka wajen ruguza rayuwar mahaifiyata? Meyasa nakejin zuciyata tana zafi?"

   Kuka ne yaci karfinta hakan yasa ta kasa karasawa, Ammar ya share kwallarsa yace " Seemah please kidaina please Seemah."

   Kuka take sosai ta kasa tsagaitawa, dakyar ta daina sai kuma ta shiga ajiyar zuciya akai akai.

  Jalal kam har karfe 12 yana nan a tsaye, harsu Kawo da Abba da Habib suka koma gida sukabar Dad agun Hajiya, Ammar agun Seemah.

  Kowa mamakin yanda yak'i tafiya yakeyi, gashi a tsaye yake ko gajiya baiyi ba ne ko me? Dad yana tsaye ta window yana kallansa, har bacci yafara d'aukan Dad, Ammar kam gun Seemah ya koma, ya kalleta yace " Seemah, Jalal fa na waje tun kafin magrib yake a tsaye a waje."
  Kallansa tai cikin mamaki idanunta suka ciciko tace " Yaya?"

  Jinjina mata kai yai yace " ko na karshe ne ki ganshi kuyi sallama."
  Ta share hawayenta tare da cewa "Ya Ammar?"

Mik'ewa yai ya fito tare da kallan Jalal da kana ganinsa kasan dauriya ce kawai yakeyi ta jaruman maza amma tabbas ya gaji, ya kalleshi yace ka shiga.

  Jalal ya d'ago ido tare da murmushi yace " tnz Ammar."

  Sai dai me? Sam ya kasa d'aga kafarsa jiyai kafar tamai nauyi, sai Ammar ne ya taimaka mai ya shiga d'akin, a tunanin Ammar Dad yayi bacci, sai dai Dad jin magana yasa ya lek'o ta window yana kallansu har Jalal d'in ya shiga.

  Kusa da Seemah ya zauna, sam ta d'auke kai daga kan Jalal, Ammar ya fita ya basu guri.

  Jalal ya kalleta baisan sanda hawayen da yake b'oyewa suka zubo ba, a hankali yace " Meemah ya jikin?"

  Jin sunan Meemah da yak'ira sai da zuciyarya ta amsa, batasan sanda ta kalleshi ba, idannunta na hawaye, yace " ya akai kika rame haka a kwana d'aya? Bakya cin abinci ko? Hala shiya haifar miki da zazzab'i."

    Ta had'iyi wani abu sannan ta kalleshi tace " meyasa kazo nan? Bayan banasan ganinka?"

  Jalal ya girgiza kai hawaye ya zubo mai yace " ta ina zakik'i san ganina bayan zuciyarmu na tare?"

  Ta share hawayenta tace " a da kenan."
  Jalal kalmar har ransa ta tab'a amma ya d'aure yace " bana tunanin a da ne, tunda haryanzu zuciyoyinmu basu rabu ba."

  Mik'ewa tai ta zauna fuskarsu na kallan juna ta goge hawayenta tace " Deen I can't be with you ko da kuwa sanka shine zai zama ajalina, mahaifinka ya cuceni, ya cuci mahaifiyata, ya cuci Dad d'ina bama haka ba ya cuci duk zuri'ata data Dad banajin zan iya yafe mai."

   Jalal ya kalleta cikin mamaki, idanunsa ya zaro yace " Meemah me kike nufi da kalamanki."

  Hannu tasa ta fara dukan kafad'arsa tana kuka tace " Meyasa zuciyata bazata tsaneka ba why?"

  Jalal ya rik'e hannunta yace " Meemah me mahaifina yai?ban gane ba?"

    Ganiyai jikinta ya shiga rawa, duk ya rud'e tare da K'iran sunan ta, ai ganiyai tayi luuu gab'a d'aya jikinta.

  Da karfi yake k'iran sunanta yana hawaye, Amnar ya shigo da sauri, ganin haka yasa ya fita k'iran likita.

  Abinda yaban mamaki, Jalal nagani ya tsuguna yana kuka kamar mace,  a raina nace baka fara bama d'an saurayi.





  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

Friday, 20 January 2017

JALALUDEEN 48

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 4⃣8⃣


    Anyi suna lafita kowa na murna, Abba kam shima a lokacin Mamie nada tsohon ciki hakan yasa batazo ba, sai dai tunda akai suna jikin Samira yak'i dad'i kullum cikin cuta.

   Fatima kam duk karshen sati suna zama da Isma'il a makaranta ya koya mata karatu, a sanu a sanu wata shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu batare da Isma'il ya farga ba, sai dai bai tab'a tunanin zai iya furta mata yana santa ba saboda sau dayawa yanaji tana zancen batasan kishiya.

   Rayuwa kenan yanzu an wayi gari shekararsu Jalal 5, kusan kullum Jalal na gidansu Ammar inkuwa baizo ba to zakaga Ammar a nasu gidan.

Jalal ya taso yaro mai zuciya, shikuma Ammar hakuri gareshi, a duk lokacin da yara sukaso rainama Ammar hankali, Jalal ne ke zuwa ya musu shegen duka, hakan yasa suka daina tsokanar Ammar.

   A b'angaren Fatima kam tana shiga gidansu Isma'il sosai sai dai a randa tasan yanada aure harda 'ya'ya ranar tasha kuka harda zazzab'inta, yanzu Fatima ta kile sosai d'an inba fad'ama akai ba bazaka tab'a cewa 'yar kauye bace.

   Samari kuwa dake santa a k'aueyen nan yawa garesu, sai dai ita zuciyarta nakan Isma'il, ta kasa tsayawa da wani sam.

   Kamar yanda ta saba yau asabar ta gama duk ayukanta, tace " Hajiya zan fita."

  Hajiya tace " Fatima jiya da daddare sai nawa Abdul ya shigo?"

  Fatima ta kalli Hajiya tace " Hajiya wlh bansani ba nidai harnai bacci banji motsin bud'e kofa ba, amma ai dama yace Campain yakeyi."

  Hajiya tai shiru tace " wani campain me da daddaren Allah? Keda kin yarda? So yake yaja min zagi dama mutane nacemasa d'an mace tunda mahaifinsa ya rasu da daddewa."

  Fatima ta matso kusa da Hajiya tace " Hajiya Allah ya gani kinayin daidai kokarinki ga matsalar kafar da kike fama da ita sannan ni fa hajiya? Kinsan iyayena sun rasu tun ina karama agun kanwar mahaifina na taso."

  Hajiya tai murmushi tace " jeki ko ba gun karatu zaki ba?"

Mik'ewa tai tana murmushi ta mata sallama ta fita, Hajiyar Abdul ta bita da kallon k'auna.

  Tazo fita taji an cafko hannunta, ko bata juyaba tasan waye hakan yasa ta dage ta fizge hannunta da karfi, Abdul haushi ya kamashi, yana takaicin yanda take nunamai kamar tana kyamarsa, sa hannu yau ya fizgota ya matseta jikin bango, ta d'ago tare da had'e rai, Abdul ya kalleta ya saki wani mugun murmushi yace "Fatima na yanke hukuncin muyi aure kawai."
  Batasan sanda ta bugamai wata harara ba, batai auni ba taji ya kifa mata mari yace " ni kike harara? Ko kin manta ni waye?"

  Kasa tai da kai tare da rik'e gun, ya saketa yace " ankusa nad'ani Chairman a garin nan, in har mai aikin gidanmu bata bani girma ba wa zai bani?"

  Ta kalleshi a ranta tace " tir da wannan mik'amin da ake shirin ba ka." Ya saketa tare da shiga ciki, cikin takaici itama ta wuce waje.

  Abdul na shiga ya gaida hajiya tare da cewa " Umma nikam aure nakeso."

Kallansa tai cikin mamaki da kuma murna tace  " wa kakeso Abdul? Naji dad'i?"

Ya d'an sosa k'eya yace " ni Fatima zaki auramin."

  Murmushin fuskarta ne ya fad'ad'a tace " Da gaske Abdul?"
Yai murmushi yace " sosai ma, amma d'an Allah Umma tunda yarinyar nan a gunki take kuma anan gidan zata zauna asa auren nan da sati 2."

  Dariya ta saki tace " Abdul matsuwar ta menene haka?"
Yace " ni kawai so nake ayi nan kusa."

Shiru tai lalai dole ta yarda ai nan kusa, d'an tasan inka ga namiji ya matsu da aure sosai to gwara amai kafin abin kunya ya ratsu ciki.

Tace to naji jeka.

Nan ya mik'e tare da Murmushin mugunta, d'an shikam kullum da sha'awar ta yake kwana.

  Fatima kam tana fitowa a waje kan dakali taga Jafar da Ammar, ta matsa tare da cewa " Me kukeyi a nan?"

Jafar ya kalleta yace " a zaune kawai muke."

Fatima tai murmushi tace " ku bakwa wasa irin na yara?"

Jafar ya kalli Ammar yace " yaran ne 'yan rainin hankali, munfisan muyi wasanmu mu biyu."

Tace " Ammar ina Babanka?"

Yace ya fita, tai murmushi tad'auko naira goma a jakarta tace " ungo kusai alawa."
  Jafar ya kalleta yace " mun gode amma bazamu ansa ba."

Ta kalleshi sannan tace "Ammar kaifa?" Kallan Jalal yai yace "a'a mun gode. "

  Ta d'an yi kasa dakai alamar rashin jin dad'i sukam sauka su kai suka shiga gidan da gudu.

A hankali take tafiya, samarin garin kowa na sha'awar yanda take da hankali ga kyau, harta isa makaranta, ta tadda Isma'il a zaune, ta gaidashi ya kalleta cikin kulawa yace " yau kin d'an dad'e Allah yasa lafiya."

  Ido ta kuramai kamar batasan me yake cewa ba, ganin yanda take kallansa yasa yai murmushi yace "da alama kunyar fulani tabar jikinki."

  Da sauri ta d'auke ido tace " Malam duk kunyata?"
"Hmm a da ba? Yanzu naga harkin fara kurama mutane ido."
Ta had'e rai tace " kaine mutane?"

Yai murmushi ya wayance da cewa " matso muyi sauri matata batajin dad'i."

Had'e rai sosai Fatima tai dama yasani, shikuma harga zuciyarsa yasan yanasanta sosai, sai dai yasani bazata iya auransa ba, ga 'ya'yan masu kud'i na santa samari, ina zai so abinda yake neman fin karfinsa?shiyasa yakesan itama ta daina sanshi.

Mik'ewa tai cikin tsananin kunar rai ba tace mai komai ba tai hanyar waje.

Isma'il ya kalleta yace " nayi zuwan banza kenan?"
  Tsayawa tai cak batare da ta juyoba idanunta na zubar da kwalla, mai yasa zuciyarta bata iya b'oye so ba? 

  Haka ta juya sukai karatun ba dad'i.


  Tana dawowa gida Hajiya tasanar da ita zancen aurensu da Abdul,  cikin mamaki ta kalleta tace " ni kuka Hajiya? Mai zai yi dani 'yar kauye?"

Hajiya tace " Fatima kitaimakeni bad'an shi ba d'an ni ayi auren nan,wannan shine buri na d'aya da ya rage min a duniya, d'azu na k'ra kanwar Babanki bakiga murnar datai ba."

  Fatima ta d'ago a ranta tace tayi murna mana tunda taji zan auri mai kudi.

  Murmushin yake Fatima tai mata sannan ta mik'e ta shiga d'an d'akinta, tana isa ta fad'a gado kuka sosai ta shiga yi, meyasa ba wanda zai tambayeta ko akwai wanda takeso? Tasani da mahaifanta nada rai dasai sun tambayeta ko tanaso, ta dad'e tana kuka kafin ganin ba mai lalashi ta mik'e.

   Isma'il kam ya dawo yana shiga d'aki, ya tadda Samira a zaune, ya shiga shima ya zauna, tamai sannu da zuwa tare da cewa" dagaske kaima kanacikin jerin masu san Fatima?"

  Da mamaki ya kalleta yace " me kike fad'a haka?"

Ta juyarda kai tace " d'azu na fita gunsu Hajiya naji wani saurayi yazo kawo musu kara wai kana santa duk asabar da lahadi sai kun had'u a makaranta kunyi zance."

  Ya mik'e tsaye yace " kuma sai kika yarda da zancen nakejan yarinya zuwa makaranta inayi?"

Juya kai ta sakeyi hakan yasa ya gane wato ta yardan kenan, a zuciye ya fito waje,  Hajiya ya gani dasu Goggo suma suna maida zancen, kallansu yai cikin takaicin abinda kowake fad'a zaiyi magana sai ga Jafar ya shigo, ya kalli Isma'il yace " Dad wai ana magana dakai."

  Yace " Jafar inji wa?"

Yace " Abba nane."

Tare suka juya sukai waje, bayan sun gaisa da Amadu ne yace " Amadu ya akai?"

  Amadu yai shiru can yace " haryanzu kana koyama Fatima karatu ne?"

Kai ya gyad'a alamar eh, Amadu ya dafa kafad'arsa yace "kayi hakuri ka rabu da yarinyar nan, nasan ka sosai Isma'il nasan kuma kana santa, wani karatu kake koyamata har shekara 5?"

  Yai ajiyar zuciya sannan ya cigaba " kaga d'azu a shago naji ana gulmarka, sannan naji ma yarinyar yaron gidan zata aura, Isma'il ka hakura kasan Abdul wanda za'aba Chairman ba mutunci garesu ba su da abokansa."

  Isma'il zuciyarshi ta tab'u dajin wai anmata miji, ya d'aure yace " nagode Amadu, insha Allah kuma mungama karatun."

  Tun daga wannan rana bata sake sa Isma'il a idanunta ba, zuciyarta takasa hakura da rashinshi, wani sa'in har gidan take zuwa sai dai kowa taga ya daina sakar mata fuska, ga abin takaici shirye-shiryen bikinsu kawai sukeyi ba wanda ya damu da halin da take ciki.




   Isma'il kam shima komai nasa ya canza bai fiya magana ma sosai ba, duk 'yan gidan hatta Samira sun fahimci yanasan Fatima sosai, sai dai yaza'ayi?

  Abdul kam abokansa sai dariya sukemai wai zai auri 'yar kauye, yace " nimafa bawai d'an inzauna da ita d'ind'ind'in nakesan auranta ba, d'an kawai in kauda kwad'ayi nane, dariya suka kwashe dashi sukace " in wannan ne ba kawai sai ka....."
  Shidai kam zuciyarshi batasan wannan kawai....d'in.

  Yau saura kwana 2 biki, d'anginsu Fatima sun cika gida, itakam kallan kowa take a baibai, sai dai ba yanda zatai, duk ta rame ta canza.

  Dad nakawo nan yai shiru tare da kallan Seemah dake zubar da kwalla kamar an bud'e famfo, Ammar ma hawaye ke zubar mai, ya kalli Habib shima haka.

  Yai shiru can yace " Ana saura kwana 2 auranta ne Ammar yazo ina zaune kusa da Samira da ba lafiya ya sanar dani wai matar nan ta gidan nan, tace d'an Allah tanasan ganina a shagon Abban Jafar. "

  Samira dake kwance ba lafiya na kalla, na share maganar tare da kallan matata, Samira ta juyamin baya tana zubar da kwalla, tausayinta dana kaina ya kamani hakan yasa na watsar da maganar Fatima nasan ganina.

   A b'angaren Fatima kam tun karfe 2 tazo gefen shagon take tsaye, har la'asar, Amadu tausayinta ya kamashi yace " Fatima anya zaizo kuwa?"

  Ga mamakinsa murmushi yaga tayi tace " zaizo."

  Anan shagon ta la'asar Amadu yabata biscuit da lemo, duk da yunwar datakeji taki amsa, duk k'iran da Amadu yake makama Isma'il a waya sai ace wayar a kashe, ga magrib ta duso, Jalal ne yazo gunsa, yace " yauwa Jalal zauna ka taya Aunty hira bari naje gidansu Ammar in dawo."



_Dad ya kallesu tare da matse kwallar sa_


  Yace " Seemah bansan meya faru ba, nidai Amadu yazo mukai sallar magrib a massallaci tare muna fitowa yasanar dani komai, da sauri muka nufi shagon ni dashi.

  Sai dai me? Shagon muka gani kamar ba kowa, hakan yasa na shiga ciki da sauri shi kuma ya zagaya, ina shiga na tadda Fatima tsirara ba kaya a kwance, kamar ma ta ruga ta suma, kana ganinta kasan ta karfi aka mata, na matsa da sauri na tallabota idanuna a rufe na riko zaninta na lil'iba mata, Amadu ya leko cikin tsoron abinda ya faru ya zube agun, nikam rungumeta nai na shiga wani irin kuka mai ban tausayi, ban farga ba naji mutane a waje ana hayaniya.

   _Dad ya share kwallarsa_
_Seemah kam kukanta ya tsananta anan_

  Amadu ne ya kallan yace " yi sauri ka fito da ita samarin garin nan ne bansan wa ya k'irasu ba."

  Na d'agota tare da nad'a mata zani, ina fitowa aka fara jifansa da dutse, ganin zasu sameta yasa na juya sukai ta dukana, wani daga cikinsu ma bamusani ba ashe yasa kalanzir kawai sai ashana mukaga an kyasta, haka na d'aureta abayana dakyar mukasha zuwa gida.



   Sai dai me? Bala'in dana tarar a gida a wuce nacan, Hajiya harta suma, Samira ma ciwonta ya tashi, sai numfashi kawai takeyi, tana ganina d'aure da Fatima kawai tayi baya luuuu, abinda ya firgitani agun tace ga garinku nan.

   Kuka ma rahama ne, a wannan ranar hawaye ma kasa zubomin sukai, Kawo da jama'ar gurin suka had'u aka fara zancen yima Samira wanka, nan Kawu ya kalli Amadu a tsakiyar mutane yace " Amadu ka tabbatar da abinda ka fad'a cewar Isma'il shiya mata fyad'e?"

   Da mamaki na kallesu ni kuma? Abinda ban tab'a zataba sai jinai Amadu yace wai eh, ya ganni da idanunsa.

   Kuka sosai kawu yai, kowa ya shiga ala wadai dani, Abdul ya koma gida cikin taron jama'ar biki yace " bazai aure Fatima ba, d'an ankamata da wani a shago."

  Tsinuwa kuka nashata, wani abin takaicin Fatima data farfado, sai kuma ba baki, ta kasa magana, duk yanda taso tai magana ta kasa, anan aka fara jifana akan lalai kafi namata da alama ma abu nasa na danne bakinta, yunk'urin ihun dataitayi yasa muryarta ta tafi.



    Dad ya kallesu hawayensa sun tsanan ta yace ban tab'a ganin bala'i kiri kiri irinta wannan ranar ba, kowa ya gujeni, A lokacin na ba Fatima takarda akan ta rubuta min sunan wanda yamata fyad'e, tana kok'arin rubutamin, Tayi baya luuu, bakinciki harya gama cin jikinta, haka na kaita asibiti aka bata gado, sai dai kamar ba rayayyiya ba, tana kwance ne kawai sai numfashi, d'anginta suka sallamata aka watse da ala tir.

   Fatima na asibiti har wata 2, Kawu da Hajiya sunyi sunyi inrabu da ita sai dai gani nake in na kyaleta mutuwa zatai d'an bakin ciki, alokacin ne kuma akace tanada ciki.

  Ganin zaman garin na neman gagararmu yasa muka dawo Suleja, anan ne har Fatima ta kawo watan haihuwa, tana haihuwa tace ga garinku, Hajiya kam da Kawu sun ma dainamin magana sam, yaya ma duk yanda yaso da in rabu da Fatima sai dai na kasa, haka na zauna agun gawar naita kuka kafin aje amata sitira.


Dad na zuwa nan yakasa magana Seemah kam jitai kanta na juyawa Ammar ya matso kusa da ita yace " Seemah, in ihu ne kiyi amma karki had'iye komai a ranki."

  Kallansa tai kawai tai baya luuuuuu, Habib ma kuka yake sosai, Dad ya mik'e dasauri ya d'auketa yai waje da ita.



  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

Thursday, 19 January 2017

JALALUDEEN 47

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 4⃣7⃣


   Fatima na shiga gidan ta ga mutane a zazaune anata murna, idanu suka had'a da Isma'il, jitai ance " Baiwar Allah lafiya kika shigo ba sallama?"

  D'auke idanta tai daga kansa tai saurin cewa Salamu Alikum, dariya suka sa mata Hajiya tace " daga ina kike?"

  Fatima tad'an saci kalan Isma'il sannan ta nuna da d'an yatsarta tace daga nan gidan, Goggo(uwar gidan Kawu) tace shigo ki zauna nasan kukan yaro kikaji shiyasa kika shigo ko? Kallan yaran tai a hannun ta murmushi ta saki sannan ta karasa tare da gaishesu, suka amsa goggo ta mik'a mata d'an, Kuramai ido Fatima tai tana san yara itakam, a hankali ta d'ago tad'an kalli Isma'il ga mamakinta shima idanunsa na kanta da sauri tai kasa da ido tace " Allah ya raya." Sukace Amin.

  Goggo tace " Isma'il ko zaka dubo mai kazar ko ya fito, naga tun d'azu mahaifinka bai dawo ba, ga shi ya kamata ama mai jego farfesu."

   Isma'il yace " bari naje."

Ji sukai Fatima tace " bari ni naje nasan gurin."

Hajiya takalleta fuskarta da fara'a tace " keda kikazo barka, ya za'ai musaki aiki sannan ga magriba ta kawo kai."

  Isma'il ya mik'e tare da cewa bari naje.

  Yana fita, Fatima tace " bari naje gida zan dawo gobe." Nan suka mata sallama ta fito da sauri.

  Can taganshi har yayi nisa, da sauri ta shiga binsa har da had'awa da gudu, tai sa'a ta kusa isa gunsa, a hankali tace " Malam." Ga mamakinta gani tai ya juyo d'an batai tunanin zai jita ba.

  Tsaya tai tana hakki, Isma'il ya matso kusa da ita yace " yana ganki anan?"

  Cikin hakki tace " biyoka nai."

Kallanta yai da mamaki yace " abu kikesan fad'amin?" Kai ta gyad'a sannan tace " Malam alfarma da taimako nakesan kamin."

  Isma'il ya kalleta yace " namefa?"

  Tai shiru tare dayin kasa dakai, ya kara kallanta yace " ke nake jira."
Tana wasa da 'yan yatsun hannunta tace " Karatu nakesan ka koyamin."

  Dariya Isma'il yasa yace " in kinasan karatu sai kice a saki a makaranta."

  Tai kasa dakai tace " ni na islamiya nakeso, kullum Hajiya sai tace in tashi inyi sallah nikuma a garinmu sai mutum yayi aure yakeyin sallah to in ina kula da yanda takeyi sai inga tana motsa baki amma bansan me take cewa ba, shine nakeso ka koyamin na islamiya insan yanda ake sallah."

  Kallanta yai cikin tausayawa, gata dai 'yar kauye mara ilimi sai dai komai nata na birgeshi, da wani ne haka zai karashi rayuwarsa ba tare dayace a koyamai ba."

   Yaja dogon numfashi yace " yanzu kije gida gobe kisame ni da yamma a kofar gida, sai insan yanda zamuyi karatun."

  Murmushi ta saki tace " nagode Malam. "

Tanakainan ta juya ta fara tafiya, kallo ya bita dashi ya shagala yana kallanta yaji an dafa kafad'arsa, ya juyo a zabure Amadu ne ya kalli inda Isma'il yake kallo yace " kasanta ne?"

  Isma'il yai saurin wayancewa yace " wa?"
" wacce kake kallo mana."
" ni kaga ina kallan wata? Kawo nake lek'awa munjishi shiru tun d'azu daya fita siyo kaza." Isma'il yai maganar yana waige-waige.

Amadu yace " Niba wannan ba gurinka fa zanje yanzu."

" haba? To gani Allah yasa lafiya."

Amadu yasa dariya yace " Habiba ta sauka d'azu da rana na k'ira wayarka bansamu ba shiyasa na yanke hukuncin zuwa gunka."

  Fara'ar Isma'il ce ta k'aru yace " kai haba? Amma naji dad'i, nima yanzun nan Samira ta sauka, oh ikon Allah kaga sun haihu a rana d'aya."

  Amadu ma fara'ar fuskarsa ya fad'ad'a yace " ikon Allah meta samu?"
"Namiji."
"Nima Namiji. "
A tare suka sa dariya tare da rike hannu Amadu yace " lalai wad'annan Aminai zasu zama da alama."

  Nan Amadu ya raka Isma'il gun mai kaza anan suka tadda kawo, sun siya suka taho tare kawo na tayasu murna yace " Lalai naji dad'i Allah ya kare mana su." Amin suka fad'a a tare.

  Har gida Amadu ya rakasu, nan matan kawu suma sukai ta tayashi murna, ya d'auki d'an cikin farinciki yace " Isma'il tunda mun haihu a tare sai muyi canje, ni zan rad'ama d'anka suna kaima sai ka rad'ama nawa."

   Duk suka kwashe da dariya kowa ya shiga cewa lalai hakan yayi.

  Amadu ne ya rad'ama Ammar suna na gaskiya sunan mahaifin Amadu wato Kabir sai yasamau sunan daza'adinga cemai Ammar.

  Shima Isma'il da kansa yaje gidan ya rad'ama yaron Jalaludeen saboda sunan dayasu rad'ama Ammar kenan.

  Murna agun mutane ba'a magana saboda kowa yasan amintar dake tsakanin Amadu da Isma'il.

  Washegari da yamma yana zaune a dakalin kofar gidan Fatima ta fito, cikin tafiyarya mai nutsuwa, tana ganinshi tai kasa dakai tana murmushi, Isma'il ya shiga kallanta harta karaso gurin, ta gaidashi a hankali, shima ya amsa tare da cewa " na d'auka kin fasa koyar karatun ganin kin dad'e baki fito ba." Yai maganar cikin zolaya, abinka da rashin wayau sai tace " bayan yanzu kazo tun d'azu nake lekowa bana ganinka."

   Dariya yai yace " ashe da gaske takesan koyan karatun."

  Kasa tai dakai tana wasa da 'yan yatsun hannunta, Isma'il yace na yanke shawara, duk ranar asabar da lahadi shine bani da makaranta da safe, wajen karfe 11 sai ki d'inga zuwa islamiya ina koya miki zuwa karfe 1, kinga karfe 2 ne ake fara karatu."

  Kai ta d'aga tace to "Malam na gode, amma wannan yaron d'anka ne?"
   Isma'il ya kalleta da mamakin tambayarta, yace " meyasa kikesan sani."

D'agowa tai a hankali ta kalleshi batace komai ba ta maida kanta kasa tare da cewa " sai ranar asabar d'in."

  Ya amsa da "Allah ya kaimu."

Ta juya tai ciki, kallanta yai tare da murmushi.

  Itakam tana shiga ta d'au tsintsiya ta hau shara ba gaira ba dalili bayan gun a gyare yake tas, shara take Hajiyar Abdul na zaune taji karar tsintsiya ta mik'e tare da fitowa, Fatima tagani tanata zabga shara zatai magana taji muryar Abdul yace " Faty Shara kikeyi ne?"

  Kallansa tai ta kaida kanra kan shara, itakam zuciyarta batasan ace d'an Isma'il ne d'an ita tanada mugun kishi shiyasa bazata iya auren mai mata ba, zuciyarta tace anya kuwa kamar malam zai rasa mata?"

  Jitai Abdul ya dafata yace " meke damunki haka?"

Ta d'ago tace " d'an Allah ina rokonka kadaina tab'ani in zakamin magana."

  Ga mamakinta jitai yace " Sorry na daina."

D'agowa tai tana mai kallan mamaki tace " ina abokan naka?"

Yai dariya yace " suna gidansu."

Tai kasa dakai tare dad'an tab'e baki a ranta tace " da walaki, d'an dama inshi kad'ai ne zakaga yanada saukin kai kuma bashi da rashin mutunci, anma da zarar sun had'u da abokansa shi kenan kuma sai rashin mutunci ta ko ina."

   Kallanta ya tsaya yanayi tana shara, sai murmushi yakeyi, Hajiya dake tsaye tana kallansu tai murmushi itama, da alama Fatima ce zata sa d'anta ya shiryu d'an wannan shine addu'arta yaran maraya ne bashida uba, sai dai yabiyema kawayen banza sun canza mai halaye.






*THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

Tuesday, 17 January 2017

JALALUDEEN 46

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 4⃣6⃣

  Zahra ta taimaka mata tasaka kaya, hannunta ta kama suka fito falo.

  A falo kuwa Dad na zaune a saman kujera yayi shiru zuciyarshi na cikin damuwa, mami na zaune daga can b'angaren itama, Habib kuma da Ammar suna zaune a kasa, Zahra ce ta fito rik'e da hannun Seemah ta zaunar da ita a kasa kusa da Dad, hannu Dad yasa ya shafi kanta.

  Kamar ba Seemah ba sam ta canza ga lab'anta duk sun bushi gwanin tausayi, Ammar ma ya kalleta tausayinta na k'ara ratsa gab'obin jikinsa.

  Dad ne ya d'aure yai gyaran murya.

  *TUNA BAYA*


  Malam Isma'il wato Dad kenan, ya kasance malamin makarantar boko ne, a garin Birnin/gwari dake kaduna, yana zaune a jikin gidan mahaifinsa ne saboda rashin hali, gashi anyi sa'a dama gidan kawo gida ne babba, kawo matansa 3 ne, sai dai duk Allah bai basu haihuwa ba sai akan mahaifiyarsu Isma'il.

  Hajiya 'yaranta biyu wato Dad da Abba (Abubakar) anyi sa'a Abba tun yana saurayi ya samu wani babban mutum d'an kasuwa a garinsu yake d'aukansa suna yawan kasuwancinsu tare, ganin kwazo dasan aiki irin na Abba yasa ya aura masa 'yar sa wato Mamie(Bilkisu) sannan ya d'aurashi akan harkokin business d'insa dake Abuja, tun daga nan ya koma can da zama.

  Dad an masa auren zumunci da mahaifiyarsu Habib wato Samira, duk da baso yakeyi ba sai dai a lokacin bashida wacce yake so kuma zab'in iyayensa shine zab'insa, bayan auransu ne Kawo ya basu b'angare d'aya suka zauna a gidan.

  A kwana a tashi har Samira ta haifi d'anta Habib, sannan ta sake haihuwar Junaid sai dai akwai ra ta a tsakaninsu, lokacin da Samira take da cikin Ammar ne ranar Isma'il ya dawo daga makaranta yaga wata bus tayi parking a mak'otansu, yarane 'yan mata su 4 suka fito daga motar, kana kallansu kasan fulanuwa ne aka kawo su irin aikin nan na aikatau.

  Isma'il ya kauda kansa tare da wucewa gidansu,  yaje daidai zai shiga yaji ance " Malam Isma'il?" Juyowa yai da fara'arsa saboda ya gane muryar, ya kalleshi yace " Amadu kaine yau a gidan namu?"

  Wanda ya k'ira da Amadun yai murmushi tare da cewa" wucewa nazo yi shine naga kamar ana sauke 'yan aiki na d'auka kaine ka d'aukarma Samira." Yai maganar cikin zolaya.

  Isma'il ya d'an kallesu caraf suka had'a ido da d'aya daga cikinsu, d'auke kai yai yace " lalai kai dai yakamata ka d'aukarma matarka."

  Sun dad'e suna hirarsu har 'yan matan suka gama shiga da kayansu suma suka shiga, Isma'il ya kalli Amadu yace " ni dama shagon ka naje na amso ma Samira kayan shayi, naga kamar wannan cikin na wahalar da ita sosai bata iya cin abinci."

  Amadu yace " Hmm nima haka nake fama da Hauwa'u inata so in tambayeka dama haka masu ciki suke shan wahala."

  Isma'il ya maida jakarsa d'aya hannun yace " A'a wlh yanayi ne dai yake zuwa kaga Samira data haifi Habibu da Junaid ai duk batasha wahalar laulayin nan ba."

  Amadu ya gyad'a kai yace " muje shagon in baka da har na kulli zance ganin Hauwa anma saboda kai zan koma."

  Suna tafe suna hirarsu har suka isa Babban Shagon Amadu ya shiga ciki ya had'omai kayan shayi, Isma'il ya bashi rabin kud'in yace sauran sai karshen wata.

Haka Isma'il ya taho yan tafe ana gaidashi saboda ganin girmansa da mutane keyi, har ya isa gida.

  Yanzun ma yazo shiga ya k'ara ganin 'yan matan sun fito sai dai ta d'azun nan tana matsar kwalla da alama kukan rabuwa sukeyi, wucewa yai ya shiga gida.

    A kwance ya tadda Samira ta kasa komai, nan ya taimaka ya had'a mata shayi ta sha, da kanshi ya shiga gyara d'akin sannan ya taimaka mata ta kwanta a kan gado.

   Ganin lokacin shiga makarantar su Habib da Junaid yayi ga kuma babban d'an Abba yasa Mamie ta ba Abba shawara akan akaisu England gun kanwarta, Abba yayi farincikin wannan shawarar ya k'ira kaninsa ya sanar dashi.

  Ba Dad ba hatta matan gidan sun tayasu murna, su Habib sai murna sukeyi sukam, bayan sati biyu da maganar Dad dakanshi yakaisu Abuja suka wuce ta can.


   Dad ya dawo daga Abuja a gajiye ya shiga gida anan ya tadda Samira ba lafiya su Hajiya da ragowar matan kawo na kanta, ya kallesu yace "Hajiya lafiya dai ko?" Hajiya tace " fita waje nak'uda ce."

  Dad ya kalli Samira yaga yanda takeshan wahala yace " Kodai akaita asibiti?"

  Hajiya tace " bakaji me nace ba?"

Jiki a sanyaye Dad ya fita ya zauna akan dakalin gidan, bai dad'e da zama ba sai gata ta dawo daga kai nik'a, a hankali cikin sanyin muryarta yaji tace " Ina wuni?"

  D'agowa Dad yai ya kalleta ranar daya fara ganinta kaya daban daban ne a jikinta gashi tayi zanen baki duk a fuskarta yanzu kuwa ba wannan shirman a fuskarta sannan kayanta tsaf,ba shakka tanada kyau sosai.
Dad yace " ina gajiya."

  Yana fad'ar haka ya kauda kai, matsowa tai kusa dashi tace " Malam menene? Naga kamar kana cikin damuwa."

  Kalanta yai da mamaki, baisan sanda yai murmushi ba yace " Ta ya akai kika sani?"

  Ta saki murmushi itama tace " kullum ina ganinka ai in na fito anma ba haka nake ganinka ba."

  Dad yai murmushi yace "a ina kike ganina?"

  Tai kasa dakai batace komai ba, yace " kije kikai aikenki kar a miki fad'a."

  Ta d'ago ta kalleshi sannan tace to, wucewa tai ta shiga gida, ya bita da kallo haka kawai yaji damuwarsa ta ragu sosai, anma ya akai yarinya karama da bata wuce shekara 18 ba tagane yana cikin damuwa?

  Yarinyar tana shiga gida ta kai markad'an sannan ta kalli matar gidan tace " Hajiya in d'an fita?"

  Ta kalleta tace " Fatima ina zaki ke kuma? Naga yamma tayi."

Tace " yanzun nan zan dawo."

  To sai kin dawo ta fad'a, da sauri Fatima ta juya ta fita, sai dai abin haushi tana zuwa taga ba kowa agun, waige waige ta fara yi sai dai bata ganshi ba, jitai anzo daidai kunenta ance " Fatima me kikeyi anan?"

  Da sauri ta juya ta kalleshi, d'an gidan da take aiki ne ko ince d'an lele, da sauri ta matsa ya kalleta sannan ya kalli abokansa jitai sun kwashe da dariya, kifkif da ido tai tace " menene?"

  D'an lelen wato Abdul yace " Abokaina kesan ganinki nace musu ankawo mana kyakyawar mai aiki shine nakeso su ganki ko zasu kyasa kamar yanda na kyasa."

  Kallansa tai da mamakin kalamansa tace " mene?"

Dariya suka kara kwashe mata dashi,  kana ganinsu kaga tantirai, Fatima kam ba abinda ta tsana irin Abdul ya shigo gida ya d'inga nanik'e mata kenan ita kuma batasan haka.

  Cikin takaicin abin yasa tai saurin shigewa gidansu Isma'il.



© *THE SEEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

Monday, 16 January 2017

JALALUDEEN 45

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

  _For you Maman Shaheed, I sincerely dedicated this page to you��thanks alot, Allah ya raya mana su Shaheed amin_

   No. 4⃣5⃣

 
   Mamie ta ja numfashi tace " Habib bazan iya baku labarin abinda ya faru ba saboda ni kaina ban san kanun labaren gaba d'aya ba sai dai zan iya sanar daku abu guda biyu zuwa uku.

   Da farko dai kamar yanda ka fad'a tabbas Isma'il ba shine mahaifin Seemah ba.

Sannan Mahaifiyarta wato Fatima fyad'e aka mata sai dai mu kanmu bamusan waye ba sai dai bayan an mata fyad'en mai shagon da akai fyad'en yace Dad ne ya mata.
  Wannan kalma d'aya daya furta yasa komai ya ruguje saboda alokacin saura kwana 2 a mata aure, alokacin wanda zai aureta ya fasa, Isma'il kuma 'yan gari suka tsaneshi har wuta aka sa a gidan Hajiya da kuma shagon da akai abin."

  Habib yace " mene?"

  Ammar kam hawaye ne kawai ke zuba daga idanunsa, me yake ji haka?
Mamie ta kallesu tace " abinda na sani kenan, bayan abin nan ya faru Fatima ta fiskanci wulakanci ta kowani b'angare har cikinta ya kawo haihuwa tana haihuwa tace ga garinku nan."

   Habib ya mik'e tare da rik'e kansa, da sauri yai hanyar kofa ya bud'e yana bud'ewa yaji mutum ya biyo kofar, da sauri ya kalli kofar Seemah ya gani ta fad'i rim, jin karar fad'uwa yasa Ammar da mamie suka juya suma.

  Habib da sauri ya tsugunna, Ammar ya taso da gudu yazo kusa da ita ya shiga jijigata yana k'iran sunanta sai dai inaaa Seemah kam ta suma.       

   Ammar ya kalli Habib idanunsa na hawaye yace " yaya kodai taji komai?" Kallan kallo sukai da Mamie, Mamie ta d'aure tace " akaita d'akin su Zahra."

Nan Ammar ya d'agata cak yai d'akinsu Zahra da ita, ya kwantar da ita, Ammar ya tsugunna a kusa da ita a rik'o hannunta idanunsa na zubar da kwalla, fita Habib yai daga d'akin d'an duk da yanajin tausayin Seemah a ransa amma yanajin haushin abinda akama mahaifinsa akan ta ta mahaifiyar.

     Seemah kam ruwa Ammar ya shafa mata a fuska, hakan yasa ta bud'e idanunta tare da jan wani dogon numfashi, Ammar ya kalleta yace " Seemah!" a cikin wani irin yanayi mai ban tausayi ta kurawa Ammar ido, alokacin abubuwan da suka faru suka shiga dawo mata.

   Da sauri ta fizge hannunta tana girgiza kai cikin kuka mai ban tausayi kawai Dad take k'ira, Ammar ganin haka yasa tausayinta yak'ara kamashi ya mik'e tare da fita falo, Dad ya k'ira.

  Daga can b'angaren Dad ya d'aga tare da cewa " Ammar ya akai?"

  Ammar yace " Dad kazo da matsala fa."

   " Matsalar me fa?"
"Dad kazo gidan Abba d'an Seemah na wani hali."

Cikin rud'ewa Dad yace " meya sami Seemar? Waya b'ata mata rai?"

  Shiru Ammar yai kafin can yace " Dad bansan me zance ba."

  Jin karar alamar sa makulli yasa ya juya da sauri ya kalli d'akin, da sauri yace " Dad kazo yanzu da matsala."

  Yana kainan ya kashe wayar tare da saurin karasawa kofar d'akin ya shiga jijigawa, jiyai ansa sakata.

  Hannu bibiyu yasa ya shiga bubuga kofar yana k'iran sunan Seemah.

  Mamie, Zahra da Zaid da sauri suka zo jin ana bubuga kofa, nan suma suka shiga k'iranta.

  Ganin ba alamar bud'ewa yasa suka tsaya jugum jugum Mamie tace " gashi babu wani makullin."

  Ammar kam haryanzu bai gaji da bubuga kofar ba, yana k'iran sunanta cikin wani irin murya.

  Sun dade agun kafin Dad ya iso da sauri yana zuwa ya kallesu yace " menene?" Shiru sukai Mamie tace "nice na fad'i abinda bai kamata ba kuma ina tunanin ta ji."

  Gaban Dad ne ya fad'i ya sa hannu zai buga kenan yaji muryar Habib yace " Zaid d'an Allah kaida Zahra kud'an bamu guri."

  Zaid ya kalli Habib cikin b'acin rai gani yake kamar rainin hankali ne hakan, a zuciye yai waje.

  Habib ya maida dubansa kan Dad yace " Dad da alama Seemah tasan komai a kanta, menene dalilin dayasa zaku b'oye wannan babban sirri ga kowa? Sannan taya za'ayi a maka sharri saboda mahaifiyarta amma ka rik'e yarinyar da ba kaine mahaifinta ba."

  Dad ya kalli Habib cikin takaicin kalamansa, kafin yai magana yaji Ammar yace " lalai ya Habib, wato kai abinda ya dameka kenan? Yarinya tana cikin d'aki Allah ne kad'ai yasan meke faruwa da ita a ciki anma kai abinda kake tunani kenan?"

  Dad ya kalli Ammar kallon jin dad'i ga kalamansa, Dad yai baya sannan ya taho da gudu ya big'e kofar, sai dai bata bud'e ba, haka sukai tayi shida Ammar har sukai sa'a kofar ta bud'e, da sauri suka shiga ciki sai dai ba kowa a d'akin, ga mamakinsu kuma karar zubar ruwa sukeji daga b'an d'aki.

  Ammar ya karasa da sauri tare da bubuga kofar toilet d'in.

  Seemah kam tana cikin bathroom ta tsugunna a cikin ta saki shaya, ga bata cire kayan jikinta ba, ga ruwan sanyi ta sakar ma kanta, hakan yasa ruwa duk ya jikata jakaf, sai dai ko damuwa batai da jikinta ba kawai kuka takeyi, gani take wannan itace hanyar da ya dace da ita, ita kad'aice hanyar dazatasa takasa gane yawan hawayen datake zubarwa.

  Kuka sosai takeyi sai dai ruwan dake zuba jikinta yasa baza'a gane ba.

  Dad ya matsa jikin kofar ya shiga k'iran sunanta, tana jin muryarsa ta mik'e jikinta na rawar sanyi, sai dai bata bud'e ba, Dad ya shiga lalashinta, can cikin lallashi yace " fito Seemah inhar kika fito zan fad'a miki duk abinda ya faru a baya, na miki wannan alk'awarin."

  Jin wannan kalaman yasa ta bud'e kofar a hankali, kofar tana bud'uwa Dad da Ammar sukai saurin shiga ciki, kallanta Ammar yai hawaye na zubo mai, kanta ya kalla sannan ya kalli yanda jikinta ke d'iga da ruwa, dukansu har Habib sai da sukaji tausayinta ya kamasu sosai.

  A hankali sukaji tace " Dad kafad'amin abinda naji ba gaskiya bane, ka fad'amin kaine mahaifina, ka fad'amin gaskiya d'an Allah."

  Dad ya share hawayensa ya matso ya rungumeta yana hawaye sosai, yace " Seemah ki kwantar da hankalinki."

  Kai ta girgiza tace " Na fahimta dagaske ba kaine mahaifina ba kenan, mahaifiyata karuwa ce, tsintata akai?"

  Kallanta Habib yai cikin tausayi da alama bataji komai ba kenan, Dad ya d'ago tare da share nata hawaye yace ki canza kaya Seemah zan fad'amiki komai, amma ko kusa Fatima ba karuwa bace, ba kuma tsintarki nai ba."

  Kallansa tai ta kasa yin komai, sai hawaye da suke tsere a idanunta, Mamie ta kwallama Zahra ido, tana zuwa tace " taimaka mata ta canza kaya."

  Dad ya kalleta yace " ki shirya ki fito fallo zan sanar dake komai."

  


  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*


��‍♀