Tuesday, 10 January 2017

JALALUDEEN 39

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   No. 3⃣9⃣

  Habib ya matsa kusa da kawo ya tsugunna agabansa idanunsa sunyi jaaa yace " kawo meke faruwa wai? Nine babban d'a agun mahaifina meyasa zaku d'inga b'oyemin abu? Gaba d'aya kun birkita min lissafi ance ba mahaifiyarmu d'aya da seemah ba? Dad yazo yace wai Ammar ba d'ansa bane, yanzu kuma Hajiya tana maganar ba'asan mahaifinta ba, in maganar mace takeyi da Seemah kenan take, gaba d'aya na kasa fahimtar abinda ke faruwa."

   Kawo yai kasa dakai yace " Habibullah maganar da ake b'oyema........"
Amman da Hajiya ta shiga kwarawa ne yasa maganar ta tsaya, gaba d'ayansu suka mik'e suka nufi gun, hajiya amai takeyi sai dai da alama ba komai a cikin ganin yanda take kak'aro aman, Habib da sauri ya d'agowa yace kawo tayani mu kaita mota, nan suka d'auketa d'an ta galabaita sukai mota da ita, kawo ya zuba musu kaya a jaka suka ja gida suka rufe suka shiga mota.

  A hanya ba wanda yai magana d'an Hajiya numfashi kawai take saki.

  Dad kuwa harya kusa fita daga birnin/gwari wata magana ta Hajiya datamai randa yaje ta fad'o mai, lokacin har yaje fita daga gidan yaji muryar ta tace " Isma'il kasan ma mahaifin yarinyar ne? Itadai bazata tab'a yarda da yarinyar da ba'asan mahaifinta ba."

  Tunano kalaman ne da Dad yai yasa ya kalli drivern sa yace mukoma inda muka fito nayi mantuwa.

  Nan driver ya juya da kan mota suka koma, Dad sai tunanin abinda yafaru a baya yakeyi, bai tab'a tunanin zai had'u da Amadu ba, abinda yafi d'aure masa kai wai Jalal d'in da Seemah takeso d'ansa ne.

  Ya zarfafa cikin tunani bai san ma harsun iso ba, sai da driver d'in yace " Alhaji mun iso. " lungun gidan Dad ya kalla ransa na kara tunzura d'an bakin ciki, haka ya daure ya fito daga mota ya nufi gidan.

  Abba kam tun bayan tafiya Dad ya zauna a waje shi da umma sai dai ba wanda ya iya yima wani magana a cikinsu, sai can Umma ta daure tace " Malam ne dana mahaifin yarinyar da Jalal keso?" Abba ya had'iyi wani abun bai iya ce mata komai ba, tacigaba " mun shiga uku malam yanzu in Jalal yasan..........wani kallo da Abba ya buga mata ne yasa tai shiru, sai dai abinda ke zuciyoyinsu na da yawa.

  Jin an kwankwasa kofa ne yasa Umma ta d'aure ta mik'e ta nufi kofar, ta bud'e ganin mutumin dake tsaye ne yasa ta fara ja da baya da baya, tare da cewa Malam? Abba dake zauna ya taso tare da cewa "ke kuma menene inaji da......" ganin Dad ne yasa shi yin shiru,  Dad ya makamai wani mugun kallo yace " inasan ganinka." Yana fad'ar haka ya juya.

  Abba ya kalli Umma itama cikin tsoro tace " Malam mun shiga uku." Takalmansa ya d'auko ya fita sai dai kana ganinsa kasan ta maza kawai yakeyi anma a tsorace yake.

  A d'an gaba da gidansa yaga Dad ya karasa gunsa, yace " Isma'il gani." Juyowa Dad yai ya kalleshi cikin d'aure fuska yace " tambaya ta karshe nazo in maka, daga wannan in har ka sake min karya wlh kaji na rantsema wannan karan ba kamar da bane dazan kyaleka, wlh sai nasa an d'aureka."


Abba ya kalleshi a tsorace, Dad yace " Wayama Fatima fyad'e?"

  Gaban Abba ne ya fad'i ya kalli Dad sannan ya had'iyi yawo bakinsa na rawa yace "Malam  Isma'il!"

Dad ya d'agamai hannu yace ba abinda nazo ji kenan ba, ka fad'amin abinda na tambayeka ko kuma wlh zakasha mamaki.

  Abba yace " Malam Isma'il alokacin wlh ba asan raina......"

  Dariya sosai Dad yai sai dai kana gani kasan ta tsabar bakin ciki ne, yace " Amadu kenan, karka sake tunanin zan yanda da kalamanka, kalma d'aya nakesan ji daga gareka, waye ya k'etama Fatima mutuncin ta?"

  Abba ya kalleshi idanu a zare, Dad ya karkatar da kai yace " Don't tell me kaine?" Da sauri Abba yace " Me kake fad'a? Ni kuma? Akan me? Kaima kasan ba hali na bane."

Dad yai murmushi yace "a shekaru masu yawa kenan nai tunanin ba halinka bane amma daga baya na gane babu babban munafikin dana tab'a gani irinka, sannan dama na sanar dakai wannan shine tambaya dazan maka ta karshe, yanzu sai ka jira d'anka d'an inaji shi kad'aine zai iya jin amsarka."

  Dad nakainan ya juya ya tafi, Abba ya rikice, sai dai kafin ya dawo hayyacinsa Dad har yayi gaba.

  Da sauri ya koma gida ya tadda Umma a tsaye tana jeka ka dawo, tana ganinshi ta rike hannayensa tace " ya kukai?" Abba yace " ya tafi yace Jalal zai fad'ama."

  Zubewa Umma tai a kasa jin haka tace " Malam meke damunka? Kataba tunanin in Jalal yaji maganar nan abinda zai yi?" Ta mik'e tace "Ko dai nima kana b'oyemin wani abu ne? Indai har abinda ka fad'amin shine gaskiya meyasa bazaka fad'ama Malam Isma'il ba? Karka manta abinda ya faru da shi da iyalinsa saboda kalma d'aya daka furta."

   Abba ya kasa magana sai zufa kawai yakeyi, ya kalleta yace " Ban b'oye miki komai ba, kema kinsan haka." Yana kainan yai waje da Sauri....





© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM.*

��‍♀

No comments:

Post a Comment