Thursday, 12 January 2017

JALALUDEEN 42

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

_This page is for you my Yar uwas, my cwty my chocolates, much luv to you�� Maijiddah_

ayushermohd.blogspot.com

   No. 4⃣2⃣

    Seemah kam gaba d'aya kanta taji yana wainawa, bata fahimci inda maganar ta dosa ba saboda ta baro gun Jalal tazo zata shiga ta tuna d'azu ance ta fita, hakan yasa ta jingina da kofar sai dai adaidai lokacin taji Hajiya tace " Kuma duk abinda ya faru dakai Isma'il kuma ka rike yarinyar nan Amana."

  A iya saninta mahaifinta ne Isma'il to wace yarinya ya rik'e amana?

  Dawowar Habib da likita ne yasa itama ta mik'e ta wuceta sukai da sauri, tabishu da kallo tare da tsayawa a bakin kofar, Duk 'yan d'akin sun rikice ganin yanda jikin Hajiya ya tashi sosai, sai dai har yanzu hannunta kankame yake dana Dad, likita na zuwa suka shiga kok'arin daidaita numfashinta, sun wahala sosai ganin jikin ba dad'e yasa sukace kowa ya fita ya barsu, nan Dad suka fito kowa jikinshi a sanyaye, idanun kowa ka kalla kasan suna cikin tsananin tashin hankali, Dad na fitowa yaga Seemah a tsaya tana hawaye ganin yanda jikin hajiya yake, hannun ta ya kama sukai waje.

  Nan aka rufe kofar, kowa yayi jugum yana addu'oi, sai da likitocin sukai minti 30 kafin su fito, suna share zufa, Abba da Dad da kawo suna ganinsu suka matsa kusa dasu, Abba yace " ya jikin nata?"

  Likitan yace " kushiga sai dai kuyi a hankali karku kuskura kuyi abinda zai tada mata hankali ko taga abinda bataso, yin hakan babbar matsala ce, sannan kar ad'inga hayaniya a kusa da ita.

  Suna kai nan sukai gaba, Habib ya matso kusa yace " Abba ya kamata ku koma gida, munyi yawa a asibitin gudun hayaniya ya kamata ka d'auki Mami da kawo ku koma gida, shima Ammar ya d'au Seemah su tafi inyaso ni zan zauna anan."

  Abba yace " haka ne amma sai dai zuciyata bazata iya kwanciya ba in na tafi."

  Kawo yace " nima kunsan bazan iya zuwa wani gun ba inbar matata anan ba."

  Sunyi shiru kafin Dad yace " mu zauna anan ai mu ba maganar da zamuyi, kai Habib ku koma gida."

  Habib ya kalli Dad yanasan yai musu anma yana tsoro, Dad ya kalli Kawo yace "kawo kaima kaje gidan yaya kai wanka kaci abinci inyaso da daddare sai ka dawo."

     Haka suka yanke shawara Dad da Abba suka shiga ciki, Habib ya kalli Ammar yace " Ammar ka d'au mami da kawo gida."

  Mami ta kalli Seemah itakam kasan ranta tana tausayin yarinyar tace " Mu wuce da Seemah ma kwana acan, sai ta kwana gun Zara."

Seemah ta kalleta jiki a sanyayi, Mami ta d'aga mata kai tare da mata murmushi, Ammar ya kalli Seemah sannan yace "muje kawo."

  Sun fita Habib yabi bayansu da kallo, bayaji zai bar asibitin nan, juyawa yai ya shiga ciki, Dad da Abba na zaune jugum-jugum.

  Ya koma gefe ya zauna.

Jalal kam yana fita daga asibitin ya shiga k'iran wayar Abba, sai dai bai d'aga ba, hankalinsa ya tashi ya rasa me ma zaiyi ga shi gobe monday yanada aiki bare ya tafi birnin/gwari yanzu, ga yamma tayi.

  Haka ya cigaba da gwada number Abba sai can harya cire rai sannan yaji an d'aga, da sauri yace " Abba?" Jiyai ance " waye?" Da mamaki Jalal yace " ba number Abba bane?" Mutumin yace " wlh bamusan wayar waye ba d'azu muka ganta a shagon nan k'ila wani ne ya mantata."

  Jalal yace " ina ne nan d'in?"
  Mutumin yace " gurin buga kati ne."

  Gaban Jalal ya fad'i wato da gaske Abba yake? Ya d'aure yace " ku ajiye wayar zan k'ira azo a amsa."

  Nan sukai sallama, Jalal ya k'ira number Umma, sai data kusa katsewa ta d'aga tare da Sallama, Jalal ya amsa tare da cewa " Umma d'am Allah Abba fa?"

  Tace " ya fita yanzun nan yamanta wayarshi a shagone shine yakesan yaje ya duba."

  Jalal yai ajiyar zuciya sannan yace " Umma d'an Allah kinsan wani Alhaji Isma'il?" Yai tambayar cikin sanyin murya.

  Umma kam gabanta ne yashiga dukan uku-uku, tace " Jalal anya kuwa?"

  Yad'an jinjina kai sannan yace " maybe ke baki sanshi ba amma ba shakka Abba yasanshi, bakomai bari in kara neman Abba."

  Dasauri Umma tace " Jalal ba ruwanka, karka kuskura ka tambayi mahaifinka Malam Isma'il."

  Da mamakin kalamanta Jalal yace " Malam isma'il? Da alama kema kinsanshi kenan, d'an nidai a sanina Alhaji nace ba malam ba, kuma daga yanda kika fad'i sunan Umma ya nuna kinsanshi."

  Umma ta had'iyi yawo tace " Jalal ka rufamana asiri d'an Allah kabar yarinyar nan, in a da ina tunanin zai iya yiwuwa ka aureta sai dai yanzu......"

  Tana zuwa nan tai shiru idanunta suka zubo da kwalla, ganin tana alamar kuka yasa ta katse wayar tare da zana a gun, tace a filin Jalal yazamuyi? Ya Allah gani gareka!!

Abba ne ya shigo tare da kallanta yace " menene kuma?" Umma ta taso tazo kusa dashi tace " Malam ya zamuyi? Jalal fa yasan kasa Malam Isma'il."

   Abba sai da jikinsa ya amsa, ya kalli Umma kawai ya shige d'akinsa, yawo ya farayi a tsakar d'akin "Yasan Halin Jalal sosai, idan yaji abinda na  aikata ta dalilinsa bana tunanin zai tab'a yafe ma kansa."

Idanu ya runtse ya tuno laifin daya aikata saboda tsoron kar a tab'amai d'ansa, bai taba tunanin abinda ya aikata zaizo ya damesu a wannan lokacin ba, shi daga baya ma yafara tunanin ko rashin lafiya da zaheera ke fama dashi alhakin abinda ya faru ne, yasani sosai ya aikata lefi mai karfi anma ya zaiyi?



  Jalal kam wayarsa yabi da kallo mamaki kalaman Umma ne suka dameshi, lalai akwai wani abun a kasa kuma dole ne yasan menene wannan abun, tunani yafara gun Dad yakamata ya koma ko gun Abba?

  Ajiyar zuciya yai yace " Abba zaiyi wuya ya sanar dani, zan kara komawa gun Dad inji ko shi zai fad'amin." Da wannan shawarar ya shiga cikin d'akinsu.

 

© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

No comments:

Post a Comment