����������������
�� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������
Na *AYUSHER MUHD*
ayushermohd.blogspot.com
No. 4⃣7⃣
Fatima na shiga gidan ta ga mutane a zazaune anata murna, idanu suka had'a da Isma'il, jitai ance " Baiwar Allah lafiya kika shigo ba sallama?"
D'auke idanta tai daga kansa tai saurin cewa Salamu Alikum, dariya suka sa mata Hajiya tace " daga ina kike?"
Fatima tad'an saci kalan Isma'il sannan ta nuna da d'an yatsarta tace daga nan gidan, Goggo(uwar gidan Kawu) tace shigo ki zauna nasan kukan yaro kikaji shiyasa kika shigo ko? Kallan yaran tai a hannun ta murmushi ta saki sannan ta karasa tare da gaishesu, suka amsa goggo ta mik'a mata d'an, Kuramai ido Fatima tai tana san yara itakam, a hankali ta d'ago tad'an kalli Isma'il ga mamakinta shima idanunsa na kanta da sauri tai kasa da ido tace " Allah ya raya." Sukace Amin.
Goggo tace " Isma'il ko zaka dubo mai kazar ko ya fito, naga tun d'azu mahaifinka bai dawo ba, ga shi ya kamata ama mai jego farfesu."
Isma'il yace " bari naje."
Ji sukai Fatima tace " bari ni naje nasan gurin."
Hajiya takalleta fuskarta da fara'a tace " keda kikazo barka, ya za'ai musaki aiki sannan ga magriba ta kawo kai."
Isma'il ya mik'e tare da cewa bari naje.
Yana fita, Fatima tace " bari naje gida zan dawo gobe." Nan suka mata sallama ta fito da sauri.
Can taganshi har yayi nisa, da sauri ta shiga binsa har da had'awa da gudu, tai sa'a ta kusa isa gunsa, a hankali tace " Malam." Ga mamakinta gani tai ya juyo d'an batai tunanin zai jita ba.
Tsaya tai tana hakki, Isma'il ya matso kusa da ita yace " yana ganki anan?"
Cikin hakki tace " biyoka nai."
Kallanta yai da mamaki yace " abu kikesan fad'amin?" Kai ta gyad'a sannan tace " Malam alfarma da taimako nakesan kamin."
Isma'il ya kalleta yace " namefa?"
Tai shiru tare dayin kasa dakai, ya kara kallanta yace " ke nake jira."
Tana wasa da 'yan yatsun hannunta tace " Karatu nakesan ka koyamin."
Dariya Isma'il yasa yace " in kinasan karatu sai kice a saki a makaranta."
Tai kasa dakai tace " ni na islamiya nakeso, kullum Hajiya sai tace in tashi inyi sallah nikuma a garinmu sai mutum yayi aure yakeyin sallah to in ina kula da yanda takeyi sai inga tana motsa baki amma bansan me take cewa ba, shine nakeso ka koyamin na islamiya insan yanda ake sallah."
Kallanta yai cikin tausayawa, gata dai 'yar kauye mara ilimi sai dai komai nata na birgeshi, da wani ne haka zai karashi rayuwarsa ba tare dayace a koyamai ba."
Yaja dogon numfashi yace " yanzu kije gida gobe kisame ni da yamma a kofar gida, sai insan yanda zamuyi karatun."
Murmushi ta saki tace " nagode Malam. "
Tanakainan ta juya ta fara tafiya, kallo ya bita dashi ya shagala yana kallanta yaji an dafa kafad'arsa, ya juyo a zabure Amadu ne ya kalli inda Isma'il yake kallo yace " kasanta ne?"
Isma'il yai saurin wayancewa yace " wa?"
" wacce kake kallo mana."
" ni kaga ina kallan wata? Kawo nake lek'awa munjishi shiru tun d'azu daya fita siyo kaza." Isma'il yai maganar yana waige-waige.
Amadu yace " Niba wannan ba gurinka fa zanje yanzu."
" haba? To gani Allah yasa lafiya."
Amadu yasa dariya yace " Habiba ta sauka d'azu da rana na k'ira wayarka bansamu ba shiyasa na yanke hukuncin zuwa gunka."
Fara'ar Isma'il ce ta k'aru yace " kai haba? Amma naji dad'i, nima yanzun nan Samira ta sauka, oh ikon Allah kaga sun haihu a rana d'aya."
Amadu ma fara'ar fuskarsa ya fad'ad'a yace " ikon Allah meta samu?"
"Namiji."
"Nima Namiji. "
A tare suka sa dariya tare da rike hannu Amadu yace " lalai wad'annan Aminai zasu zama da alama."
Nan Amadu ya raka Isma'il gun mai kaza anan suka tadda kawo, sun siya suka taho tare kawo na tayasu murna yace " Lalai naji dad'i Allah ya kare mana su." Amin suka fad'a a tare.
Har gida Amadu ya rakasu, nan matan kawu suma sukai ta tayashi murna, ya d'auki d'an cikin farinciki yace " Isma'il tunda mun haihu a tare sai muyi canje, ni zan rad'ama d'anka suna kaima sai ka rad'ama nawa."
Duk suka kwashe da dariya kowa ya shiga cewa lalai hakan yayi.
Amadu ne ya rad'ama Ammar suna na gaskiya sunan mahaifin Amadu wato Kabir sai yasamau sunan daza'adinga cemai Ammar.
Shima Isma'il da kansa yaje gidan ya rad'ama yaron Jalaludeen saboda sunan dayasu rad'ama Ammar kenan.
Murna agun mutane ba'a magana saboda kowa yasan amintar dake tsakanin Amadu da Isma'il.
Washegari da yamma yana zaune a dakalin kofar gidan Fatima ta fito, cikin tafiyarya mai nutsuwa, tana ganinshi tai kasa dakai tana murmushi, Isma'il ya shiga kallanta harta karaso gurin, ta gaidashi a hankali, shima ya amsa tare da cewa " na d'auka kin fasa koyar karatun ganin kin dad'e baki fito ba." Yai maganar cikin zolaya, abinka da rashin wayau sai tace " bayan yanzu kazo tun d'azu nake lekowa bana ganinka."
Dariya yai yace " ashe da gaske takesan koyan karatun."
Kasa tai dakai tana wasa da 'yan yatsun hannunta, Isma'il yace na yanke shawara, duk ranar asabar da lahadi shine bani da makaranta da safe, wajen karfe 11 sai ki d'inga zuwa islamiya ina koya miki zuwa karfe 1, kinga karfe 2 ne ake fara karatu."
Kai ta d'aga tace to "Malam na gode, amma wannan yaron d'anka ne?"
Isma'il ya kalleta da mamakin tambayarta, yace " meyasa kikesan sani."
D'agowa tai a hankali ta kalleshi batace komai ba ta maida kanta kasa tare da cewa " sai ranar asabar d'in."
Ya amsa da "Allah ya kaimu."
Ta juya tai ciki, kallanta yai tare da murmushi.
Itakam tana shiga ta d'au tsintsiya ta hau shara ba gaira ba dalili bayan gun a gyare yake tas, shara take Hajiyar Abdul na zaune taji karar tsintsiya ta mik'e tare da fitowa, Fatima tagani tanata zabga shara zatai magana taji muryar Abdul yace " Faty Shara kikeyi ne?"
Kallansa tai ta kaida kanra kan shara, itakam zuciyarta batasan ace d'an Isma'il ne d'an ita tanada mugun kishi shiyasa bazata iya auren mai mata ba, zuciyarta tace anya kuwa kamar malam zai rasa mata?"
Jitai Abdul ya dafata yace " meke damunki haka?"
Ta d'ago tace " d'an Allah ina rokonka kadaina tab'ani in zakamin magana."
Ga mamakinta jitai yace " Sorry na daina."
D'agowa tai tana mai kallan mamaki tace " ina abokan naka?"
Yai dariya yace " suna gidansu."
Tai kasa dakai tare dad'an tab'e baki a ranta tace " da walaki, d'an dama inshi kad'ai ne zakaga yanada saukin kai kuma bashi da rashin mutunci, anma da zarar sun had'u da abokansa shi kenan kuma sai rashin mutunci ta ko ina."
Kallanta ya tsaya yanayi tana shara, sai murmushi yakeyi, Hajiya dake tsaye tana kallansu tai murmushi itama, da alama Fatima ce zata sa d'anta ya shiryu d'an wannan shine addu'arta yaran maraya ne bashida uba, sai dai yabiyema kawayen banza sun canza mai halaye.
*THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
��♀
No comments:
Post a Comment