����������������
�� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������
Na *AYUSHER MUHD*
ayushermohd.blogspot.com
No. 4⃣1⃣
Dad yana karasowa gun ya kalli Ammar wanda ya kauda kai, yace " me kakayi anan bayan a ciki ya kamata in ganku?"
Seemah ta matso kusa da Dad tace " Dad ni na fito dashi, kayi hakuri."
Ammar ya kalleta yace " Dad taya za'ayi ace Abba ya kore Seemah daga ciki? Ban fahimci me hakan yake nufi ba."
Da sauri Seemah tace " Dad ba wani abun bane, Ya Ammar kaya ya d'au abin da zafi ne."
Jikin Dad yai sanyi ya kalli Seemah cikin tausayinu sannan ya maida idansa kan Jalal harzai mai magana ya fasa ya juya tare da cewa Seemah muje ciki, itakam idanunta nakan Jalal shikansa kallanta yakeyi, kallan juna suke cikin wani yanayi, Ammar ya kalli yanda Seemah ke kallan Jalal jiyai ransa ya sosu, Dad ya juyo ganin Seemah batada alamar tahowa, Dad a harzuk'e yace " Seemah wuce nace ko?"
Dasauri tace " to dad." Tana juyawa Jalal yace " Dad inada magana."
Dad ya juyo ya bugamai wani kallo, ba shakka Jalal yananan kamar yanda yasanshi, sai dai yasan dabadan abinda ya faru ba yasan da amintarsu da Ammar bazata rabu ba.
Had'e rai yace " Jalaludeen sunan ka ko?"
Jalal ya d'aga kai yace " Eh, amma ban fahimci menene dalilin dayasa kaje har gidanmu kacima mahaifina mutunci ba."
Dad yace " me kace?"
Ammar ya matso yace " kai gyara bakinka wani shirman kake fad'a?"
Seemah ta kalli Jalal sannan ta kalli Dad tace "Dad kaje gidansu ne?"
Dad dake kallan Jalal yace " ka koma ka tambayi mahaifinka abinda ke faruwa bawai kazo nan kanamin shirme ba."
Jalal ya kalli Dad yace " Na d'auka maganar ni da Seemah a tsakanin mu zai tsaya amma yaza'ayi kamar kai kaje har ka shake mahaifina? Me yayi?"
Dad yai d'an wani murmushi a ransa yace " Jalal kenan bai mantashi ba halayensa nanan, tun yana karami baya shakkar tambaya."
A fili yace " bakaji amsata bane? Nace ka koma ka tambayi mahaifinka wanda a fili za'a d'auka mutumin arzik'i ne amma a zuciya" ya jijiga kai......
Ran Jalal yakai matuka gun tunzura, Seemah ta kalli Jalal ganin yanda idanunsa sukai yasa jikinta yai sanyi, Kallansa tai idanunta sun cika da kwalla, Jalal ya kalli Dad yace " ban fahimci kalamanka ba? Kasan mahaifi nane? Ko kuwa a ganinsa dakai yau shine yasa kake fad'ar haka?"
Dad ya kalleshi yace " indeed you are smart tunda har kai tunanin haka, sai ka koma ka tambayi Amadu ko ya sanni."
Amadu? Jalal ya maimaita, ba shakka wanda yasan Abba ne yake fad'a masa haka, to amma ta ya? Dad ya kalli Ammar dake jin kalamansu cike da mamaki yace " Ammar muje ko? Ina bukatar ganin Hajiyata."
Bai jira abinda Jalal zai fad'a ba yai gaba, Ammar ya bishi a baya, Seemah ta kalleshi tace " Deen meke faruwa?" Kallanta yai idanunsa a kad'e yace " Meemah I don't know, ni dai kawai ancemin Dad d'inki yaje gida har shakema Abbana wuya yayi, shiyasa nazo inji, to amma yanzu I am confused, ya akai Dad yasan Abba?"
Seemah ta kalleshi jiki a sanyaye, tace " Deen nasan Dad d'ina kwarai, duk da nasan bayasan alakarmu hakan bazai sa ya shakema Abba wuya ba, akwai dai wani abun."
Jalal ya d'ago ya kalleta jiki a sanyaye ya jinjina kai yace " karki damu kije gun mara lafiyar."
Yana kai nan ya juya, har yad'anyi nisa tace " Deen?" Tsayawa yai tare da juyowa ya kalleta ta matso kusa dashi kad'an tace " Can you promise me something? " kai yad'an langwab'ar tacigaba " can you promise me you will always love me?"
Wani sansanyar murmushi ya sakar mata ya lumshe ido sannan yace " u are my first love how can I stop loving you? "
Itama murmushi tai tace " yazanyi ind'ingajin muryarka bani da waya?"
Wayarshi ya mik'a mata tare da zare layinsa dayake amfani dashi yabar Etisalat d'in da ba wanda yasanshi dashi dama saboda browsing yake amfani dashi.
Ta kalleshi sannan ta kalli wayar tace ta meye? Yace kiyi using wannan ni nasai wata.
Murmushi tai harsai da fararan hak'oranta suka fito tace " karka damu nasan yanda zanyi inada idea."
Yad'an harareta kad'an yace a hakan? Tace zaka gani.
Tana kainan ta juya ta fara tafiya, tsayawa yai kawai yana kallanta zuciyarshi tayi wani sanyi.......
Dad kam yana shiga Abba yace " Isma'il tund'azu ina ka tsaya Hajiya na nemanka?"
Da sauri Dad ya matsa gunta, ya rik'e hannayenta, tana ganinshi ta rike hannunsa itama tace " Isma'il nasani ka ga rayuwa, kaga tashin hankali duk da dai muma mun gani a shekara 20 data wuce, sai dai abinda ka gani bai kai namu ba."
Dad ya kalleta sam yamanta da Habib da Ammar agun d'an hankalinshi nakan mahaifiyarsa, Hajiya ta cigaba" nasani haryanzu bakamanta azal d'in daya fad'a maka ba, 'yan gari sun tsaneka saboda abinda bakai kayi ba, matarka mahaifiyar 'ya'yanka wannan abin shine ajalinta, wannan dalilin yarabaka da kasarka muma dole ne yasa mukabar garin."
Tai ajiyar zuciya tare da share hawayen dake zubo mata, ba itaba hatta mamie da Dad hawaye suke, Ammar kam da Habib kallansu kawai suke mamakin kalaman nan suke.
Hajiya tasa hannu ta share mai hawayensa tace " kuma duk abinda ya faru dakai Isma'il ka rik'e yarinyar nan amana....."
Kawo ya kalleta yace " ya isa Karki kara tada ma kanki hankali ki kuma k'ara tadama d'anki."
Kallan Isma'il tai zatai magana numfashinta ya fara yankewa Dad ya rik'ece yace " a yi sauri ka k'ira Likita." Duk ya rikice Habib yai saurin fita, Yana bud'e kofa yana fita, yaga Seemah tsugunne a waje, bai kulata ba yai sauri yai gaba.
Ammar kam gaba d'aya kwakwalwarsa ta rufe, meke faruwa? Me kalaman Hajiya ke nufi? Wa aka rike? A iya saninsa 'yar Dad mace d'ayace Seemah to mekenan?
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
��♀
No comments:
Post a Comment