Saturday, 28 January 2017

JALALUDEEN 53

����������������
     �� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������




Na *AYUSHER MUHD*

ayushermohd.blogspot.com

   _*This Page is Dedicated to you ��herty�� wish u ol the best in ur Exams..... Thanks once again*_

   No. 5⃣3⃣


     Jalal jikin bango ya jingina a sulale ya tsugunna hawaye ke malala a kuncinsa, Umma dake zaune itama tana kuka ta taso ta matso kusa dashi tace Jalal! Wani irin kara yayi da duk sai da suka tsorata kuka ya wuce da shi kamar wani karamin yaro, Umma tsoro ya fara kamata ta kalli Abba tace " Meyasa ka fad'amai? Yanzu in wani abu ya sameshi fa?"

   Abba ya kalleta cikin wani yanayi, yace " daga sanda Isma'il yazo gidan nan nasan ban isa in b'oye sirrin nan ba, da wani a waje ya fad'amai mahaifinsa yaci amanar Amininsa gwara ni dakaina insanar dashi. "

  _Nikaina Ayusher yanda naga Jalal na kuka sai da naji hawaye ya zubomin a hankali nayi waje d'an bazan iya zama ba._

  A b'angaren Seemah kuwa bayan mutane sun ragune Ammar ya shigo d'akin, ya kalleta a rak'ub'e a gefen gado, tausayinta ya kara kamashi ya matso inda take tare da d'agata, kallanshi tai kamar wacce hankalinta baya jikinta tace " Ya Ammar am d'aura ko?"

  Kallanta yai idanunsa suka ciciko, hannu yasa a kafad'arta yashiga jijigata yana cewa " Get hold of your Self Seemah, please. "

  Ya d'ad'e yana jijigata kafin ta kalleshi tace " Yaya ya zanyi?"
  Yace " Seemah England zamu koma ranar bakwai inajin shi kad'ai ne zai sa ki manta komai."
   Ta d'aga kai tace " na yarda Yaya ni kaina haushin kaina nakeji."

  Nan ya mike yai waje, bai dad'e ba sai gashi ya dawo rik'e da plate na abinci, Zama yai kusa da ita tare da d'ebo abinci a cokali da niyyar ba ta, ta kalleshi sannan ta amshi cokalin tace " Zanci da kaina Oppa."

  Murmushi ya mata sannan ya mik'a mata spoon d'in, ta fara ci, yace " Matar Dad tazo ta dubaki?"
  Ta d'an tab'e baki har zatai maganar rashin kunya ta tuna ashefa ta fita matsayi yanzu, tai kasa dakai tare da cewa " Ta l'eko d'azu."
  Ammar yai d'an karamin tsaki yace " bansan ya akai Dad ya aureta ba, sam batada kara."
  Seemah tai shiru can tace " Ka manta Yaya? It is all my fault, bakaji Dad nacewa saboda ni ya aureta ba? Na sani saboda yanaso akula da......."
  Kasa karasawa tai saboda hawaye, Ammar ya kallera yai murmushi yace " Oh yazanyi da wannan kanwar tawa mai saurin kuka?"

  Ta kalleshi tare da share hawayenta tace " Yaya?"

  Yad'an rangwab'ar dakai yace " Seemah rufe idonki."
  Ta kalleshi tad'an turo baki kad'an, sannan ta rufe, hannu yasa a aljihunsa, sannan yace "bud'e."
  Da sauri ta bud'e tanasan ganin menene, kwalin waya ya mika mata, ta kalli wayar Iphone 6 ce, tace " yaya inafa da waya?"

  Yace " Dad ne yace kar abaki waccan."

  Tai murmushi sannan ta amsa tace " Thanks Bro."
  Yai murmushi shima yace " Ahhh naji dad'i kinyi murmushi, sannan kinci abinci."

  Ta kalleshi tace " saboda Deen ne ba'asan abani d'ayar wayar?"
  Ammar ya kalleta bai amsa ba, ta kara murmushu tace " karkadamu yaya, yama za'ai in sake ganinshi? Sannan bazan bari effort d'inka ya tafi ba yanda kasa naji zuciyata tayi sanyi ba."

  Ammar kallanta kawai yake, ta kara sakar mai murmushi sannan ta hure mai ido tace " Yaya kallan fa?"

  Mik'ewa yai da sauri tare dasa hannu a aljihu duk ya rikice yace " Ehem dama dama fita zan d'anyi, nan zafi ko bakya ji?"

  Batasan sanda tasa dariya ba, tace " Zafi kuma yaya? Nan d'in?"

  Kallanta yai yace " Seemah just now dariya kikai ko? Badai hallucination na gani bako?"

   Tai kasa dakai tana murmushi tace "kai yaya kai d'in ne wai zafi."

  Kallan yanda take murmushi yasa ya farajin zafin na karuwa, da sauri yai waje, yana fita daga d'akin ya fara furzar da wata iska yanacewa " Cool down Ammar."

  Can kuma yace " meke damuna?"

  Junaid ne ya dafashi yace " Ammar agidan gaisuwar ba kunya kake soyayya?"

  Kallan Junaid yai a tsorace, Junaid yai murmushi yace " Ya Habib ya fad'amin komai karka damu."

  Ammar yai ajiyar zuciya sannan ya kuma kalleshi da mamaki yace " ban gane soyayya ba kuma?"
  Junaid yace " in ba soyayya ba me kake a d'akin?"
  Ammar ya kalleshi da mamaki yace " What? Seemah ce fa a d'akin."

  Junaid ya d'an jinjina kai yace "ai sanin Seeman ce yasa na fad'a, Ammar ka nutsu ka tambayi zuciyarka, wacce irin soyayya kake mata?" Junaid na kainan ya juya yai gaba yabar Ammar da binsa da kallo.

  


   Jalal kam bayan su Abba sun fita yana nan dai a gun da yake, ya dad'e agun kafin ya daina kukan, yafara cewa " ya zanyi Seemah?"

  Jin ba amsa yasa yai shiru can yace " Abdul?"
  Cikin zafin nama ya mik'e yai waje,  a waje yaga Abba, Abba na ganinsa wani dad'i ya kamashi da alama harya sauko kenan, Jalal ya kalleshi cikin d'aure fuska yace " Abdul d'in yana ina yanzu?"

   Abba ya girgiza kai yace " Jalal ka rufamin asiri d'an Allah wannan mutumin yafi karfin mu bani ba har Isma'il d'in dayake da kud'i."

  Jalal ya kalli Abba yace " Abba ina Abdul d'in yake yanzu? Dole ne ya nemi yafiya agun Seemah da iyayenta, kaima kuma Abba dani dolene mu nemi yafiya, duk da ba lalai a yafemana ba, wayasan wace irin rayuwa suka shiga akan kalaman nan guda d'aya?"


   Abba ya kalleshi a tsorace yace " Jalal ninaji zan bada hakuri ko mai za'amin bazan damu ba amma Jalal ba ruwanka da harkarnan, dama tun farko baka san komai ba, d'an haka yanzun ma ka nuna bakasan komai ba."

  Jalal idanunsa suka ciciko yace " Me kace Abba? In nuna bansan komai ba? Taya zan iya?"
Hawaye suka zubo mai yacigaba " akan Mahaifiyar Seemah ne fa da kuma Wanda ya rik'eta kamar 'yarsa Amininka kuma."

  Yai ajiyar zuciya sannan yai d'an murmushin yake yace " Tunda naji labarinnan nasan ban cancanci auran Seemah ba, ko da kuwa iyayenta zasu amince dani, Ammar shine ya dace da ita koda har karshen rayuwata zan kasance cikin tsananin begenta bazan kuskura inkara gangancin cewa ina santa ba."

  Kalaman Jalal sun ratsa zuciyar Abba shima ya share kwallarsa yana kallan Jalal, cigaba da magana yai da cewa " Shiyasa nakeso ko ban aureta ba insamu in mata wani abinda zaisa ta rage tsanar datamin hakan ne zaisa ta manta dani."
  Ya kara share kwalla sannan ya kalli Abba yace " Abba kataimakeni inma Seemah abu guda d'aya a rayuwar duniyar nan."

  Abba bai san sanda ya rungume Jalal ba, yace " Jalal a koda yaushe ina alfahari dakai, kafi wannan mahaifin naka tunani mai tsawo."

  Jalal idanu kawai ya runtse, shikad'ai yasan rad'ad'in dayakeji a ransa.










  © *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*

��‍♀

1 comment: