����������������
�� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������
Na *AYUSHER MUHD*
No. 3⃣4⃣
Ammar gidan Dad ya wuce kai tsaye, saboda ganin yanda Dad yai ta k'iransa, ya dade yana knocking kafin Dad yazo ya bud'e mai, yana ganin Dad yace " Dad saura kiris in b'ata ai gashi na iso a gajiye amma ka k'i bud'e min kofa."
Dad ta d'an hararesa sannan ya kamo kunensa da karfi ya jawo shi ciki, Ammar ya saki kara tare da cewa " Dad so kake d'an saurayin d'an naka ya rasa kunne daga nan ya rasa matar dazai aura?"
Dad yasa hanunnsa a hab'arsa ya d'an karkata yace " Wato tun safe daka iso sai yanzu zakazo ganin mahaifinka ko?"
Ammar ya dariya tare da cewa " Dad kasani kaima inda nake ai, balle na d'ade banganta ba, kasan me?"
Bai jira amsar Dad ba yacigaba" wlh yanzun ma gudowa nai ban bari munyi sallama ba ina tsoron kar inmuka kara had'uwa in kasa tahowa."
Dad ya girgiza kai yana wani murmushin farin ciki yace " Alhamdulila nasani ko yanzu na mutu Ammar bazaka bari swthrt d'ina ta wulakanta ba."
Dariya yai yace " yanzu dai ka huce kenan?"
Kara kama kumnensa Dad yai ya jashi cikin falon, Ammar ya rik'e kunnen yana cewa Dad yanzu in na kawo matar dazan aura taga anamin haka ai rainani zatai.
Dad ya sakeshi tare da cewa " ka kusa kawota ne? Na d'auka bakada wacce ta kwanta maka?"
Ya d'anyi kasa dakai yace " Dad anya lafiyata kalau kuwa? Narasa meke damuna, duk macen dana gani wlh sam bata birgeni, har addu'a nake Allah yasa in samu wacce zata dinga birgeni ko kwatan yanda Seemah take birgeni ne."
Dad ya kara sakin murmushi baice komai ba amma a zuciyarsa fal take da farinciki.
Ammar ya kalli Dad yace "Dad nasani abu kakesan fad'amin ko?"
Dad yai ajiyar zuciya yace " eh Ammar amma kuma ina tunanin, maganar nan dole sai Habib yana nam za'a yita, ka k'irashi kaji in zai saku damar zuwa to, inkuma sai gobema dai to duk d'aya ne."
Ammar yace ok bari na k'irashi, waya ya d'aga ya k'ira number Habib.
Habib kam bayan ya shiga da Seemah cikin gida, bai saketa ba sai da suka shiga d'akinsu ya saketa ta zauna a bakin gado tare da turo baki tace " Ya Habib wai meke damunka kwana biyu ne? Ko ka daina so nane?"
Had'e fuska yai yace " Seemah bawai san ki bane na daina sai dai bazan yarda kiyi abinda zai ja miki dana sani ba har karshen rayuwarki."
Cikin rashin fahimta ta kalleshi tace " San Jalal ne zai ja min dana sani? Ko kuwa me?"
Had'e fuska ya sakeyi yace " bani wayarki?"
Da sauri ta mik'e tsaye tace " ban fahimta ba?"
Habib yace " ki bani wayarki nace ko?" Seemah ta mik'e tare da turo baki gaba cikin shagwab'a tace " Ya Habib kasan dai bazan iya rabuwa da wayata ba ko?"
Matsoyai kusa da ita tare da fizge wayar yace " kanwata ajiye miki zanyi, sannan gobe kishirya mu fita yawo."
Yana kainan yai hanyar waje, zubewa tai a kasa tafara kukan shagwab'a tana bubuga kafa, tasani indai tafara wannan kukan to kome takeso sai an mata shi koda kuwa ba'a san yi mata, sai dai mamakinta yau Habib ko juyowa baiyi ba, duk da kasan zuciyarsa kukan na tab'ashi sosai sai dai bazai bari rayuwarta ta salwanta ba saboda yarinta ba.
Yana shiga d'aki ya kashe wayar ya bud'e drawer ya sata sanna ya zauna a bakin gado yana tunanin mezai wa Seemah dazai sa ta manta wani Jalal.
Wayar Ammar ce ta shigo ya d'aga wayar kamar bayaso, Ammar yace " Dad ne kesan magana da kai amma yace in akwai abinda kake ka bari......."
Katseshi yai da sauri da cewa ganinan zuwa yanzun nan, yana kainan ya katse wayar tare da yin waje da sauri, tunaninsa d'aya "Dad ya sauko zai sanar dashi komai."
Da sauri ya fito falo yai hanyar waje, Farida data fito daga kitchen rik'e da tire ta yanka kayan marmari aciki, ganin ya fito da sauri yasa ta shiga k'iransa sai dai inaaaa hankalinsa yayi waje sam bai kula da ita ba.
Ajiyar zuciya tai sannan ta koma kitchen d'in.
Habib da kanshi ya shiga mota ya fara driven ya fito yabi inda da Jalal ya tsaya da wani kallo ganin basanan yasashi yin tsaki.
●●●●●●●□□□□□□□●●●●●●●●●●●□□
Jalal kam bayan Seemah ta shiga gida Sagir ya shigo motar tare da kallansa yace " Jalal sam ban fahimce meke faruwa ba, dan Allah kamin bayani."
Kansa ya rik'e dayakeji yana sara mai ya juyo a hankali yace " muje Sagir zan fad'ama."
Nan Sagir ya tadda mota suka d'au hanya, sunyi tafiya mai nisa kafin Jalal yace " Sagir ina san Seemah." Juyowa Sagir yai ya kalleshi sannan ya maida kansa titi yace " Jalal amma kasan........
Wani irin murmushin kafin hali Jalal yai yace " I am not worthy ko?"
Sagir yace ba haka bane, ni a guna you are far much more worthy sai dai su a gunsu.........
Jalal ya kwantar da kansa yace " Nasani Sagir, su sunfisan 'yarsu ta auri wanda yake the same class da su."
Yai ajiyar zuciya sannan yace " Sai dai abinda ban fahimta ba shine, na d'auka in mace da namiji suna san junasu shikenan, na farko ita yarinyarnan tasan banida hali kuma a hakan ta aminta dani, na biyu yarinyar nan tana sona, so ni ina tunanin kamar abinda akeyi baya dacewa."
Sagir ya d'an kalli Jalal yace " haka ne Jalal abinda kafad'a haka yake sai dai yanzu rayuwar da ake ciki kenan."
Jalal ya furzar da wata iska sannan cikin kakkausar murya yace" Sagir kasan me? " sannan ya saki murmushi yace " a farko nayi tunanin kamar da wahala a barmu tare da Seemah sai dai d'azu zuciyata ta sanar dani wani abu, bazan rabu da Seemah ba duk tsanani da abinda zasu ce, sannan bazan yarda su wulakantani ba, wannan alkawari nama zuciyata."
Sagir ya kalleshi yace " Jalal please nidai shawarata d'aya shine ka hakura da yarinyar nan, ni yaushe ka fara soyayya haka dakake jin zaka jure komai na abinda za'a maka? "
Jalal ya maida kallansa jikin window yace " yanzu nafara shiyasa nakeji kamar nafi kowa kamuwa da soyayya."
Dariya sosai Sagir yai yace lalai Jalal.........
Nima nace Lalai.............
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
��♀
No comments:
Post a Comment