*ZUCIYA*
_ĸowa da ιrιn тaѕa_
© *na Ayυѕнer Mυнd*
ayushermohd.blogspot.com
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*Where am i going to started? Ayeesh! U really left me without word, Thanks alot for the dedication of the whole book "Jini D'aya", I really appreciate ur love....May almighty Allah help and guide u through the right path...Ameen*
58
Bayan ya gama ne ya sa mata karamin towel ya sa mata akai sannan ya kalleta yace " zaki fita in watsa ruwa ko zaki zo mu watsa......"
Ai bata jira ya karasa bama tao waje da sauri, murmushi yai sannan ya tura kofar.
Nafi kam kofar tabi da kallo tace "wato yaya sam bashida kunya ko?"
Zama tai a bakin gado littafin nan na diary ta gani a hankali ta zaro shi ta bud'e shafin farko "To My dearest Son Ashraf."
Abinda ke rubuce kenan tai murmushi ganin wani d'an karamin hoto ba sai an tambaya bama Ashraf ne, passport ne da alama yana nursery aka d'auka tai murmushi sannan ta bud'e shafi na biyu.
_Ashraf Allah baiyi zanga girmanka ba sai dai inaji ajikina ko bani zaka zama yaro na gari, mai san 'yan uwansa da na kasa dashi._
Nafi ta sake murmushi tace "Abba ai d'an naka ne ba a gane cikinsa."
Tana bud'e d'ayan page rubutu ne sosai, tana kokarin karantawa taji motsin alama na bud'e kofa, da sauri ta maida littafin sannan ta mike.
Ashraf ya kalleta sannan ya karaso inda take, yace "matsoraciya."
Kanta ta kawar gefe batace komai ba.
Toilet ta wuce da sauri, yabi bayanta da kallo zuwa cinyoyinta da suke a waje, kansa ya shafa sannan ya zura riga doguwa ya fita falo.
Nafi kam bayan ta watsa ruwa ta fito tare da tsayawa a d'akin to me ma zatasa? Ina kuma yayan yaje? Rigarsa ta gani t-shirt irin mai dogon hannun nan kawai ta zura sai ta sauke towel din kasa ta d'aurashi kamar zani.
Tana d'aura kanta da ribbon Ashraf ya shigo, kallanta yai yadanyi dariya yace " da har ina tunanin d'auko miki kayan yayarki?"
Da sauri tace " wacce yayar?"
Ya d'an bata rai kadan yace "wace yayar kike da ita a gidan nan?"
Baki ta tabe tace " bansa kayanta bama an jikani ina kuma ga ta ganni da kayanta?ai inaji kanazir zata zubamin ta kyasta ashana."
Ashraf ya danne dariyarsa yace " ke dai tsoronta kawai kikeji da alama, ko da yake baki da laifi Anisa ai akwai zuciya, ga kwarjini kuma bata da tsoro kamar o'o."
Nafi ta d'an harareshi kadan tace " nima ai inada zuciyar kuma ba tsoro garen ba kawai dai raga mata nake nima."
Ashraf baisan sanda yasa dariya ba, sai dayai sosai sannan ya kalleta ta wani ci magani yace " ayya bansan raga mata kike ba ai, ashe karamar matar tawa ba tsoro."
Nafi ta kara had'e rai tace " ai in aka bi ta gaskiya ma nice babba dan nice uwargida."
Baki Ashraf ya bud'e sannan yai dariya yace "Uwar gida?"
Ta turo baki tace" to wacce in ba ni ba?"
Dariya yasa zai yi magana yaji ana knocking, nan yai waje yana dariya, lalai yarinyar nan, uwar gida??? Ha ha ha ni kaina sai da na sa dariya.
Dan liti ne bayan ya shigo ne Ashraf ya kalleshi yace " ya? Ina da ina yaje?"
Nan Dam litti yashiga mai bayani, Ashraf yai shiru can yace " shikenan sai zuwa gobe."
Dan litti yamai sallama ya fita, Nafi bayan taji rufa kofa ne ta fito, a falo ta ganshi ya zauna tare da sa hannunsa duka biyu akan hancinsa zuwa bakinsa, Nafi ta zauna kusa dashi tace "Lafiya?"
Kallanta yai tare da girgiza mata kai alamar ba komai, ya mata murmushi.
Itama murmushin tai sannan tace " nikam kun hadu da babansu Ferry ko?"
Kallanta yai yace " Inda kikai yaji?"
Tai murmushi tace " ka ganshi?"
Kai ya d'aga alamar eh, sannan yace " ya akai?"
Tace " baka sanshi ba ko?"
Kai ya d'aga mata cikin rashin kulawa yace " yeh."
Shiru tai hakan yasa yace "ya akai?ya kamata in sanshi ne?"
Tai shiru kafin tace " a company din Abba yai aiki da."
Kallan mamaki ya mata yace " what?"
Tace " kuma da alama abokin Abba ne, dan bayan rasuwarshi ya ajiye aikinsa na company din."
Ashraf yace " ko abokinsa ne mai zai sa ya ajiye aikinsa dan Abba ya rasu?"
Shiru tai hakan yasa ya dafata yace "Nafisa!"
Nafi tace " wlh bansan dalili ba sai dai kamar yana zargin mutuwar Abba ne."
Shiru yai hakan yasa tace " menene?"
Ya kalleta yace " sunansa Isma'il?"
Kallan mamaki tamai tace kasan sunan ne?"
Da sauri ya mike yace " zan turo Little ta kawo miki kayanki."
Ta mike tace " ina zaka?"
Bai amsa mata ba sai makulli daya zara yai waje da sauri.
Bayansa tabi da kallo, sannan ta kalli ledar daya bata d'azu, mam ta bud'e ganin kwalin waya yasa wani farin ciki ya kamata, irin wayar hannunsa ce har kalar sai dai ita bata kai waccen ba, wani murmushin farin ciki tai tace "Yaya na gode."
Nan ta bud'e wayar ta shiga ta tabata.
********
Ashraf direct a kofar gidan su Ferry yai parking, ya karasa suka kaisa da mai gadi sannan ya tambayeshi ko mai gidan na nan, mai gadi yace " eh yana gida, wa za'ace mai?"
Ashraf yace kace " Dan marigayi Abbas ne."
Nan mai gadi yai cikin gida, baifi minti 3 ba sai gashi ya dawo wai ya shiga.
Nan ya rakashi falon baki, Nabil na zaune kusa da mahaifinsa yana ganin Ashraf ya mike suka gaisa sannan cikin muryar rada yace " rannan ya aka kare kai da budurwata Feena?"
Ashraf ya makamai harara sannan shima cikin rada yace " kai saurin gyara bakinka,wacce budurwar taka?"
Yana kainan yai gaba, a gaban mahaifinsu Ferry ya zauna, tare da gaidashi cikin ladabi.
Dad ya amsa sannan ya kalli Ashraf cikin tsoron abinda yazo dashi yace "Ashraf ya akai?"
Ashraf ya d'ago yace " Tun ranar da na fara zuqa gidan nan ka san ni ko?"
Dad ya kalleshi bai amsa mai ba, Ashraf yai murmushi yace " Na dade ina nemanka sai dai bansan ta inda zan soma cigiya ba, shiyasa nabarma kaina saninka."
Kallansa Dad yai yace " nema na?"
Ashraf yai murmushi yace "kasan lawyer din Abbana?Uncle Salim?"
Dad yace " Salim?"
Ashraf ya d'aga kai yace " ya sanar dani kai da amintar dake tsakaninka da mahaifina sai dai kowa na mamakin barinka company daga sanda Abba ya rasu."
Ashraf yad'an tsaya sannan ya cigaba, " sai dai ni ina tunanin ba aminta bace tasa kabar company din sai dai cikin d'ayan biyu, ko dai kasan abinda ya faru da mahaifina? Ko kuma da kai akai abinda akai, sai dai a koda yaushe in zuciyata ta rayamin na biyun ina saurin neman sauki gun Allah daya sa hakan karya zama gaskiya."
Dad ya kalli Ashraf ga mamakin Ashraf sai jiyai yace " Ya Mansir?"
Ashraf yace " kawu? Yana nan." ya fada yana mai kallan mamaki.
Dad yai murmushi yace " me kake tunani gama da Mansir?"
Ashraf ya d'an rage idanunsa yace "naam?"
Dad ya sake murmushi yace " u are smart, nasan kasan me nake nufi."
Ashraf ya kalli Dad yace " nagane me kake san tambayata sai dai bansan meyasa nakeji a jikina ba Kawu bane kadai."
Dad yai murmushi yace " As i expected nasan dan Abbas bazai bani kunya ba, u are right sai dai bazakaji komai a bakina ba, sai dai zan baka suna guda d'aya kaje kai amfani da wannan sunan ka gano shi da su waye suka had'u sukama Abbas haka."
Ashraf yai shiru yana kallan Dad, dad yace " Auwal max."
Kaje kai tunani ka kuma yi amfani da wannan sunan mutumin ka gano su waye ragowar, in ka gano sai ka dawo ni zan sanar da kai abinda na sani saboda a lokacin ne zan gane lalai zaka iya komai."
Ashraf ya maimaita sunan "Auwal Max!"
Sannan yai godiya ya mike ya fito, a wajen falon ya tsaya yana kallan kofar falon, lalai mutumin nan ya iya d'aure magana, ya maimaita sunan Auwal Max!
Sannan ya fito daga gidan yayi sa'a bai ga Nabil ba da sauri ya fada mota yai gaba.....
*GODIYA MARA ADADI AKAN ADDU'OINKU.*
_Nagode kwarai, insha Allah zaku cigaba da jina kullum._
_Tnx for ur love and support💞_
*ASHRAFEENAH TEAM*
*LET'S GO👩🏻✈*