*ZUCIYA*
_ĸowa da ιrιn тaѕa_
© *na Ayυѕнer Mυнd*
ayushermohd.blogspot.com
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*Wannan shafin sadaukarwace gareki yar uwar arziki Lubbabatu Maitafsir, Allah ubangiji ya kareki daga sharrin mutane, yasa ki gama da duniya lafiya....Ameen suma Ameen*
*43*
Da safe bayan nafi ta tashi daga bacci tai wanka sannan ta fita zuwa kitchen, da kanta ta shiryama Ashraf abinci sannan ta d'auka tai b'angarensa.
Tsayawa tai tana mamakin ganin taje kwankwasawa taga kofar a bud'e, shiga tai tare da sallama sai dai jin shiru ba'a amsa mata ba yasa tai tunanin ko wanka yakeyi.
Shiga tai ta ajiye tiren a kan dinning sannan ta karasa cikin falon da niyyar zama, a kwance ta ganshi akan duguwar kujera yana bacci, ta saki murmushi sannan ta karasa gun.
Tsugunnawa tai a saitin fuskarsa ta kuramai ido bacci yakeyi sosai, a hankali tace "Handsome." sannan ta kalli kirjinsa littafine wanda bangonsa ke da kauri kana gani kasan ba irin littafan yanzu bane, hannu tasa ta d'aga littafin, jitai an rike hannunta.
Da sauri ta kalleshi har a lokacin idanunsa a rufe suke, ta sake littafin tare da neman tashi, jawo ta yai wanda hakan yasa ta fad'a kan kirjinsa, idanu ta shiga kiftawa tana kallansa, idanunsa a rufe yace " ina zaki?"
Kallan mamaki tamai ya akai yasan itace? Ko ya d'auka matarsa ce? Katseta yai da cewa " kin gama kallan nawa? Me kika gano?"
D'agashi tai kad'an sannan tace " yaushe na kalleka?"
Murmushi yai sannan ya bud'e idansa a hankali ta d'auka zaiyi mamakin ganinta sai taji yace " kin tabbatar ba kallona kike ba?"
Kai ta d'aga tare da d'an juya kai, ya d'an had'e rai yace " to amma ya akai nakeji kamar anata kallona?"
Ta kalleshi cikin shagwaba tace " dama ba bacci kake ba?"
Ya sakar mata hannu sannan ya d'auke littafinsa tare da mikewa zaune yace " wayacemiki ba bacci nake ba?"
Ta kalleshi idanunsa kuma sun nuna bacci yakeyi, tace " to ya akai kasan ina kallanka bayan bacci kake??"
Ya sa diary din a gefensa sannan yace " ke zan tambaya."
Mamaki ya kamata ta kalleshi sannan ta nuna kanta da yatsa tace " ni kuma?"
Ya juya kai sannan yace " amma da alama in babanki ya ganki yanzu banaji zai yarda kece 'yarsa."
"Why?"ta fad'a tana kallansa, yace " komanki ya canza kinsan me ake nufi da komai?" ya karasa maganar yana neman kare mata kallo, mikewa tai da sauri tace " ni bansan wani komai ba sannan me yasa kabar kofarka a bud'e?"
Yace " baki nake jira sai dai nayi mamaki danaji basuzo ba."
Baki? Da safe?
Kai ya d'aga sannan yace " bakin da ba'a sanin zuwansu bare tafiyarsu."
"B'arayi??" tafad'a cikin tsoro, wani murmushi ya saki sannan yace " just 4get,kikace me jiya?"
Tace " cewa nai zankoma skul yau saboda karatu, na saba bana dawowa gida shiyasa yanzu nakejina daban."
Dinning ya kalla ganin breakfast yasa ya mike ba tare da ya bata amsa ba ya d'au diary djn nan ya shiga d'akinsa, toilet ya fad'a yai wanka sannan yai brush ya fito ya shirya.
Nafi kam haushi duk ya isheta taya za'ai suna magana ya tashi ya barta agun ba tare Da yace mata komai ba, ta d'an harari kofarsa kad'an sanna tace " badai bacci ya koka ba? Wata zuciyar tace zai iya kuwa dan kinsan ya tab'a tsaidake yai bacci, ta dan cije leb'e sannan ta mike da niyyar yin zuciya ta fita, har taje bakin kofa ta tuna so take fa ashe tabar gidan nan, komawa tai a hankali tana tafe tana zumbure zumbure, har ta shiga falon zata zauna sai kuma ta kara kallan kofar ta kalli hotonsu da Anisa ta makama hoton harara sannan ta tab'e baki tace " da alama kai kadai kake santa, dan da tana sanka da bazata yarda da sharrin da akama ba wani ni karu.....Tsaki taja sannan ta kara hararar hoton tace " ko meye ma nasa hoto a falo? Sai kace ba'a sansu ba?"
Ta had'e rai tare da kara hararar kofar tace " san maso wani kaima dai kakeyi kamar ni." tana cikin murg'udawa kofar baki Ashraf ya fito, idanu ta zaro ganin ya ganta yanda ta karkace baki, juya baya tai da sauri tare da rufe bakinta da hannu.
Har ya karaso gunta bata sani ba sai kamshin turarensa kawai da takeji yana ratsata,har wani lumshe ido takeyi, saitin kunnenta ya kai bakinsa yace " badai bayan murgud'a bakinba harda zagi?"
Daidai inda yai maganar ta juyo da fuskarta da sauri cikin tsautsayi bakinta ya tab'a nashi, jikinta ne ya hau rawa da sauri ta matsa ta fara ja da baya ta rufe bakinta da hannu tai waje da gudu.
Shi kansa a kame ta barshi ganin yanda ta fita da gudu baisan sanda ya saki wani murmushi ba, da sauri ya girgiza kai yace " me ke damuna? Rainane ya kamata ya b'aci fa ganin abinda ya faru meyasa nake murmushi???"
Kan dinning ya karasa ya bud'e babbar kular dankali ne na turawa sai dai an sarrafashi da nikaken nama dasu vegetables, kamshi ne kawai ke tashi, murmushi yai sannan ya bud'e d'ayar karamar kular awara ce a ido sai dai dayakai bakinsa sai yaji kamar cuscus, ya sake murmushi sannan ya had'a tea yana cin abinci yana santi, a ransa yace " nasan Nafisa ce tai lalai mijinta ya......." kasa karasa wa yai sakamakon jin dayai maganar tamai banbarakwai.
Nafi kam da gudu ta fad'a d'aki a zaune taga little tana waya da alama da ya Habib ne ganin yanda take wani rage murya, Nafi ta fad'a gado sannan taja bargo ta rufe kanta ruf, tanaj Little na cewa " Yaya to ai kaine jiya ka tafi ba sallama, daga fitarmu."
Nafi kam haryanzu bakinta a rufe yake duk da tana cikin bargo, me ta aikata??idanu ta runtse tace " me yasa ya kawo kanshi nan to?" iho ta d'anyi tare da kara dukunkunewa ganin haka yasa Little tai sallama da Habib ta matso tace " Feena meye hakan?" ta fad'a tana kokarin yaye bargon, Nafi kam ta kara kankame bargon ta daddane,Little tace " feenah meye hakan? Wani abun aka miki?ko su umma ne?"
Nafi kam ba magana sai kara kudun dunewa take hakan yasa Little ta mike tai waje, a falo ta tsaya ta kira Ashraf, shi kuma a lokacin yayi shiru sai abinci da yakeci yana mamakin meya hanash karasa maganarsa wayar Little ta shigo.
Yana d'agawa tace " yaya inaji fa su Umma sun ma Feenah wani abun kaganta ta dawo ta shige bargo ko magana ta kimin.
" karki damu bari nazo sai inji." tace to amma ni Mumy na kirana, zan bwrdai d'akin a bud'e.
Ya amsa da to.
Sai daya gama cin abinci sannan ya d'au key din mota ya fita, b'angarensu ya nufa, kamar yanda tace kofar kuwa nanan a bud'e hakan yasa ya shiga, tare da sallama.
Nafi tanajin sallamarsa ta kara kudundunewa, Ashraf ya karasa tare da tsayuwa a gefen gadon yace " Malama tashi ko? Ko kin fasa tafiyar?"
Nafi ta kara shigewa, ya d'aga kafad'a yace " bari kawai in fadama little mai kikai inaji hakan zai sa ki tashi."
Gaban Nafi ne ya fad'i batai auni ba taji yace " Little kinsan mai yarinyar nan tamin??????"
Ai batasan sanda tai wani irin mikewa va ta rufe mai baki da hannunta duka biyu ba tana faman girgiza mai kai Alamar kar ya fad'a.
Kallanta yai duk ta sake karfinta akansa, wuyansa har kasa yai ya d'an sa hannu ya fara known karin zare mata nata hannun ita kuma ta kankame bakinsa, juyowa tai da niyyar yima Little magana sai taga ba kowa.
Mamaki ya kamata ta juyo ta kallesh.
Hannu yasa ya zare nata hannun da karfi yace " me? Kunya kikeji?"
*THE INNOCENT TEAM*
No comments:
Post a Comment