Thursday, 13 July 2017

Zuciya....Kowa da irin tasa 44

*ZUCIYA*
       _ĸowa da ιrιn тaѕa_

© *na Ayυѕнer Mυнd*
    ayushermohd.blogspot.com

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡

  *44*

   Nafi fuskarta d'auke da mamaki ta ke kallansa, ya kalleta shima yace " What?" murmushi tai sannan tace " dama ka iya tsokana? This is the first time i......"
  Katsets yai tare da had'e fuska yace " yaushe kika dawo da kike tunanin komawa?"
 Tai murmushi sannan tace " Yaya S3 zamu shiga so nake kafin lokacin waec a karamin lesson sosai."
Ashraf bai san sanda yace " ai kina kokari sosai, bakiyi primary ba amma gaski kin iya speaking sannan ko a class result dinki ba mai muni bane." a zahirin gaskiya shi ya d'auka a ransa yake fad'a sai dai gani yai Nafi tayi kasa dakai cikin farin ciki tace " Yaya a koda yaushe tsoro nake kar exam ta fito inga banyi abin arziki ba banaso kayi tunanin rashin amfanin kaini makarantar dakai."

   Kallanta yai na wasu 'yan dakiku duk da kanta na kasa sai dai yaji dadin kalamanta, yace " yanzu kin daina san kiga Mahaifinki?"

  D'agowa tai ta kalleshi idanunta suka ciciko sai dai hawayen basu zuba ba, Ashraf ya sake had'e rai yace " Naga alama haryanzu ke raguwa ce." ya juya zai fita, hannu tasa da sauri ta riko rigarsa, ya tsaya cak sai dai bai juya ba.

  A hankali ta fara magana " Yaya ba wai dan kayi zancen Baffa bane yasa kaga nayi haka, kuma yanzu ko ni bazance zanje ba harsai na gama karatuna, sai dai naji dadi ta yadda baka manta da komai ba."

  Juyowa yai da niyyar yi mata magana idanunsa suka sauka akan wayar da saurayinta ya bata a gabansa, ji yai ransa ya b'aci ya kurama wayar ido ba tare da ya d'auke idansa ba yace " ki shirya ki sameni a bakin mota."
 Yana kai nan ya juya, da sauri itama ta juya dan ganin inda ya kalla, waya ta gani da sauri ta dafa kai cikin takaici ta d'au wayar har tana kokarin jefata cikin drawer sai tace " wait a moment..... Me yasa yaji haushi dan yaga wayar?"
  Ferry ce ta fad'o matavda sauri ta kuna wayar ta danna number ferry, sai data kusa katsewa ta d'aga cikin muryar iyayi tace " Hello! "
  Nafi tai dariya tace " to uwar jan ra'ayin maza nice."

 Muryarta  ta sake sannan tace " Feenah amma kin kwafsa."
  Nafi tai murmushi sannan tace " Ferry tambaya zan miki."
 Tace "me? Akan yayan naki?"
 Nafi ta d'aga kai kamar tana ganinta sannan tace " yanzu yaga wayar da wani ya bani sai naga ya had'e rai sosai, me kenan?"

  Ferry tai dariya sannan tace " cikin d'ayan biyu ko ya fara kishinki ko kuma kice kika fasara abun haka."
  Nafi cikin masifa tace " Nafassara kamar ya?"

  Ferry ta sake dariya sannan tace " saboda kinaso yai kishinki mana yasa kikai tunanin haka."

  A zuciye Nafi ta katse wayar ta ja dogon tsaki sannan tace " na fassara? A gabana fa naga ya had'e rai."

   Wayarce taji tayi kara tana dubawa taga ansa My Number, Alamin ne tai d'am tsaki ba tare da ta d'auka ba ta mike ta hau shiryawa.

   Ashraf kam yana fita yai b'angaren Umma, a zaune ya samesu suna breakfast ya karasa ciki bayan anmai izinin shigowa, Anisa dai kawai cakular abincin takeyi ganin Ashraf yasa ta kuramai ido tanaji kamar taje ta rungumeshi, sai dai abin haushi ko kallanta bataga yayi ba, ya karasa ciki ya kalli Asim wanda ya had'e rai yana zubamai harara.
  Kowa a falon ya d'auka biko yazo yi, bayan ya gaida Umma ta amsa sai ta d'ora da cewa " Ashraf yanzu meye amfanin fad'an da kukai bayan kowa yasan yanda kuke san junan ku yanzu
......"

  Katseta yai tare da kallan Anisa yace " ina kikasamin takarduna na rannan?"

  Kowa yayi mamakin wannan kalaman nasa sannan ran kowa ya b'aci, Ashraf ya cigaba " na kira wayarki a kashe, fad'amin inda suke dan inada abinyi." ya karasa maganar tare da mikewa tsaye, Anisa cikin tsantsan kuluwa da takaici tace " Suna drawer d'akinka."

  Bai sake cewa komai ba ya juya ya fita, Asim ya daki kirjinsa da karfi cikin takaici yace " Umma yaron nan zai samin hawan jini in har ba'a kawar dashi daga gabana ba."

   Ashraf yana fita har zai wuce sai yai tunanin gaida mumy hakan yasa ya shiga, tana zaune itama kusa da Kawu ta zubamai abinci yana ci ita kuma tana zaune kusa dashi, ransa yakai kololuwar b'aci a duniya ba A binda ya tsana irin ya shigo yaga mahaifiyarsa da kanin babansa a zaune suna soyayya duk sai yaji komai yamai zafi, juyawa yai ba tare da ya musu magana ba yai waje, Little dake gyara falon Mumy ta kalleshi tace " har ka fito?"
  Kallanta yai da jajayen idanu wanda hakan ya bata mamaki taga yanzu ya shiga lafiya kalau, yace " karkice mata nazo."

  Ya juya ya fita, kallo ta bishi dashi sannan itama ta leka wajen dinning din, yanda ta gansu a kasa suna cikin fara'a gasu daf da juna yasa ta fahimci abinda ya sa yayan nata haka.
  Ashraf kam yana fita yai bakin mota, tun daga nesa ya hangota zuciyarshi tai haske duk da bai fito kan fuskarsa ba amma ya rasa dalilin dayasa yaji kashi 60 na bakin cikinsa ya yaye.

 Cikin atamfa riga da siket take sun zauna a jikinta kalar atamfar akwai orange hakan yasa ta sa mayafi orange tayi kyau sosai.
  Yana karasawa ya bud'e mota ya shiga itama ta shiga, Anisa kam da bayan fitar Ashraf ta d'an tsaya kad'an can ganin zata cuci kanta yasa ta fito da gudu ko d'ankwali babu a kanta tana yin kwanar inda ake ajiye motoci ta hangosu sun shiga mota tare.

   Wani irin kishi ne ya lulub'eta ta saki kukan takaici da tsana da take musu duka su biyun, a haka ta koma ta sanar dasu Umma nan  suka samu abinda sukeso sukaita zugata yau kam zugar tayi tasiri dan ta d'au alwashin amso zuciyar mijinta da dukiyarsa sannan ta kora wannan kucakar kauyensu.

  Suna shiga mota ya kalleta zaiyi magana ringing ya katsesu, jin ba irin ringing d'insa bane yasa ya kalleta, itama cikin nata salon dan da saninta ta d'auko wayar tanasan tabbatar da abinda zuciyarta ke so, kallansa tai cikin shakka sannan ta kalli wayar, ta canzama Alamin suna daga My Number zuwa My Alamin, ganin sunan daya fito kan wayar yasa ransa ya sake b'aci dama gashi bai gama warewa ba a zuciye ya fizgi motar sukai waje.

  Nafi kam bata d'auki wayar ba sai tai kamar irin tsoron Ashraf takeyi,sunyi nisa akan titi ba wanda ya kula wani, Nafi ganin haka yasa ta d'aure tace " yaya baka tsaida magana ba akan tafiya..."
 Bata karasa ba taji yace " gobe ki shirya ko driver din mumy ne ya kaiki."

  She really feel disappointed ganin yanda ya bata amsa ba wani damuwa ko kulawa, wata zuciyar tace " dan kawai ya sake miki fuska yau kin dauka sanki yake? Stop dreaming Feenah."

  Kanta ta juya ta kurama titi ido, a cikim ginin Ado bayaro mall yai parking sannan ya fito, a hankali itama ta fito tare da kallan garin, hadari ne ya fara had'uwa.
 Ta juyo ta kalleshi taga yayi gaba, tsayawa tai cak ranta inyayi dubu ya b'aci ta bi bayansa da kallo ba tare da ta je inda yake ba, sai dayai nisa sannan ya juyo mamaki ya kamashi ganin bata taho ba tana tsaye a jikin mota sai idanu da ta kafeshi dashi.

  Shima tsayawa yai yana kallanta me takeyi acan?"
  Nafi ta juya tare da kifa kanta a saman mota ji take kamar tai kuka ko zataji dadi wannan dizgi har ina? Suzo tare amma ba magana sai kawai yai gaba ya barta, so yake ya nunama kowa bashida hadi da ita ko me?

  Jitai ance " in bazaki jeba shiga mota in maidake gida ko ki hau adaidaita ki tafi, kina tunanin banda abinyi ne?"

  Ta juyo ta kalleshi yana tsaye ya had'e fuska sosai, d'azu ta tuno sanda ya sakar mata fuska wannan wani irin mutum ne?"
  Ran Ashraf ya kara b'aci ganin wayar a hannunta, ta d'aure tace " yaya kasan ban taba zuwa ba amma kana ajiyeni kai gaba kabar ni, ya kakeso inyi?"
  Ranshi ya sake b'aci yace " bakida kafa ne ko kuwa jaririya ce ke?"

  Nafi ma cikin b'acin rai tace " duk da ni ba d'aya daga cikin abinda ka lissafa bace amma ai nima inasan kulawa, taya zamu taho tare ace kana can gaba ni kuma ina can baya?"
 Ashraf ya kalleta zaiyi magana yaji tace " so kake ka nunama kowa bakada alaka dani?na sani kafi karfin ajina balle har ka jera dani sai dai na rasa me yasa nakeji zafin hakan aduk lokacin da kamin, nasan da hakan har kasan zuciya ta to why nakejin zafi?"
 Ta fad'a tare da juyawa tana neman maida kwallarta, jikinsa ne yai sanyi sam matsalarshi kenan bayasan yaga ya sa mace kuka, kallanta yai sannan yace " zaki iya tahowa yanzu?"

  Kallansa tai sannan ta fara takawa a hankali, Yana gaba kad'an tana binshi a baya, har suka isa cikin shop right  nan ya nuna mata babban cart ita kuma ta jawo suka fara zagawa, ita take nunamai abin bukatar makaranta inta sa d'aya sai ya kara biyu a ciki su zama uku, haka suka sai kaya sosai, ita har tsoro take nawa za ace musu in akazo gun biyan kud'i?

  Bai bari taji ba ana fad'an nawa ne yai saurin mika Atm card dinsa nam aka cira sannan akasa wani ya kai musu mota.

  Suna fitowa sukaga gari ya turnuke sosai, nan sukai sauri suka shiga mota, ko fita daga mall din basuyi ba aka fara yayyafi, kafin kace me? Ruwa ya tsuge sosai ruwa mai karfin gaske wanda ko gaban mutum baka gani.

  Nan Ashraf ya gangara gefen titi yai parking, sunyi shiru sai kallan yanda ruwa yake sauka kawai sukeyi, Nafi batai auni ba taji muryar Ashraf cikin sanyi yace " karki sake cemin nafi karfinki wai ko na tafi saboda bazan iya jera wa dake ba."

  Kallansa tai cikin wani irin yanayi mai wuyan fassarawa ya juyo shima ya kalleta, ganin yanda take kallansa yasa yaji wani abu na ratsamai jiki, kansa ya d'auke da sauri, ya had'e rai sosai, Nafi ta matso sannan tace " Yaya ni..."
 Wayarta ce ta sake katseta ya juyo ya kalleta tare da kallan wayar, number d'azu ce, ta kalleshi cikin tsoro kafada ya d'aga mata sannan ya mata alama akan ta amsa wayarta.

  Jiki a sanyaye Nafi ta d'aga tare da sallama, Alamin yai ajiyar zuciya yace " At last kin d'au wayata."
 Nafi idanunta nakan Ashraf tace " sry d'azun ma wani abu nakeyi."
 Ashraf kam wayarsa ce a hannunsa yana dannawa sai dai hankalinsa na kan wayar da take.
  Alamin ya saki murmushi sannan yace " Feenah plz ki daina jamin rai wlh zuciyata zata iya kamuwa da ciwo in har baki tausaya kin amince da ita ba."

  Har yanzu idanta nakan Ashraf sai dai jin kalaman Alamin sun sa ta d'an sassauta murya kamar mai rad'a tace " Alamin ya kake so inyi wai?"

  Yace " ki amince dani na zama saurayinki ni kadai."
  Tace " bangane ka zama saurayina kai kadai ba??"

  Ashraf ne ya juyo ya buga mata wani mugun kallo wanda batasan sanda ta sauke wayar ba daga kunnenta hannubya bata akan ta bashi wayar ba musu kuwa ta mikamai ya sa hannu ya amsa tare da kashe wayar gaba d'aya, mamaki ya kamata a ranta tace ko kishin ne??
 Jitai yace " ku mata wani sa'in me yasa bakuda tunani ne?"

  Nafi ta zaro ido cikin mamaki tace name fa?

  Ya kalli wayar yace " ke kina ganin burgewa ne saurayi yaba budurwa waya ba wata magana mai karfi a kasa?"
  Nafi ta turo baki batare da ta amsa ba, yace darajarta take ragewa agunsa alama kuke nunawa na abin hannunsa kuke so.

  Nafi cikin takaici tace " ai ba ni nace ya bani ba sannan magana mai karfi ai za'ayita in na gama makaranta."

  Dariya taga yayi sannan taji yace " kin manta me nace miki kenan ko? Randa zakizo garin nan."
 Kallan mamaki tamai yace " cewa nai sai na yarda da yaron sannan zan baki takardarki."

  Kallan sa tai sai dai zuciyarta taji ba dadi haryanzu wato yana tunanin bata takarda ko??????

*THE INNOCENT TEAM*

No comments:

Post a Comment