����������������
�� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������
Na *AYUSHER MUHD*
No. 2⃣3⃣
Nan ya fara nuna mata yanda ake tuki, tafara ja sunayi suna kallan juna wani so ne ke kara ratsa dukansu, bayan sun gama suka fito waje, Seemah ta hau saman bayan mota Jalal ya tsaya a gabanta ta kalleshi tace " wani irin farin cike ne ke ratsani Deen."
Kallanta yai cikin so sai dai kafin yai magana wayarsa tai kara yacirota, yana dubawa yaga Abbansa hakan yasa yad'an matsa kad'an da Seemah, bayan sun gaisa ne Abba yace " Zaka shigo wannan weekend d'in?" Kallan Seemah yai sannan yace " Wlh Abba bansanj ba tukun na ya jikin Zaheeda?"
Abba yace " Da sauki dama zancen kai kudin ka ne, a cikin kud'in da kake turowa akwai ragowa ina ganin ya kamata mukai karshen satin nan." Jalal jiyai kamar an d'au bokitin ruwan sanyi an shekamai a jiki, dakyar ya daure yace kud'i kuma Abba? Da wuri haka? Yad'an kara matsawa hakan yasa Seemah hankalinta ya gaza kwanciya, saukowa tai tare da zuwa ta bayanshi kad'an.
Abba yace " Jalal me za'a jira to? Munada d'akuna dayawa kasani Zainab ba irin yan matan zamani bace da zatace sai kaza take so,to me zamu jira?"
Idan Jalal ya kad'a yace " Amma Abba ita Zainab d'in ta fad'a tana so nane? Karfa ayi abinda bazaiyi dad'i ba, d'an Allah Abba a d'an tsagaita maganar kai kud'in ka ga........"
Abba ya katseshi yace "Jalal anya zaman Abujan nan bai fara lalatamaka dab'iun ka ba? Ka tab'amin musu akan al'amuran dana yanke a kanka? Yau kai ne da kanka?"
Ajiyar zuciya Jalal yai zuciyarshi tai ba dadi yace " Abba ba haka bane kayi hakuri d'an Allah." Katse wayar Abba yai Jalal yanata Hello hello jin shiru yasa ya duba wayar, gaba d'aya jiyai jikinsa ba dad'i juyowa yai da niyyar ganin Seemah sai dai a bayanshi ya ganta idanunta taf da kwalla da sauri ta juya zata wuce, hannu yasa da sauri ya riko hannunta, tana tsaye batare da ta juya ba sai dai hawaye a hankali suka fara sauka daga idanunta, Jalal ne ya matso ta gabanta tare da kallan fuskarta, da sauri tai kasa da ido tana hawaye jikimshi ya karayin sanyi, dakyar ya daure tare da jan hannunta suka fara tafiya, gun zamanta ya bud'e mata ta shiga shikuma ya tsugunna daga setin kafafunta hanayensu na rik'e, yadaure yace " Meemah kinji komai?"
Kallansa tai da raunanan idanunta hawaye suka zubo ta luntse ido tare da had'iyar wani abu tace " Deen aure za'a maka?"
Shiru yai baice komai ba tace " dama a can England ana yawan cewa First love bai fiya kai mutum ga aure ba, Deen ban tab'a soyayya ba sai akanka, na d'ade da fara sanka amma sai yau Allah yai zamu fad'ama juna sirrin zuciyoyin mu ashe yau ne kuma rana ta karshe da......." da sauri yakai yatsarsa bakinta yace shiiiiiii Meemah don't say something like that. "
Kallansa tai hawaye nakara bin kuncinta hannu yasa yana share mata yana cewa " Meemah iyayen na ke san auramin ita, kuma bansan yanda zanyi in hana ba, d'an haka na taso ban iya musu ga mahaifina ba."
Hannunsa dake kan kuncinta yana goge mata hawaye ta rik'e kallanta yai da mamaki tace " Deen please don't live me."
D'ayan hannunsa yasa ya kara damke hannun nasu yace " I won't live you Meemah, but ke kina tunanin za'a barki ki aureni?" Kallansa tai tace "menene da kai? Ni komai yamin naka."
Dariya yai yace "ba wannan ba, kinsan dai duniyar da nake ciki da wacce kuke ciki va d'aya bace."
Tace" Duk abinda nace inaso ahi akemin a gidan mu so karka damu da wannan, kai nake so ba wani abu naka ba."
Murmushi ya saki sai kuma ta fizge hannunta tare da hard'e su, ya kalleta yace " lafiya?" Tace " ba dai auran waccen zakai ba sai kuma kai tunani kara aure na ba?" Kallanta kawai yake yana mamakin kalamanta tacigaba" Jal nifa a tarihin rayuwata babu raba miji."
Kallanta yai ya guntse dariyar dake neman fitowa ya mik'e tsaye tare da cewa " Shikena da na d'auka ko mata uku gareni tunda muna san juna ba wani abun bane amma yanzu na gane." Yai maganar fuska a had'e.
Seemah ta kalleshi tace uku? Da sauri ta fara waige waige Jalal ya kalleta da mamaki wani shago taganu daga nesa da sauri ta fara tafiya, Jalal yasha gabanta yace ina kuma zaki? Bata mai magana ba kawai nunamai shagon tai, yace me kikeso? Alama tamai da ruwa, yace koma bari in siyo, nan ya karasa yace abashi robar ruwa, nan mai shagon yace naira 100, Jalal ya zaro ido yace ya pure water naira 5 shikuma wannan har 100? Mai shagon ya kalleshi da mamaki, wallet d'insa ya d'auko 200 ne a ciki ya mika tare da ansar ruwan, ya juya yana zuwa ya mika kata, ansa tai tasha sannan ta mikamai tace kuskure bakinka, yace bangane ba? Cikin shagwab'a tace nidai ka kuskure bakinka banasan tuna kalamanka dakai na mata uku.
Dariya ce ta kamashi yace " haka kike da kishi? Tace ba kishi bane ba amma ai......... Dariya yasa tare da girgiza kai, komawa yai mazaunin driver yace " Yamma ta farayi kar a nemiki a gida."
Juya kai tai tana kallan window, Jalal yai murmushi ya tada mota, sun fara tafiya ya sa hannu ya anshi ruwab hannunta ya sha, kallobta bishi dashi tace "cewa fanai ka kuskure baki ba fa ka shanye maganarka ba." Kallan bakin jarkar yai saitin inda shatin jambakinta yake nan ya kara kafa rubar yasha tare da sakin wani murmushi shikanshi mamakin kansa yakeyi.
Fizge robar tai tace " bazaka amsamin ba?" Kallanta yai kad'an sannan ya maida kallansa zuwa titi baice komai ba.
Tafiya suka cigaba ba tare da kowa yayi magana ba haushi ya gama kama Seemah kara ta saka da sauri Jalal ya kalleta yace " Seemah menene? Da sauri ya gangara gefen titi tare da maida hankalinshi gaba d'aya kanta hannayenta ta sa ta rufe fuskarta, ciki damuwa ta sa hannu ya zare hannun data rufe fuskarta yace " Meemah menene?"
Idanunta a rufe suke yace " wani gurin ne ke miki ciwo?" A hankali ta bud'e idanunta tace" banasab ina maka magana kana k'in bani amsa, it hurt me."
Kallanta yai batare dayace komai ba ya gyara zamanshi tare da fara tuki, kallansa take rai a b'ace jitai yace " Wani sa'in ne bana sanin me zan ce miki, ban tab'a shiga ciki hali irin wannan ba inji wai bansan me zance ba sai a kanki."
Juyowa yai yad'an kalleta sannan yacigaba " Ban tab'ajin irin haka ba a tsawon rayuwata."
Kallansa takeyi jikinta yai sanyi, kalamansa sun tab'ata idanu ta lumshe tare da jingina kai tace " I will take ur word as ni ka fara so a duniya."
Kallan hanya kawai yake yana murmushi itama lumshe ido tai tana murmushi, wani irin so takema Jalal da ko suna tarr jitake tana missing d'insa, zuciyarta na bugawa a duk lokacin dayake kusa da ita, kalamansa kesa zuciyarta da ganganjikinta su yi lum cikin wani shauki, ya zatai in wani abu ya bemi shiga tsakanin............wayar Ammar ce ta katseta, basai ta duba ba d'an ringing d'insa daban ne a wayarta, d'auka kawai tai tare da gyara kwanciyar kanta zuwa kallan Jalal, tace " Yayana ya? Ammar yace " Seemah yanzu Zaid ya kirani wai a lalai shi ya d'auka number kice, murmushi tai tana kallan Jalal tace " Shareshi yaya shi wai a dole sai na bashi number ta shine na bashi ta ka."
Ammar yai Dariya yace " Kai Seemah, me yasa? Bai miki ba?"
Tana kallan Jalal tace " inafa zaimin bayan na riga na kulle zuciyata?bana kuma tunanin wani zai samu damar shiga." Kallanta Jalal yai wani farin ciki ma ratsashi bai tab'a ganin yarinya kamar Seemah wacce bata kunyar kalamanta ba, ko d'an ba anan ta taso ba? Sam bata kunyar fad'ar abinda ke ranta.
Da mamaki Ammar yace kamar ya? Tace " there is something like that. "
Tana kainan tace yaya bye zan k'ira anjima.
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
*FIGHTING*
��♀
Shukran.
ReplyDeleteShukran.
ReplyDelete