����������������
�� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������
Na *AYUSHER MUHD*
No. 2⃣7⃣
Jalal zaune yake akan kujera rik'e da takardu inka ganshi zaka zaci karantawa yake sai dai sam hankalinsa baya kan takardun, Seemarsa kawai yake gani a jikin takardar tana murmushi, ya kurawa takardar ido a hankali shima ya saki murmushi jiyai an kwankwasa masa desk, da sauri ya d'ago ganin manager d'insu ne yasa ya mik'e tare da cewa " Manager yaushe ka shigo."
Kai ya girgiza yace " Jalal kwana biyu meke damunka? Sam baka maida hankali akan aikinka, gashi ka tsiri wani d'aukan excuse inka fita sai ka dad'e baka dawo ba."
Kasa dakai yai baice komai ba, da fa kafad'arsa yai yace " Please Jalal ka koma yanda na sanka, yanzu ka duba maganar project d'in nan namu, sam ka kasa maida hankali akai gashi kasan kaf Team d'in nan namu da kai muka dogara."
A hankali Jalal ya d'ago ido ya kalleshi jikinsa yai sanyi a hankali ya furta" I will work really hard Manager."
Yace " thank you Jalal." Yana kainan ya bud'e office d'insa ya shiga, Jalal kam fita yai ya shiga toilet, ruwa ya zuba a fuskarsa sannan ya sa hannayensa biyu a kuncinsa yace " Wake Up Jalal, Get a Hold of Yourself. " yana kainan ya fito ya koma office ya fara aikinsa, sai dai jefi jefi yana kallan agoggon hannunsa.
Seemah kam tagama yanke hukuncin fad'ama su Dad maganar Jalal saboda sam batasan sud'inga zuwa wanj gun in zasuyi zance, bayan tayi Sallar magrib ta fito falo, anan ta taradda Farida dasu Ra'isa, suna ganinta suka fara murna ta karaso kusa dasu ta zauna tace homework akeyi? Suka d'aga mata kai, tace to azo nizan koya muku, da gudu suka mik'e daga kusa da Farida suka dawo kusa da Seemah, dariya tai tace Aunty na mik'i kwace.
Cikin sakin fuska tace " ni naji dad'in kwacen ma dan dama na gaji."
Seemah ta dukufa tana koya musu homework har ya Habib ya dawo, da sauri ta mik'e taje kusa dashi tace " Yaya ka dawo? Ka fad'ama Dad?"
Kanta ya dafa yace " oh ni kaina nakosa inji me Autarmu zata fad'amana haka, na fad'ama Dad yace muje gidan da yake."
Da mamaki ta kalleshi tace " wani gida yake?"
" ni kaina ban sani ba ashe Dad daga can yasa Abbansu Zaid ya d'inga masa gini, yana turo kud'in sai d'azu ya fad'ama."
Ta jinjina kai tace " ohhhh lalai Dad da alama yayi tanadin bikina, kasan ku maza ne a gidan Abba akai taronka haka ma za'ai nasu ya junaid, duk da banzo bikinka ba amma naji a jikina bayan bikin kane Dad yafara min tanadi."
Dariya sosai Habib yai yace " lalai kanwata kin girma, mene? Tanadin bikinki? Hahhhhh lalai zan sanar ma Dad 'yarsa aure takeso."
Idanu ta rufe sannan tace " yaya mu tafi to ko?" Yace " haba kanwata a barni inga 'ya'yana da matata tukunna mana."
Baki ta turo ta juya baya alamar fushi, Farida data dawo daga kai briefcase d'insa d'aki ta tsaya tana kallam ikon Allah, Habib yace "naji muje to tunda haka kikeso." Juyowa tai ta saki ihu tace " yauwa my bros." Da gudu ta wuce d'akinsu d'auko mayafi, tana kallan Aisha a zaune ko kulata batai ba taja mayafi tai waje, Aisha ta bita da tsaki tace " wani sa'in ta kulani, wani sa'in kuma ta nuna batamasan inagun ba."
Seemah na fita, Habib ya kalli Farida yace " sai na dawo" sannan yabi goshin su Ra'is da kiss suka juya sukai waje, suna shiga mota Ammar ya k'irata, tad'aga wayar ta shiga zubamai shikuma yana biyeta,bai gayamata gobe zaizoba saboda yanasan ya bata suprise.
Habib ya girgiza kai yace " Seemah in baki shawara?" Tace tame fa? Yace " karki kuskura kuyi waya da Ammar a gaban saurayinki ko wanda zaki aura, in fact karma ki bari su had'u.
Da mamaki tace "meyasa? Bayan yayana yafi ji dani nima kuma haka."
Habib yai murmushi yace "shine matsalar ai, yanda kukeji da juna in saurayinki ne ko budurwarsa sukaga yanda kuke zasuyi zargin wani abu."
Dariya sosai tai harda tafa hannu tace " Zargin me zasuyi bayan yayana ne uwa d'aya uba d'aya?"
Habib yace " wannan shikad'ai ne hujjar zai sa suyi shiru."
Takarasa dariya tace " to da wannan hujjar da mezai sa suyi zargin wani abu? Kaidai kawai yaya kanaso ka cina nine."
Haka yai ta tsokanarta har suka isa wani katon gida, bawai kato bane sosai sai dai yana da nasa girma d'an yayi biyun na Ya Habib, Habib ya kalli gidan yace " Lalai Dad har yai gida babban a garin nan ni babban d'ansa ban sani ba? Tace kamanta na fad'a maka? Yace auuuuuu na manta ai ashe fa na bikin Seemah me.
Tai kasa dakai tana murmushi, an bud'e musu gate sun shiga, Habib ya kara kallan gidan fitilon da akai kwalliya dasu a waje sun kara fito da filin gun, Seemah tace wow yaya bazan bika ba, na dawo gidanmu kenan.
Ya d'an ja kunnenta yace " ina kika isa? Ai kafata kafarki, kuma ma kinga ai ba masu girki a gidan, ko kin iya abinci ne? Ta ciji leb'enta tace " yaya fad'ar bakar magana ko? Zan baka mamaki ne."
Tana kai karshen maganar ta bud'e kofar motar ta fito, ta nufi gidan, Habib ma ya fito sunyi knocking sosai har Habib yafara kokarin k'iran Dad sai kuma aka bud'e kofar, Dad ne tsaye sanye da jallabiya, yace " Sorry my Princess na barki a waje ko?"
Ta had'e rai tace " da alama Dad bakai farin cikin ganina ba."
Hannu yasa ya jawota ciki yace " Sorry Swthrt kema kinsan ba haka bane wani tunani nakeyi sam banjin kwankwasa kofar ba."
Ta furzar da wata iska sannan tasa hannu tad'an biki goshinta tace " Oh God! Yazanyi da Dad d'ina? Dad kamanta an hanaka tunani mai zurfi? Ko kake hawanjinin ka ya tashi in shiga uku?"
Shiga ciki yai yana murmushi, Habib ya matso kusa dashi ya kara kallan falon komai ansa na furniture's da kayan kallo, yace " kaiii Dad yaushe akai gidan nan da har komai an saka?"
Dad ya kalleshi yace " kaidai kanada aure karma kai tunani zan baka aran d'aki a gidan nan." Ya juya zai ma Seemah magana sai dai bata gun, ya waige waige yace " Seemah!!!" Tace naam, ya juya da sauri inda maganar ke fitowa, tana kan matattakalar beni, yai murmushi wato d'akinta take nema tunda tasan Dad yasan tafisa Sama, kallanta yai yace muje in nuna miki d'akinki.
Da gudu ta karasa Sama tare da bud'e d'akin datake tunanin shine, baki ta bud'e ta kasa karasawa ciki Habib ya karaso da dariya yace " hala d'akin naki ba komai sai katifa........"
Shikanshi kallan d'akin yake komai na d'akin pink ne sai ratsin milk, ya juyo ya kalli Dad, da sauri Dad ya juya baya yana sosa keya, Seemah da gudu ta juya ta fad'a jikin Dad tace " Dad thank you soo much, Dad duk wani abu danakeso kafin na fad'a kake min, I love you soo much."
Da sauri ta sakeshi ta koma d'akin ta shiga kallan komai, Habib ya kalli Dad yace " Dad amma yaushe ka gyara d'akin nan?" Yai murmushi baice komai ba, ji sukai Seemah tace " Dad ku shigo mana," nan suka shiga suka kalleta ta baje akan gado, suna shigowa ta mik'e ta kamo hannun Dad ta zaunar akan gadon, tace " Dad na fad'a soyayya mai karfi, yazanyi inbanyi shekara 2 a d'akin nan ba?" Tai maganar cikin shagwab'a, da mamaki Dad ya kalleta sannan ya kalli Habib yace " me kikace Seemah? " ta mik'e tace ehem, Dad kasan me? Ya girgiza kai, tace wani guy nake bala'in so, ban tab'ajin abin da nakeji ba sai a kansa.
Gaban Dad ne yai wani irin mugun fad'uwa, cikin tsoro ya kalleta yace " just now what did u say?"
Ba Dad kad'ai ba ko Habib yasha jinin jikinsa, shima yace " Seemah me kikace?" Tace" ahhhhh so nawa zan maimaita, yaya shine wanda ka tambayenk d'azu, ah kama sanshi ai jalal na gun aikinka."
Dad ya runtse ido abinda yake tsoro shikenan yana shirin faruwa, Habib cikin b'acin rai yace " Haba Seemah wannan yaron kike so? Yaron da ko kayan jikinsa kika kalla kinsan abinda zasuci a gidansu ma da alama wahala yake basu, shi kike cemana kina so?"
Dad cikin tsoro da mamaki ya kalli Habib yace " mene?" Seemah ta mik'e taye taje kusa da Habib ta rik'e hannunsa tace " Yaya nifa a hakan nace ina sansa, meyasa bazaka bani goyon baya ba? Yaya bazaka gane irin san danake mai b..........."
Jitai an wanke ta da mari, cikin firgice ta kalli Dad da itadunsa suka kad'a sukai jajjawur, kamar me shirin zubar da kwalla mai zafi, Cike da mamaki Habib ma ya kalleshi, bai tab'a ganin Dad a wannan yanayi ba, cikin fad'a Dad yace kada ki kuskura ki kara min zancen yaron nan, sannan ku wuce ku koma gidan Habib dare yayi, Seemah data kasa tantance meke faruwa, mafarki take ko kuwa gaskiya ne, kamar bata motsi take kallan Dad, Dad ya kalli Habib yace " sannan kada ka kuskura ka kara barin Seemah ta fita, in fitar ta zama dole sai ka sanar dani." Yana kainan yai waje.
Seemah tabi bayansa da kallo, tama kasa kuka kawai hannunta ne a gun, Habib ne ya tako a hankali yazo kusa da ita zai dafa ta, juyawa tai da gudu tana hawaye tai kasa, mota ta bud'e ta zauna ta saki wani irin kuka mai ban tausayi.
Habib ya sauko tare da kallan Dad dake zaune a kan kujera idanunsa a rufe, yasan halin Dad da kuma yanda yake san Seemah, da alama ya mareta ne amma a zahirin gaskiya yafita jin zafin marin, harzai mai magana yaga kamar gwara ya kyaleshi, shima yai waje.
Yana shiga mota yaji kuka da Seemah take ya b'aci cikin damuwa ya kalleta yace " Seemah is okay kema kinsan Dad bawai yaso dukanki bane, ko ya tab'a dukanki?" Ta girgiza kai cikin kuka tace " Yaya menene laifina? D'an inasan Jalal ko d'an bayaso inso talaka?"
Habib yace " ya isa haka, gwara ki bar maganar wani Jalal d'an ko Dad bai hanaki ba ni zan hanaki."
Takara sa kuka, meyasa kowa bai fahimceta ba? Ita tad'aurawa kanta soyayyar nan? Basa ganin inta rabu da Jalal ta rabu da farin cikin ta ne?
Jalal kam jin d'akin ya isheshi ga sai hira suke da shewa yasa ya fito waje, yana tsaye a kan hanyar layin banda tunanin Seemah ba abinda yakeyi, gobe zaije gida ya sanar dasu...........wani me keke ne yayo kansa gadan gadan da sauri Jalal ya tsalle daga gun zuwa jikin bishiyar dake gun, hannunsa ne ya bugi bishiyar yai ajiyar zuciya tare da kokarin mekewa, mai keken ne ya taho da sauri ya taimaka mai yace " kaji ciwo ne? Jalal ya kalleshi yace a'a, amma wani irin tuki kake haka?"
Yace " Yahkuri wlh fitilar kekence ta mutu sam ban kula ba." Jalal ya kalleshi yace to Allab ya kiyaye, mutumin ya juya, hannunsa Jalal yaje kad'ewa mezai gani? Agogonsa ne ya fashen, cikin takaici ya kalli agogon kamar yasa ihu, kalaman Seemah ne suka dawomai, na in agogon ya tsage akwai Bad abu dazai faru da su.
Dariya ya saki yace " Jalal meke damunka? How can you believe that?"
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
��♀
Tnx Allah ya kara taimako.
ReplyDeleteYau talata an yi kamfa ne? Da fatan dai Lafiya? Allah yasa. Amin.
ReplyDeleteSalamu Aleikum, har yau laraba, jarumar shiru, da fatan Lafiya dai ko? At least dai mu San cewa Lafiya kike.
ReplyDeleteAllah yasa Lafiya ce dai.
Har yanzu dai, toh Allah sa Lafiya.
ReplyDeleteWlh lafiya, wani uzurine ya hanani typing.
ReplyDeleteNagode kwarai
Toh, mashaAllah tunda dai lau. Tnx
Delete