����������������
�� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������
Na *AYUSHER MUHD*
No. 2⃣5⃣
Dad ya fito jiki a sanyaye, mota ya shiga tare da dafa kansa da sitiyarin motar, zuciyarshi a ciki take fall da damuwa, yanzu ba wanda zaibi bayanshi a birne maganarnan da Ammar? Yasan halin yayansa sarai bazai bi bayan shawarar nan ba sai dai bashi da wani zab'in daya wuce yayan nashi.
Nan ya tada mota yafara tuki, yana gaf da shiga layin Seemah ta k'irashi tace Dad yaushe zakazo kad'auken? Dad yace " Seemah ina d'an wani abin ne bansan how long abin zai kai ba , ko zamu bari sai gobe muje?"
Seemah ta turo baki tace " shikenan Dad, Allah yakaimu." Yace Amin.
Suna Sallama ta kalli kanta a madubi da sauri ta rufe fuskarta da hannu biyu sannan ta bud'e ta kanne ido d'aya tace "See you My Deen." Tana fad'ar haka tasa dariya tare da kara rufe fuska tana murmushi.
Wayarta ce tai kara ta jawota ganin no name yasa tai sauri zata d'auka sai kuma ta ce haba Seemah d'an tsaya mana,Cool down, kinfiya azarb'abi, nan ta tsaya sai da ta kusa katsewa ta d'aga tare da cewa " ya akai?"
Kallamanta sun bashi mamaki yace " ban gane ya akai ba? Bakiso na k'iraki ba ko me?"
Seemah tai shiru tanajin wani sanyi a zuciyarta, Jalal yace shikenan sai anjima, zai katse tai saurin cewa Deen?
Jalal ya maida wayar, Seemah tace " irin jan ajin nan na mata fa zan maka kaikuma ba hakuri."
Dariya ce tazoma Jalal yace" to ni nasan ba wannan tsakanina dake, in fact ma ba haka kike ba."
Cikin masifa Seemah tace " Me kake nufi da ba haka nake ba? Lalai ma Deen wato kana so kace bani da aji ko me?"
Jalal yace" kema kinsan ba haka nake nufiba, nufina sanda kikemin nasan bazai barki kimin haka ba, kuma nima........"
Ha what? Deen mai kake nufi? Wato harkasan sanda nake maka? Ni bansan wanda kake min ba."
Jalal yace "oh my God! Seemah meke damunki yau? Ko kin tsaya kinji karshen maganata?"
Dariya Seemah tasa tace" just teasing you! Kasan me? Inaso inga ima tsokanarka."
Iska Jalal ya furzar sannan yace " zan rama ne." Tace guess what? Dad ya fasa zuwa muje d'an haka zamu iya had'uwa.
Wani sansanyan murmushi Jalal ya saki yace inzo gidanku mu tafi? Tace a'a zan zo wajen Company d'in sai kazo mu tafi, yace alright nan sukai sallama tabi wayar da kallo tarr da manna mata kiss.
Dad yana shiga yai parking har ya nufi ciki yaji ance " Mazan England ne a kasar tamu?" Juyowa yai jin muryar d'an uwa rabin jikinsa, a zaune ya ganshi daga gefen garden d'insa yana rik'e da jarida, nan dad ya juya zuwa inda yake, suna haduwa suka rungume juna Dad yace Yaya ashe kana waje? Abba ya kallesa yace baka fad'amin zakazo ba?
Dad yai ajiyar zuciya tare da zama a d'aya kujerar yace " Yaya su Seemah sunzo ko?" Wani mugun kallo Abba ya sakar mai ya had'e fuska kamar zaki dama shi bashida fara'a, yace" Isma'il da hankalinka ka turo yarinyar nan kasar nan?"
Dad yace " Yaya ya zanyi? Yarinyar nan takai shekara 20 'yan uwanta da ita kanta sun damu akan tazo nikuma sai naga kamar lokaci yaja yaci ace magana yanzu ta wuce."
Abba yace " kai kana tunanin magana irin wannan tana wucewa ne? Ko ni dana ganta jinai komai ma neman dawomin sabo."
Dad ya runtse ido yace " Yaya ka taimakeni yanda ka taimaken a baya, mu binne maganar nan da auranta da Ammar, in nace Ammar ba d'ana bane ba wani abu, nasan Ammar sarai bazai damu ba."
Abba idanunsa suka kad'a yace " wai Isma'il kanada hankali kuwa? Bakasan tsatsonta ba amma me? Ka aura mata Ammar? Wai kai wani irin mutum ne da bashi da zuciya, banda bala'in da mahaifiyarta ta ja maka yanzu kuma me? Ammar?"
Dad idannunsa suka ciciko yace " Yaya karka tunamin da abinda ya faru d'an Allah yaya, yanzu ni yaya matsalata d'aya banasan abinda zaisa Seemah cikin bakin ciki bare har tasan wannan mumunan al'amarin."
Abba ya mik'e cikin zafin rai yace " Bazan goyi bayanka akan lalatamana zuri'a ba, sannan bazan yanda kasama Ammar bakin ciki akan wata banza da ba'a............"
Da karfi Dad ya rufe ido yace " Yaya Please stop saying anything, please. "
Abba ya kalleshi yana tausayin Kanin nasa sai dai bazai yadda da hukuncinsa ba, nan yace " Isma'il inka warware mayi maganar ka gama tunanin ka shigo ciki."yana kainan yai ciki, Dad ya fara saukar da numfashi sama sama, kansa na sarawa, hannu yasa ya rik'e kansa jiyai hawaye na zubomai.
Seemah tana gama shiryawa ta fito a falo taga farida tace "Aunty zan danje ganin gari." Tace Seemah kinsan halin yaya......
Seemah ta katseta da cewa" ai shima bai hanani ganin gari ba." Tana kainan tai waje, sun fito ita da bala sai dai motarsu na fita Zaid ma kokarin shigowa sai dai ganinta a baya yasa ya saki murmushi tare da juya kan motar ya bita, sam ita batasan yana binta ba.
Suna zuwa wajen company d'in tace Bala yai parking ta mik'amai kud'i tace ka koma gida, yace madam yau dai d'an Allah......, ta katseshi da cewa " so kake in koreka daga aikin ko me?" Da sauri ya amsa tare da bata hakuri, yana fita tama Jalal waya ta iso, jitai anbud'e d'ayan gefen datake zaune ta baya da mamaki ta kalli kofar kafin tai magana Zaid ya shigo, ta kalleshi da mamaki tace " malam ya dai?"
Zaid ne ya juyo da fuskarsa tare da cewa " Wow I really miss u a lot. "
Ta kalleshi tare da nunashi da yatsa tace " You?" Yatsar ya rik'e tare da ajiyar zuciya yace " yeah Baby is me, wow har naji wani sanyi."
Hannunta ta fizge sannan ta kara nuna shi da yatsa tace " Ya Zaid don't you dare try to touch me again."
kai ya kwantar ajikin kijera yace woooo kai baby u are killing me with your charm.
Leb'e ta ciza sannan ta fito daga motar cikin takaici ta jingina da motar.
Zaid ma ya fito yazo daf da ita tare da cewa ina zamu ne Baby? Harara ta nakamai tace matsa min ko bakaga a yanda kake bane? Tafad'a tana kallan yanda ya babbaketa, murmushi ya saki sannan yace " Baby I........" Naushin da aka mai a fuska ne yasa bai karasa ba, jikake tim ya fad'i a kasa, Jalal cikin hucci yake kallan shigarsa kana gani kasan ta samarin zamani ne da sukejin kansu a sama, Seemah ganin naushin nan yasa ta kalli Jalal zatai magana taga ya kara d'agoshi zai makamai wani, da sauri ta rik'e hannun Jalal tace " Deen?"
Idanunsa sun kad'a sunyi jaa, ya kalli Zaid sannan ya kalleta yace waye? Zaid kam zafin dakemai zugi a baki ne yasa yakai hannu gefen bakinsa mezai gani? Jini? Wani kara ya saki yace jini? Jalal ya makamai harara yace kamin shiru kosai na karama wani? Zaid ya kalli Seemah yace " Babyna waye wannan da......." Jalal ya dunkule hannu saura kiris ya bugamai, sai kuma ya tsaya tare da kallan Seemah, sannan ya kalli Zaid yace baby?
Seemah ta kalli Jalal tace " My Deen sakeshi d'an uwana ne he is just joking, baka ga yanda yake magana ba? Kana gani kasan na mayaudara ne ai."
Jalal ya maimaita sunan a ansa My Deen? Tamasan ta fad'a kuwa? Kallanta yake cikin wanj shauki sannan ya tura Zaid gefe yace " Meemah me kika ce?" Ta kalleshi tace name fa? Yace " Abinda kikace yanzu da zakimin magana."
Kai ta juya tana murmushi tace muje ko? Jalal ya d'an canza fuska.
Zaid ya kalli Jalal yace " wai d'an tacema My Deen? Ahh amma kai gara ne, kamar bakasan mata da yaudara ba? Sai suce ma mutum My Heart sai ka duba wayarsu kaga ansa maka Jerk.
Jalal ya kalleshi da mamaki sannan ya kalli Seemah tare da cewa muga wayarki? Kasa tai da ido tace " So kake kabar Ya Zaid ya had'amu dakai?"
Zaid yace " Ahaf da alama ma bakada sunan mutunci a wayar." Yana kai nan yad'agama Jalal hannu yace " Boxing Man nayi nan.
Jalal ya d'auke idansa daga kan Zaid ya kalli Seemah tare da cewa muga wayarki? Miyau ta had'iya ta tina No name tasa, da sauri ta zagaya ta shiga mota sannan ta danna horn, Jalal ya bud'e motar ya shiga fuska a had'e gani yake kamar jerk d'in ma aka samai.
Seemah ta kalleshi ganin yanda yakejan mota da karfi, sai da sukaje can wanj guri sannan ya gangara yai parking tare da mik'a mata hannu alamar ta bashi, d'an yaga ta d'auko wayar da alama so take ta canza, ganin bata da niyya yasa ya fizge wayar tare da fitowa daga motar, wayarsa yadaga ya kirata, me zai gani No name ne ya bayyana akan wayar kurama sunan ido yai No name? Da rashin suna ai gwara jerk d'in ma, Seemah ce ta fito tazo kusa dashi jiki a sanyaye tace " My Deen amma......" wanj kallo daya buga mata yasa ta kasa karasa maganar, tafiya ya farayi itama tana binshi a baya, takalmi mai tsini ne a kafarta sam bata kula ba ashe dutse ne a gun kawai tai tuntube da takalmin Kara ta saka Jalal ya juya da sauri, sai dai ina? Har ta fad'i ta fara gangarawa dama kwari ne a gun, cikin tsananin rud'o ya lekata, ganinta a ya she a gefe yasa yai saurin d'ilikawa, yana sauka ya d'agota duk ya rikice ya shiga jijigata tare da k'iran sunanta, a hankali ta bud'e idanunta ta saukesu a kansa, kallansa takeyi shima kallanta yakeyi jiki a sanyaye yace "Seemah are u alright? "
Murmushi ta saki tare da cewa a hankali" ba wai rashin me zan sa maka bane yasa na saka No name, nasane saboda a time d'in ina sanka gashi fad'a kawai ke had'amu da kai shi yasa......"
Yatsa yasa a leb'anta cikin sanyin murya shima yace " Ya isa haka Meemah it doesn't matter ko me kikasa, abu d'aya na sani ina ganin sona a idanunki kamar yadda nima nake sanki."
Ta lumshe ido tace " then why?"
Kin manta nace miki zan rama? D'azu da mukai waya? Banyi tunanin abin zai jawo har ki fad'i haka ba."
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
��♀
Afuwo
ReplyDelete