����������������
�� *JÅĹÀĹÙĎĚĚÑ*��
����������������
Na *AYUSHER MUHD*
No. 2⃣4⃣
Sun isa gidan Jalal yai parking a waje sannan ya kalleta yace " zan wuce." Kallansa tai tare da d'aga kai alamar eh, Jalal na fita itama ta fito tare da Kallansa ta baya, sannan tai ajiyar zuciya ta shiga gida, a tsatsaye taga su Farida da Aisha, suna ganinta Farida ta hau cewa Seemah ina kika shiga? Ko kallanta batai ba ta karasa gun Bala ta mik'amai key tace ka shigo min da mota, sannan ta karasa inda suke, tace " sannunku da gida yaya fa?"
Wani kululun takaicine ya kamasu duka, Aisha ta zuciya tace " bakiji tambayarki ake ina kika je ba? Kinsan neman da muka miki ne?"
Wani irin kallo ta watsa mata tare da cewa " ke in kin fita nemanki ake? Me kuka d'aukeni? Jaririya? Ko me? Ko kuwa ban isa in fita ba?" Tana kainan ta kallesu tai ciki, Aisha tai kwafa tace " wlh Auntu na tsani yarinyar nan."
Farida ta bi Seemah da kallo tace " in muka duba kalamanta bata fad'i karya ba, in kika fita ba nemanki akeyi ba, meyasa ita bata isa ta fitaba sai muhau nemanta."
Aisha tai shiru, Farida tace " Aisha na kula Seemah ba yarinyar banza bace kawai yanda zatai responding magana ne bata iya ba, ita kawai abinda ke ranta take fad'a bata damuwa ko kalaman zasu b'atawa wanda aka fad'awa rai."
Aisha ta jinjina kai, nan sukai ciki gani za'a bud'e gate a shigo da mota.
Seemah kam tama shiga a bakin gado ta zauna ranta a b'ace, dasauri tai dialing number Jalal yana d'agawa yai sallama, ajiyar zuciya tai jin muryarsa sai taji duk bakin cikin ya tafi murmushi tai sannan ta katse layin tare da kwanciya ta rungume pillow, wani shaukin so ne ke ratsata, Aisha ce ta shigo tare da kallanta tace "Seemah me kikeyi hakan?" Bud'e idanu tai tace " Bazaki gane ba ko na fad'a miki." Aisha kam ta sani batasan Seemah sai dai wannan hali nata ma birgeta ko anyi fad'a da ita yanzu in har ka mata magana to komai ya wuce.
Zama tai a bakin gadon tace " nakula dai soyayya ke ratsaki." Seemah najin haka ta mik'e tare da cewa kun shirya da saurayin ki? Tagumi tai tace " inafa haryau bansan a ya muke ba." Seemah tai ajiyar zuciya tace a ganinki yana sanki? Aisha tace I can't tell d'an shekara 1 da suka wuce ne ya ganni a hanya yace ya sona, to ni tun daganan muka fara waya, sai dai bai tab'a zuwa inda nake ba sannan ba nemana yake ba.
Seemah ta kalleta tace " Just 4get him, d'an banaji yana sanki ko kuma mayb akwai wacce ya gani yanaso daga baya." Aisha ta kalleta tace " ni kaina inasan in manta dashi sai dai na kasa, amma ke kamar naga kwanan nan kina cikin wani yanayi.
Seemah tai murmushi tare da cewa " wani nake masifar so sai dai ni kaina nasan nafi sanshi." Aisha tace ya akai kika sani?
Seemah ta rufe ido tace " ni bai dameni ba d'an nafi sanshi abinda na damu da sani shine shima yana sona," tai ajiyar zuciya tace "that's all I need. "
Aisha ta kalleta gaskiya wannan boldness na Seemah da kuma halin ko in kula yana birgeta.
Jalal kam ya kwanta bacci sai dai sam ya kasa bacci sai juyi yakeyi shi kad'ai why is he feeling uneasy? ganun abun bazai kare ba yasa ya mik'e ya d'auro alwala tare da fara salolin nafila.
Da safe wajen karfe 10 Seemah dake kwance ta bud'e ido a hankali, sai dai abinda ta gani ne yasa ta kara lumshe ido, DAD ta gani ya na shafa kanta, bayan ta kara bud'e idon tau murmushi tace " Dad I miss u alot." Ita duk ta d'auka mafarki take jitai yace " kin tashi Sweetheart? "
Mik'ewa tai da sauri ta zauna ta zaro ido tace Dad? Dad ya kalleta yace " dafatan Princess d'ina tana lafiya."
Rungumeshi tai tare da cewa Dad yaushe kazo? Ya shafa bayanta yace " nayi missing daughter ta dayawa shiyasa nazo in ganta mukuma tafi tare."
Dagowa tai cikin mamaki tace " Dad satina fa d'aya?"
Dad yace tashi kiyi wanka kiyi breakfast ni zan d'an fita im ma dawo sai muje yawo, murmushi ta saki tare da dunkule hannunta ta bar babbar d'an yatsa tace " Dad u are the best."
Dad ya mik'e tare da cewa sai na dawo tace " ok" shima yace ok.
Farida ya tadda a kasa yace bari in wuce, tace Dad bakai breakfast ba? Yace naci abinci a jirgi zani Suleja ne.
Bayan Dad ya isa Suleja ya fito ya shiga gidansu, Hajiya na zaune a tsakar gida ta baza tagumi yai sallama, tare da shiga amsawa tai tana kallan hanyar kofar.
Dad ya shiga yana cewa " Hajiya meyasa ake barin kofar nan a bud'e." Kallansa tai cikin wani farincikin ganin d'anta shikanshi jira yake yaga ta mike sai dai abinda ya bashi mamaki gani yai ta koma ta had'e fuskarta, shiyasan laifin amma gani yake yanzu ai yaci ace an daina.
Karasawa yai ya zauna a kusa da ita tare da gaisheta, ta amsa fuskarnan a had'e, kofar band'aki aka bud'e mahaifinsa ne ya fito Dad cikin farinciki yace kawo ka fito.
Kawo ya karaso ya zauna Dad ya gaida shi, sai dai kawo bai amsa ba sai fad'a daya biyo baya, Isma'il ni zaka cima mutumci? Har kaine zaka turomin yarinyar nan gidana? Dad ya kalleshi tare da cewa " Kawo naga wai ai yanz....."
Katse shi kawo yai yace " Yanzu me? Ka d'auka zamu manta? Ko kuwa d'an ka raina mu? To wlh bari kaji ko mutuwa nai bana bukatar yarinyar nan ta min zaman makoki."
Dad idanunsa suka kad'a yace " Haba Kawo in muka duba abin nan yarinyar nam ba itace mai laifi ba me ta sani?"
Hajiya ta katseshi" haka zaka ce? Yarinyar da dalilinta ya ruguzamana farinciki, ya sa mukai hijjira daga garin mu, kacemin me? Ba ruwanta?"
Jikin Dad yai mugun sanyi yace " Dan Allah kubar maganar nan."
Kawo ya mik'e cikin fad'a yace " kai wai wani irin mara zuciya ne? Ko kuwa san Fatima ne ya maka yawa? To wlh bari kaji na fad'ama, magana ma sai tazo aure, kai kana tunanin zaka iya boye maganar ne har karshen rayuwar ka?"
Dad ya runtse idanu da karfi, meyasa kowa bazai fahimceshi ba? Suna tunanin abinda ya faru shi bai ji zafin abin bane ko me?
Hajiya tace " sannan kayima yaranka waya su dawo Nigeria na hana zaman kasar wajen, dama d'an kar muga fuskar yarinyar yasa muka ce kabar kasar amma yanzu tunda kai dakanka ka aikota har cikin gidan mu sai ka shirya shirin dawowa, karkuma ka kuskura kamin musu akan maganar nan."
Dad yace " naji zan dawo amma maganar karatun Seemah fa?" Kawo yace " kai wannan ya dama ba mu ba."
Sunyi shiru kafin dad yace
" Dama abinda ya kawoni shine ina tsoron kar Seemah ta iso lokacin aurene zancen da aka burne ya taso, sannan banaso yarinyar ta fuskanci wannan gaskiyar mai wahalar gaske, shiyasa nake tunanin aura mata Ammar."
Hajiya ta watsa mai wani kallo tace " me? Ammar? Kanada hankali kuwa?" Dad yace " dan Allah Hajiya ku yanda da shawarar nan, in yaso sai ince Ammar ne ba d'ana ba."
Kawo ya ce lalai na yadda Isma'il ka fara zarewa, tashi kabar mana gida sannan kamasu Junaid waya su tattaro su dawo, in ka kuskura ka koma kasar nan zakaga maizai biyo baya.
Dad kamar wanda akama duka ya mik'e abin mamaki Hajiya ganitai hawaye yana kwaranya daga gefen idanunsa, ita kanta jikinta sai yai sanyi.
Hmm Turkashi. ......
Seemah kam tana fitowa daga wanka ta k'ira wayar Jalal shima yana zaune a office, ganin kiranta yasa ya mik'e ya fita yana sallama ta lumshe ido wani sanyi na tsata itama ta amsa, Jalal ya saki wani murmushin dad'i yace " Meemah kamar na dad'e ban gankiba nakejina."
Wani dad'i ne ya kamata tace " kasan me? Yace a'a tace "jinake kamar nayi shekara 1 da fara sanka, ji nake kamar bazan iya rayuwa ba in wani abun ya rabani........"
Jalal ne ya katseta yace"Karki karayin wannan furucin, ba abinda zai rabamu in sha Allah, in kuma kina bukatar b'acin raina kisake fad'ar haka."
Kan gado ta fad'a tare da lumshe idanunta tace " Deen ina masifar sanka, ni na sani nafi sanka akan yanda kake sona."
Karfe dayake gun ya dafa yad'an kwanto yace " haka dai kike tunani amma ni anawa sanin nafi sanki, yau zamu had'u amma ko?"
Tace " Dad yazo yau zamu fita dashi sai dai komin dare inajin in ban gankaba za'a iya samun matsala." A tare sukai murmushi yace bari inkoma aiko tace to Deen.
Yana katse wayar ta rungume wayar a kirjin ta idanunta a lumshe hango Jalal takeyi kawai a idanun nata.
© *THE SEEMAH'S LOVE TEAM*
��♀
No comments:
Post a Comment